< בראשית 40 >
ויהי אחר הדברים האלה חטאו משקה מלך מצרים והאפה--לאדניהם למלך מצרים | 1 |
Bayan ɗan lokaci, sai mai riƙon kwaf da mai tuyan sarkin Masar suka yi wa maigidansu, sarkin Masar laifi.
ויקצף פרעה על שני סריסיו--על שר המשקים ועל שר האופים | 2 |
Fir’auna ya yi fushi da hafsoshin nan nasa guda biyu, shugaban masu shayarwa da shugaban masu tuya,
ויתן אתם במשמר בית שר הטבחים--אל בית הסהר מקום אשר יוסף אסור שם | 3 |
ya kuma sa su a kurkuku a cikin gidan shugaban masu tsaro, a wannan kurkukun da aka sa Yusuf.
ויפקד שר הטבחים את יוסף אתם--וישרת אתם ויהיו ימים במשמר | 4 |
Sai shugaban masu tsaro ya danƙa su a hannun Yusuf, ya kuwa yi musu hidima. Bayan sun jima cikin kurkuku,
ויחלמו חלום שניהם איש חלמו בלילה אחד--איש כפתרון חלמו המשקה והאפה אשר למלך מצרים אשר אסורים בבית הסהר | 5 |
sai kowanne a cikin mutum biyun nan, mai riƙon kwaf da mai tuya na sarkin Masar, waɗanda aka sa a kurkuku, suka yi mafarki a dare ɗaya, kuma kowane mafarki ya kasance da fassara irin tasa.
ויבא אליהם יוסף בבקר וירא אתם והנם זעפים | 6 |
Sa’ad da Yusuf ya zo wurinsu kashegari, sai ya ga duk sun damu.
וישאל את סריסי פרעה אשר אתו במשמר בית אדניו--לאמר מדוע פניכם רעים היום | 7 |
Saboda haka ya tambayi hafsoshin Fir’auna, waɗanda suke a kurkuku tare da shi, a gidan maigidansa ya ce, “Me ya sa fuskokinku suke a ɓace haka?”
ויאמרו אליו--חלום חלמנו ופתר אין אתו ויאמר אלהם יוסף הלוא לאלהים פתרנים--ספרו נא לי | 8 |
Sai suka amsa, “Mu biyu, mun yi mafarki, amma babu wani da zai fassara mana su.” Sa’an nan Yusuf ya ce musu, “Fassara ba daga Allah take zuwa ba? Ku faɗa mini mafarkanku.”
ויספר שר המשקים את חלמו ליוסף ויאמר לו--בחלומי והנה גפן לפני | 9 |
Sai shugaban masu shayarwa ya faɗa wa Yusuf mafarkinsa. Ya ce masa, “A cikin mafarkina, na ga kuringa a gabana,
ובגפן שלשה שריגם והוא כפרחת עלתה נצה הבשילו אשכלתיה ענבים | 10 |
kuma a kuringar, akwai rassa uku. Nan da nan kuringar ta yi toho, ta huda, ta kuma yi nonna har suka nuna, suka zama inabi.
וכוס פרעה בידי ואקח את הענבים ואשחט אתם אל כוס פרעה ואתן את הכוס על כף פרעה | 11 |
Kwaf Fir’auna kuwa yana a hannuna, na kuma ɗiba inabin na matse su cikin kwaf Fir’auna, na kuma sa kwaf ɗin a hannunsa.”
ויאמר לו יוסף זה פתרנו שלשת השרגים--שלשת ימים הם | 12 |
Yusuf ya ce masa, “Ga abin da mafarkin yake nufi, ‘Rassan nan uku, kwana uku ne.
בעוד שלשת ימים ישא פרעה את ראשך והשיבך על כנך ונתת כוס פרעה בידו כמשפט הראשון אשר היית משקהו | 13 |
Cikin kwana uku, Fir’auna zai fitar da kai, yă maido da kai a matsayinka, za ka kuwa sa kwaf Fir’auna cikin hannunsa, kamar yadda ka saba yi sa’ad da kake mai riƙon kwaf nasa.
כי אם זכרתני אתך כאשר ייטב לך ועשית נא עמדי חסד והזכרתני אל פרעה והוצאתני מן הבית הזה | 14 |
Amma fa, sa’ad da kome ya zama maka da kyau, ka tuna da ni, ka kuma yi mini alheri, ka ambace ni wa Fir’auna, ka fid da ni daga wannan kurkuku.
כי גנב גנבתי מארץ העברים וגם פה לא עשיתי מאומה כי שמו אתי בבור | 15 |
Gama da ƙarfi ne aka ɗauke ni daga ƙasar Ibraniyawa, ko a nan ma ban yi wani abin da ya cancanci a sa ni cikin kurkuku ba.’”
וירא שר האפים כי טוב פתר ויאמר אל יוסף אף אני בחלומי והנה שלשה סלי חרי על ראשי | 16 |
Sa’ad da shugaban masu tuya ya ga cewa Yusuf ya ba da fassara mai gamsarwa, sai ya ce, wa Yusuf, “Ni ma na yi mafarki. A kaina, akwai kwanduna uku na burodi.
ובסל העליון מכל מאכל פרעה--מעשה אפה והעוף אכל אתם מן הסל--מעל ראשי | 17 |
A kwandon na bisa, akwai kayan iri-iri da aka toya, masu kyau domin Fir’auna, amma tsuntsaye suka ci su a kwandon da yake kaina.”
ויען יוסף ויאמר זה פתרנו שלשת הסלים--שלשת ימים הם | 18 |
Yusuf ya ce, “Ga abin da mafarkin yake nufi, ‘Kwanduna uku, kwanaki uku ne.
בעוד שלשת ימים ישא פרעה את ראשך מעליך ותלה אותך על עץ ואכל העוף את בשרך מעליך | 19 |
Cikin kwana uku, Fir’auna zai fid da kai, yă rataye ka a kan itace. Tsuntsaye kuwa za su ci naman jikinka.’”
ויהי ביום השלישי יום הלדת את פרעה ויעש משתה לכל עבדיו וישא את ראש שר המשקים ואת ראש שר האפים--בתוך עבדיו | 20 |
To, a rana ta uku ne, ranar tunawa da haihuwar Fir’auna, ya kuwa yi biki wa dukan hafsoshinsa. Ya fid da shugaban masu shayarwa da kuma shugaban masu tuya a gaban hafsoshinsa.
וישב את שר המשקים על משקהו ויתן הכוס על כף פרעה | 21 |
Ya mai da shugaban masu shayarwa a matsayinsa, saboda haka shugaban masu shayarwa ya sāke sa kwaf a hannun Fir’auna,
ואת שר האפים תלה כאשר פתר להם יוסף | 22 |
amma ya rataye shugaban masu tuya, kamar dai yadda Yusuf ya faɗa musu a fassarar mafarkan da suka yi.
ולא זכר שר המשקים את יוסף וישכחהו | 23 |
Shugaban masu shayarwa fa, bai tuna da Yusuf ba; ya mance da shi.