< איוב 13 >

הן-כל ראתה עיני שמעה אזני ותבן לה 1
“Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
כדעתכם ידעתי גם-אני לא-נפל אנכי מכם 2
Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
אולם--אני אל-שדי אדבר והוכח אל-אל אחפץ 3
Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
ואולם אתם טפלי-שקר רפאי אלל כלכם 4
Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
מי-יתן החרש תחרישון ותהי לכם לחכמה 5
In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
שמעו-נא תוכחתי ורבות שפתי הקשיבו 6
Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
הלאל תדברו עולה ולו תדברו רמיה 7
Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
הפניו תשאון אם-לאל תריבון 8
Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
הטוב כי-יחקר אתכם אם-כהתל באנוש תהתלו בו 9
In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
הוכח יוכיח אתכם-- אם-בסתר פנים תשאון 10
Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
הלא שאתו תבעת אתכם ופחדו יפל עליכם 11
Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
זכרניכם משלי-אפר לגבי-חמר גביכם 12
Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
החרישו ממני ואדברה-אני ויעבר עלי מה 13
“Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
על-מה אשא בשרי בשני ונפשי אשים בכפי 14
Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
הן יקטלני לא (לו) איחל אך-דרכי אל-פניו אוכיח 15
Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
גם-הוא-לי לישועה כי-לא לפניו חנף יבוא 16
lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
שמעו שמוע מלתי ואחותי באזניכם 17
Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
הנה-נא ערכתי משפט ידעתי כי-אני אצדק 18
Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
מי-הוא יריב עמדי כי-עתה אחריש ואגוע 19
Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
אך-שתים אל-תעש עמדי אז מפניך לא אסתר 20
“Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
כפך מעלי הרחק ואמתך אל-תבעתני 21
Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
וקרא ואנכי אענה או-אדבר והשיבני 22
Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
כמה לי עונות וחטאות-- פשעי וחטאתי הדיעני 23
Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
למה-פניך תסתיר ותחשבני לאויב לך 24
Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
העלה נדף תערוץ ואת-קש יבש תרדף 25
Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
כי-תכתב עלי מררות ותורישני עונות נעורי 26
Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
ותשם בסד רגלי-- ותשמור כל-ארחתי על-שרשי רגלי תתחקה 27
Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
והוא כרקב יבלה כבגד אכלו עש 28
“Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.

< איוב 13 >