< דברי הימים א 16 >
ויביאו את ארון האלהים ויציגו אתו בתוך האהל אשר נטה לו דויד ויקריבו עלות ושלמים לפני האלהים | 1 |
Suka fa kawo akwatin alkawarin Allah, suka sa a cikin tentin da Dawuda ya kafa dominsa, suka kuma miƙa hadayun ƙonawa da hadayu na salama a gaban Allah.
ויכל דויד מהעלות העלה והשלמים ויברך את העם בשם יהוה | 2 |
Bayan Dawuda ya gama miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama, sai ya albarkaci mutane a cikin sunan Ubangiji.
ויחלק לכל איש ישראל מאיש ועד אשה--לאיש ככר לחם ואשפר ואשישה | 3 |
Sa’an nan ya ba da dunƙulen burodi da wainar dabino da kuma kauɗar zabibi ga kowane mutumin Isra’ila namiji da ta mace.
ויתן לפני ארון יהוה מן הלוים--משרתים ולהזכיר ולהודות ולהלל ליהוה אלהי ישראל | 4 |
Ya sa Lawiyawa su yi hidima a gaban akwatin alkawarin Ubangiji, su ɗaukaka, su gode, su kuma yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila.
אסף הראש ומשנהו זכריה יעיאל ושמירמות ויחיאל ומתתיה ואליאב ובניהו ועבד אדם ויעיאל בכלי נבלים ובכנרות ואסף במצלתים משמיע | 5 |
Asaf shi ne babba, sai Zakariya na biye, sa’an nan Ya’aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Mattitiya, Eliyab, Benahiya, Obed-Edom da Yehiyel. Su ne za su kaɗa molaye, da garayu, Asaf kuwa zai buga ganguna,
ובניהו ויחזיאל הכהנים--בחצצרות תמיד לפני ארון ברית האלהים | 6 |
Benahiya da Yahaziyel firistoci za su busa ƙahoni kullum a gaban akwatin alkawarin Allah.
ביום ההוא אז נתן דויד בראש להדות ליהוה--ביד אסף ואחיו | 7 |
A wannan rana, da farko, Dawuda ya sa Asaf da’yan’uwansa su rera wannan zabura ta yabo ga Ubangiji.
הודו ליהוה קראו בשמו-- הודיעו בעמים עלילתיו | 8 |
Ku yi godiya ga Ubangiji, ku yi shelar sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
שירו לו זמרו לו-- שיחו בכל נפלאתיו | 9 |
Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan ayyukan banmamakinsa.
התהללו בשם קדשו-- ישמח לב מבקשי יהוה | 10 |
Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
דרשו יהוה ועזו-- בקשו פניו תמיד | 11 |
Ku dogara ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
זכרו נפלאתיו אשר עשה-- מפתיו ומשפטי פיהו | 12 |
Ku tuna ayyukan banmamakin da ya aikata, mu’ujizansa da kuma hukuntai da ya yanke,
זרע ישראל עבדו-- בני יעקב בחיריו | 13 |
Ya ku zuriyar Isra’ila bayinsa, Ya ku’ya’yan Yaƙub maza, zaɓaɓɓunsa.
הוא יהוה אלהינו-- בכל הארץ משפטיו | 14 |
Shi ne Ubangiji Allahnmu; hukuntansa suna a cikin dukan duniya.
זכרו לעולם בריתו-- דבר צוה לאלף דור | 15 |
Yakan tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
אשר כרת את אברהם-- ושבועתו ליצחק | 16 |
alkawarin da ya yi wa Ibrahim rantsuwar da ya yi ga Ishaku.
ויעמידה ליעקב לחק-- לישראל ברית עולם | 17 |
Ya tabbatar da shi ga Yaƙub kamar ƙa’ida, ga Isra’ila kamar madawwamin alkawari.
לאמר לך אתן ארץ כנען-- חבל נחלתכם | 18 |
“Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana kamar rabon da za ka gāda.”
בהיותכם מתי מספר-- כמעט וגרים בה | 19 |
Sa’ad da suke kima, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
ויתהלכו מגוי אל גוי-- ומממלכה אל עם אחר | 20 |
suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga wannan mulki zuwa wancan.
לא הניח לאיש לעשקם-- ויוכח עליהם מלכים | 21 |
Bai bar wani ya zalunce su ba; saboda su ya tsawata wa sarakuna.
אל תגעו במשיחי-- ובנביאי אל תרעו | 22 |
“Kada ku taɓa shafaffuna; kada ku yi wa annabawana lahani.”
שירו ליהוה כל הארץ-- בשרו מיום אל יום ישועתו | 23 |
Ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
ספרו בגוים את כבודו-- בכל העמים נפלאתיו | 24 |
Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, ayyukansa masu al’ajabai a cikin mutane.
