< איוב 19 >

ויען איוב ויאמר 1
Sai Ayuba ya amsa,
עד-אנה תוגיון נפשי ותדכאונני במלים 2
“Har yaushe za ku yi ta ba ni azaba ku kuma murƙushe ni da maganganunku?
זה עשר פעמים תכלימוני לא-תבשו תהכרו-לי 3
Yanzu sau goma ke nan kuna wulaƙanta ni, kuna kai mini hari na rashin kunya.
ואף-אמנם שגיתי אתי תלין משוגתי 4
In gaskiya ne na yi laifi, kuskurena ya rage nawa.
אם-אמנם עלי תגדילו ותוכיחו עלי חרפתי 5
In kuwa za ku ɗaukaka kanku a kaina kuna ɗauka wahalar da nake sha domin na yi laifi ne,
דעו-אפו כי-אלוה עותני ומצודו עלי הקיף 6
sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.
הן אצעק חמס ולא אענה אשוע ואין משפט 7
“Ko da yake na yi kuka cewa, ‘An yi mini ba daidai ba!’ Ba a amsa mini ba; ko da yake na nemi taimako, ba a yi adalci ba.
ארחי גדר ולא אעבור ועל נתיבותי חשך ישים 8
Ya tare mini hanya yadda ba zan iya wucewa ba; ya rufe hanyata da duhu.
כבודי מעלי הפשיט ויסר עטרת ראשי 9
Ya cire darajar da nake da ita, ya kuma cire rawani daga kaina.
יתצני סביב ואלך ויסע כעץ תקותי 10
Ya yi kaca-kaca da ni har sai da na ƙare; ya tuge begen da nake da shi kamar itace.
ויחר עלי אפו ויחשבני לו כצריו 11
Yana jin haushina ya lissafta ni cikin maƙiyansa.
יחד יבאו גדודיו--ויסלו עלי דרכם ויחנו סביב לאהלי 12
Rundunarsa ta zo da ƙarfi; suka kafa sansani kewaye da ni, suka zagaye tentina.
אחי מעלי הרחיק וידעי אך-זרו ממני 13
“Ya raba ni da’yan’uwana maza; abokaina sun zama baƙi gare ni.
חדלו קרובי ומידעי שכחוני 14
Dangina sun tafi; abokaina na kurkusa sun manta da ni.
גרי ביתי ואמהתי לזר תחשבני נכרי הייתי בעיניהם 15
Waɗanda sukan ziyarce ni, da masu yi mini aiki mata sun ɗauke ni baƙo.
לעבדי קראתי ולא יענה במו-פי אתחנן-לו 16
Na kira bawana, amma bai amsa ba, ko da yake na roƙe shi da bakina.
רוחי זרה לאשתי וחנתי לבני בטני 17
Numfashina yana ɓata wa matata rai;’yan’uwana sun ƙi ni.
גם-עוילים מאסו בי אקומה וידברו-בי 18
Har’yan yara suna rena ni; in sun gan ni sai su fara yi mini riyar reni.
תעבוני כל-מתי סודי וזה-אהבתי נהפכו-בי 19
Duk abokaina sun yashe ni; waɗanda nake ƙauna sun zama ba sa ƙaunata.
בעורי ובבשרי דבקה עצמי ואתמלטה בעור שני 20
Ni ba kome ba ne sai dai fata da ƙashi, da ƙyar na tsira.
חנני חנני אתם רעי כי יד-אלוה נגעה בי 21
“Ku tausaya mini, abokaina, ku ji tausayina, gama hannun Allah ya sauko a kaina.
למה תרדפני כמו-אל ומבשרי לא תשבעו 22
Don me kuke fafarata kamar yadda Allah yake yi? Ba ku gaji da yagar fatata ba?
מי-יתן אפו ויכתבון מלי מי-יתן בספר ויחקו 23
“Kash, da ma a ce ana rubuta maganganuna, da an rubuta su a littafi,
בעט-ברזל ועפרת-- לעד בצור יחצבון 24
a rubuta su da ƙarfe a kan dutse don su dawwama har abada!
ואני ידעתי גאלי חי ואחרון על-עפר יקום 25
Na san wanda zai fanshe ni yana nan da rai, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya.
ואחר עורי נקפו-זאת ומבשרי אחזה אלוה 26
Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.
אשר אני אחזה-לי--ועיני ראו ולא-זר כלו כליתי בחקי 27
Zan gan shi da kaina da idanuna, Ni, ba wani ba ne. Zuciyata ta cika da wannan tunani!
כי תאמרו מה-נרדף-לו ושרש דבר נמצא-בי 28
“In kuka ce, ‘Za ku ci gaba da matsa mini, tun da shi ne tushen damuwa,’
גורו לכם מפני-חרב--כי-חמה עונות חרב למען תדעון שדין (שדון) 29
sai ku ma ku ji tsoron takobin; gama fushi yakan kawo hukunci ta wurin takobi, sa’an nan za ku san cewa akwai shari’a.”

< איוב 19 >