< ישעה 3 >

כי הנה האדון יהוה צבאות מסיר מירושלם ומיהודה משען ומשענה כל משען לחם וכל משען מים 1
Yanzu ka duba fa, Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana shirin yă ɗauke kowane tanadi da taimako daga Urushalima da Yahuda dukan tanade-tanaden abinci da kuma dukan tanade-tanaden ruwa,
גבור ואיש מלחמה שופט ונביא וקסם וזקן 2
jarumi, da soja, alƙali da annabi masu duba da dattijo,
שר חמשים ונשוא פנים ויועץ וחכם חרשים ונבון לחש 3
shugaban sojojin hamsin da mutum mai makami, mai ba da shawara, gwanin sarrafa abubuwa da mai gwanintan dabo.
ונתתי נערים שריהם ותעלולים ימשלו בם 4
“Zan sa’yan yara su zama shugabanninsu;’yan yara kurum za su yi mulkinsu.”
ונגש העם איש באיש ואיש ברעהו ירהבו הנער בזקן והנקלה בנכבד 5
Mutane za su zalunci juna mutum da mutum, maƙwabci da maƙwabci. Yara za su rena tsofaffi, ƙasƙantacce zai rena mai daraja.
כי יתפש איש באחיו בית אביו שמלה לכה קצין תהיה לנו והמכשלה הזאת תחת ידך 6
Mutum zai kama ɗaya daga cikin’yan’uwansa a gidan mahaifinsa ya ce, “Kana da abin sawa, ka zama shugabanmu; wannan kango kuma yă zama a ƙarƙashinka!”
ישא ביום ההוא לאמר לא אהיה חבש ובביתי אין לחם ואין שמלה לא תשימני קצין עם 7
Amma a ranan nan zai tā da murya ya ce, “Ba ni ba dai. Ba ni da abinci ko abin sawa a gidana; kada ka mai da ni shugaban mutane.”
כי כשלה ירושלם ויהודה נפל כי לשונם ומעלליהם אל יהוה למרות עני כבודו 8
Urushalima tana tangaɗi, Yahuda yana fāɗuwa; maganganunsu da ayyukansu suna gāba da Ubangiji, suna rena ɗaukakar kasancewarsa.
הכרת פניהם ענתה בם וחטאתם כסדם הגידו לא כחדו אוי לנפשם כי גמלו להם רעה 9
Fuskokinsu shaidu ne a kansu; suna nuna zunubinsu a fili kamar yadda Sodom ya yi; ba sa ma ɓoye shi. Kaitonsu! Sun jawo wa kansu masifa.
אמרו צדיק כי טוב כי פרי מעלליהם יאכלו 10
Ku faɗa wa masu adalci cewa kome zai zama musu da kyau, gama za su ji daɗin aikin da hannuwansu suka yi.
אוי לרשע רע כי גמול ידיו יעשה לו 11
Kaiton masu mugunta! Masifa tana a kansu! Za a rama abin da hannuwansu suka yi.
עמי נגשיו מעולל ונשים משלו בו עמי מאשריך מתעים ודרך ארחתיך בלעו 12
Matasa suna zalunta mutanena, mata suna mulki a bisansu. Ya mutanena, jagorarinku suna ɓad da ku; suna karkatar da ku daga hanya.
נצב לריב יהוה ועמד לדין עמים 13
Ubangiji ya ɗauki mazauninsa a cikin ɗakin shari’a; ya tashi don yă shari’anta mutane.
יהוה במשפט יבוא עם זקני עמו ושריו ואתם בערתם הכרם גזלת העני בבתיכם 14
Ubangiji yana shari’a da dattawa da kuma shugabannin mutanensa, “Ku ne kuka lalace gonar inabina; ganimar talakawa suna a gidajenku.
מלכם (מה לכם) תדכאו עמי ופני עניים תטחנו נאם אדני יהוה צבאות 15
Ina dalilin da kuke marmatsa mutanena kuna gurgurje fuskokin talakawa?” Ni Ubangiji Maɗaukaki na faɗa.
ויאמר יהוה יען כי גבהו בנות ציון ותלכנה נטוות (נטויות) גרון ומשקרות עינים הלוך וטפף תלכנה וברגליהם תעכסנה 16
Ubangiji ya ce, “Matan Sihiyona suna da girman kai, suna tafiya da wuya a miƙe, da idanu masu yaudara, suna takawa ɗaya-ɗaya a hankali, da mundaye a ƙafafunsu, suna cas-cas.
ושפח אדני קדקד בנות ציון ויהוה פתהן יערה 17
Saboda haka Ubangiji zai kawo gyambuna a kawunan matan Sihiyona; Ubangiji zai sa a aske kawunansu, a bar su ƙwal.”
ביום ההוא יסיר אדני את תפארת העכסים והשביסים--והשהרנים 18
A wannan rana Ubangiji zai ƙwace abin da suke taƙama da shi, mundayensu, ɗankwalin kansu da abin wuyansu,
הנטפות והשירות והרעלות 19
’yan kunnensu, kwandagansu da lulluɓinsu,
הפארים והצעדות והקשרים ובתי הנפש והלחשים 20
kitsonsu, sarƙar da suke sa wa damatsansu da ɗamararsu, kwalabai turare da layu,
הטבעות ונזמי האף 21
da ƙawanen da suka sa a yatsotsinsu da hancinsu,
המחלצות והמעטפות והמטפחות והחריטים 22
tufafi masu kyau, da manyan rigunansu, da mayafansu, da jakar kuɗinsu
והגלינים והסדינים והצניפות והרדידים 23
da madubi, da kuma tufafin lilin da adikai, da gyale.
והיה תחת בשם מק יהיה ותחת חגורה נקפה ותחת מעשה מקשה קרחה ותחת פתיגיל מחגרת שק כי תחת יפי 24
A maimakon ƙanshi, wari ne za a ji; a maimakon abin ɗamara, igiya ce za a samu; a maimakon kyakkyawan gashi, sanƙo za su kasance da shi a kai; a maimakon tufafi masu kyau, za su sa tsummoki; a maimakon kyau, za su zama munana.
מתיך בחרב יפלו וגבורתך במלחמה 25
Mazanku za su mutu ta wurin takobi, jarumawanku za su mutu a yaƙi.
ואנו ואבלו פתחיה ונקתה לארץ תשב 26
Ƙofofin Sihiyona za su yi makoki su kuma yi kuka; za tă zama wofi, za tă zauna a ƙasa.

< ישעה 3 >