כי גדול יהוה ומהלל מאד-- ונורא הוא על כל אלהים | 25 |
Gama Ubangiji mai girma ne ya kuma cancanci yabo; dole a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
כי כל אלהי העמים אלילים-- ויהוה שמים עשה | 26 |
Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ya yi sammai.
הוד והדר לפניו-- עז וחדוה במקמו | 27 |
Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da farin ciki suna a wurin zamansa.
הבו ליהוה משפחות עמים-- הבו ליהוה כבוד ועז | 28 |
Ku yabi Ubangiji, ku iyalan al’ummai, ku yabi ɗaukaka da ƙarfin Ubangiji,
הבו ליהוה כבוד שמו שאו מנחה ובאו לפניו-- השתחוו ליהוה בהדרת קדש | 29 |
ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa. Ku kawo hadaya ku kuma zo gabansa; ku yi wa Ubangiji sujada cikin darajar tsarkinsa.
חילו מלפניו כל הארץ-- אף תכון תבל בל תמוט | 30 |
Ku yi rawar jiki a gabansa, ya ku duniya duka! Duniya ta kahu sosai; ba za tă jijjigu ba.
ישמחו השמים ותגל הארץ-- ויאמרו בגוים יהוה מלך | 31 |
Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari su ce a cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki!”
ירעם הים ומלואו-- יעלץ השדה וכל אשר בו | 32 |
Bari teku da kome da yake cikinsa su yi ruri; bari gonaki da kome a cikinsu su yi farin ciki!
אז ירננו עצי היער מלפני יהוה--כי בא לשפוט את הארץ | 33 |
Sa’an nan itatuwan jeji za su rera, za su rera don farin ciki a gaban Ubangiji, gama ya zo don yă hukunta duniya.
הודו ליהוה כי טוב-- כי לעולם חסדו | 34 |
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama shi nagari ne; ƙaunarsa madawwamiya ce.
ואמרו--הושיענו אלהי ישענו וקבצנו והצילנו מן הגוים להדות לשם קדשך להשתבח בתהלתך | 35 |
Ku yi kuka, ku ce, “Cece mu, ya Allah Mai Cetonmu; tara mu ka kuma cece mu daga al’ummai, don mu yi godiya ga sunanka mai tsarki, don mu ɗaukaka a cikin yabonka.”
ברוך יהוה אלהי ישראל-- מן העולם ועד העלם ויאמרו כל העם אמן-- והלל ליהוה | 36 |
Yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Sai dukan mutane suka ce, “Amin.” Suka kuma “Yabi Ubangiji.”
ויעזב שם לפני ארון ברית יהוה לאסף ולאחיו לשרת לפני הארון תמיד--לדבר יום ביומו | 37 |
Dawuda ya bar Asaf da’yan’uwansa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji don su yi hidima a can kullum, bisa ga tsari na kowace rana.
ועבד אדם ואחיהם ששים ושמונה ועבד אדם בן ידיתון וחסה לשערים | 38 |
Ya kuma bar Obed-Edom da’yan’uwansa sittin da takwas don su yi hidima tare. Obed-Edom ɗan Yedutun da Hosa kuma, su ne matsaran ƙofofi.
ואת צדוק הכהן ואחיו הכהנים לפני משכן יהוה--בבמה אשר בגבעון | 39 |
Dawuda ya bar Zadok firist da’yan’uwansa firistoci a gaban tabanakul na Ubangiji a tudun da yake a Gibeyon
להעלות עלות ליהוה על מזבח העלה תמיד--לבקר ולערב ולכל הכתוב בתורת יהוה אשר צוה על ישראל | 40 |
don su miƙa hadayun ƙonawa ga Ubangiji a kan bagaden hadaya ta ƙonawa kullum, da safe da kuma yamma, bisa ga kome da yake a rubutacce a cikin Dokar Ubangiji, da ya ba wa Isra’ila.
ועמהם הימן וידותון ושאר הברורים אשר נקבו בשמות--להדות ליהוה כי לעולם חסדו | 41 |
Tare da su akwai Heman da Yedutun da sauran waɗannan zaɓaɓɓun da aka rubuta sunansu don yin godiya ga Ubangiji, “gama ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
ועמהם הימן וידותון חצצרות ומצלתים למשמיעים וכלי שיר האלהים ובני ידותון לשער | 42 |
Heman da Yedutun su ne da hakkin busa ƙahoni da kaɗa kuge da sauran kayan bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe, waɗanda ake amfani da su lokacin da ake rera waƙoƙi masu tsarki.’Ya’yan Yedutun maza, su aka ba wa aikin tsaron ƙofa.
וילכו כל העם איש לביתו ויסב דויד לברך את ביתו | 43 |
Sa’an nan dukan mutanen suka tashi, kowa ya koma gidansa, Dawuda ya koma gida yă sa wa iyalinsa albarka.