< איוב 11 >

ויען צפר הנעמתי ויאמר 1
Sa’an nan Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
הרב דברים לא יענה ואם-איש שפתים יצדק 2
“Duk surutun nan ba za a amsa maka ba? Ko mai surutun nan marar laifi ne?
בדיך מתים יחרישו ותלעג ואין מכלם 3
Ko maganganun nan naka marasa amfani za su sa mutane su yi maka shiru? Ba wanda zai kwaɓe ka lokacin da kake faɗar maganar da ba daidai ba?
ותאמר זך לקחי ובר הייתי בעיניך 4
Ka ce wa Allah, ‘Abin da na gaskata ba laifi ba ne kuma ni mai tsabta ne a gabanka.’
ואולם--מי יתן אלוה דבר ויפתח שפתיו עמך 5
Da ma Allah zai yi magana, yă buɗe baki yă faɗi wani abin da ka yi da ba daidai ba
ויגד-לך תעלמות חכמה-- כי-כפלים לתושיה ודע-- כי-ישה לך אלוה מעונך 6
yă kuma buɗe maka asirin hikima, gama hikima ta gaskiya tana da gefe biyu. Ka san wannan, Allah ya riga ya manta da waɗansu zunubanka.
החקר אלוה תמצא אם עד-תכלית שדי תמצא 7
“Ko za ka iya gane al’amuran Allah? Ko za ka iya gane girman asirin Maɗaukaki?
גבהי שמים מה-תפעל עמקה משאול מה-תדע (Sheol h7585) 8
Sun fi nisan sama tudu, me za ka iya yi? Sun fi zurfin kabari zurfi, me za ka sani? (Sheol h7585)
ארכה מארץ מדה ורחבה מני-ים 9
Tsayinsu ya fi tsawon duniya da kuma fāɗin teku.
אם-יחלף ויסגיר ויקהיל ומי ישיבנו 10
“In ya zo ya kulle ka a kurkuku ya ce kai mai laifi ne, wa zai hana shi?
כי-הוא ידע מתי-שוא וירא-און ולא יתבונן 11
Ba shakka yana iya gane mutanen da suke marasa gaskiya; kuma in ya ga abin da yake mugu, ba ya kula ne?
ואיש נבוב ילבב ועיר פרא אדם יולד 12
Amma daƙiƙin mutum ba ya taɓa zama mai hikima kamar dai a ce ba a taɓa haihuwar ɗan aholaki horarre.
אם-אתה הכינות לבך ופרשת אליו כפיך 13
“Duk da haka in ka miƙa masa zuciyarka, ka kuma miƙa hannuwanka gare shi,
אם-און בידך הרחיקהו ואל-תשכן באהליך עולה 14
in ka kawar da zunubin da yake hannunka, ba ka bar zunubi ya kasance tare da kai ba
כי-אז תשא פניך ממום והיית מצק ולא תירא 15
shi ne za ka iya ɗaga fuskarka ba tare da jin kunya ba; za ka tsaya da ƙarfi kuma ba za ka ji tsoro ba.
כי-אתה עמל תשכח כמים עברו תזכר 16
Ba shakka za ka manta da wahalolinka, za ka tuna da su kamar yadda ruwa yake wucewa.
ומצהרים יקום חלד תעפה כבקר תהיה 17
Rayuwarka za tă fi hasken rana haske, duhu kuma zai zama kamar safiya.
ובטחת כי-יש תקוה וחפרת לבטח תשכב 18
Za ka zauna lafiya, domin akwai bege; za ka duba kewaye da kai ka huta cikin kwanciyar rai.
ורבצת ואין מחריד וחלו פניך רבים 19
Za ka kwanta, ba wanda zai sa ka ji tsoro, da yawa za su zo neman taimako a wurinka.
ועיני רשעים תכלינה ומנוס אבד מנהם ותקותם מפח-נפש 20
Amma idanun mugaye ba za su iya gani ba, kuma ba za su iya tserewa ba; begensu zai zama na mutuwa.”

< איוב 11 >