< Halelu 78 >
1 E NA kanaka o'u, e hoolohe mai oukou i ko'u kanawai; E haliu mai hoi i ko oukou pepeiao i na olelo a ko'u waha.
Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
2 E hooaka ae au i kuu waha ma na himeni, A e hai aku hoi i na mele kahiko;
Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
3 I na mea a kakou i lohe ai, a i ike ai hoi, A ua hai mai no ko kakou poe makua ia kakou.
abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
4 Aole kakou e huna, mai ka lakou poe keiki, A hiki aku i ka hanauna hope loa, I ka hoike ana aku i na halelu no Iehova, A me kona ikaika, a me na mea kupanaha ana i hana'i.
Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
5 Hoopaa oia i mea hoike no ka Iakoba, A kau no hoi oia i kanawai no ka Iseraela, A kauoha mai la i na kupuna o kakou, E ao ae lakou ia mea i ka lakou poe keiki:
Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
6 I ike ka hanauna hope loa aku, E ku mai hoi na keiki i hanau mai a hoike i ka lakou mau keiki;
don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
7 I kau aku ko lakou manaolana i ke Akua, Aole hoi e poina na hana a ke Akua, Aka, e malama i kana mau kauoha:
Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
8 I like ole lakou me ko lakou poe kupuna, He hanauna ku e, a kipi hoi; He hanauna hooponopono ole i ko lakou naau, A hilinai ole hoi ko lakou naau i ke Akua.
Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
9 O na mamo a Eperaima i kahikoia i ke kakaka, Huli hope no lakou i ka la i kaua'i.
Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
10 Aole lakou i malama i ka berita o ke Akua, A hoole lakou i ka hele ma kona kanawai:
ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
11 Poina ia lakou kana mau hana. Na mea kupanaha hoi ana i hoike mai ai.
Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
12 Hana iho la no oia i na mea kupanaha imua o ko lakou poe makua, Ma ka aina o Aigupita, ma ke kula hoi o Zoana.
Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
13 Mahele ae la oia i ke kai, a alakai mai la ia lakou; Hooku ae la oia i na wai me he puu la.
Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
14 Ma ke ao oia i alakai mai ai ia lakou i ke ao, Ma ka malamalama o ke ahi hoi i na po a pau.
Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
15 Wahi ae la oia i na pohaku ma ka waonahele, Hoohainu mai oia, e like me na ale nui.
Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
16 Hoopuka ae la oia i na wai kahe mailoko mai o ka pohaku, A kahe mai la na wai e like me na muliwai.
ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
17 Hana hewa hou aku la lakou ia ia, I ke ku e ana i ka Mea kiekie ma ka waoakua.
Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
18 Hoao aku la lakou i ke Akua ma ko lakou naau, I ka nonoi ana i ai, no ko lakou kuko iho.
Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
19 Hoowahawaha aku la lakou i ke Akua, i iho la, E hiki anei i ke Akua ke halii i papaaina ma ka waonahele?
Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
20 Aia hoi! hahau ae la oia i ka pohaku, a kahe iho la na wai, A huliamahi mai la na wai kahe; E hiki anei ia ia ke haawi mai i ka ai? A e hoomakaukau hoi i ia no kona poe kanaka?
Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
21 Nolaila, lohe mai la o Iehova a huhu iho la; A hoaia ke ahi maloko o ka Iakoba, A pii ae la ka huhu maluna o ka Iseraela:
Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
22 No ka mea, aole lakou i manaoio i ke Akua; Aole hoi i paulele i kona kokua ana.
gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
23 Ua kauoha nae oia i na ao, mailuna mai, A ua wahi no hoi i puka ma ka lani,
Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
24 A ua hooua mai oia maluna o lakou, i mane e ai ai, A ua haawi mai i ka hua palaoa o ka lani na lakou.
ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
25 Ai iho la na kanaka i ka ai a ka poe kiekie: Hoouka mai la oia i io na lakou a nui.
Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
26 Hoopa mai la oia i ko ka hikina makani ma ka lani: A i kona ikaika, kai mai la oia i ka makani o ke kukuluhema.
Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
27 A hooua mai oia i ka io maluna o lakou me he lepo la, A me na manu hulu, e like me ke one o ke kai.
Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
28 Hoohaule iho la oia ia mea ma ke kahua hoomoana, A puni hoi ko lakou wahi i noho ai.
Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
29 A ai iho la lakou, a maona loa ae la: Hoopuka mai no oia na lakou i ka mea a lakou i kuko ai.
Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
30 Aole nae lakou i huli, mai ko lakou kuko ana; I ka wa e waiho ana ka ai i ko lakou waha,
Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
31 Kau mai la ka huhu o ke Akua maluna o lakou, A luku iho la oia i ko lakou poe ikaika; A hookulou no hoi i ka poe i waeia o ka Iseraela.
fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
32 Aka, ma ia mau mea a pau, hana hewa hou iho la no lakou, Aole i manaoio i kana mau hana kupanaha.
Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
33 Nolaila, haawi oia i ka noho makehewa ana i ko lakou mau la, A me ka wiwo wale, i ko lakou mau makahiki.
Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
34 Ina luku oia ia lakou, alaila, nonoi aku lakou ia ia, Huli ae la no hoi, a imi i ke Akua.
A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
35 Hoomanao iho la lakou, o ke Akua ko lakou Pohaku, A o ke Akua kiekie hoi ko lakou Hoolapanai.
Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
36 Aka, hoomalimali aku lakou ia ia ma ko lakou waha A wahahee aku no hoi ia ia ma ko lakou alelo.
Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
37 Aole i kupaa ko lakou naau ma ke Akua, Aole hoi i hilinai i kona berita.
zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
38 Lokomaikai mai no nae oia, a kala mai i ka hala, Aole i anai mai ia lakou: Hoohuli pinepine aku oia i kona huhu, Aole i hoala i kona inaina a pau.
Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
39 No ka mea, hoomanao oia, he palupalu lakou, He ea hele wale aku, aole hoi mai.
Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
40 Me he aha la la ko lakou kipikipi ana ia ia ma ka waonahele? A hoonaukiuki ia ia ma ka waoakua?
Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
41 A huli ihope lakou a hoao i ke Akua, Hoehaeha no hoi i ka Mea Hemolele o ka Iseraela.
Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
42 Aole lakou i hoomanao i kona lima, I ka la ana i hoopakele ai ia lakou i ka pilikia,
Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
43 I ka manawa ana i kau ai i kona mau hoailona ma Aigupita, A me kana hana kupanaha ma ke kula o Zoana:
ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
44 Hoolilo oia i ko lakou muliwai i koko, A me na kahawai hoi, a hiki ole ia lakou ke inu.
Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
45 Hoouka ae la oia i ka makika maluna o lakou, A nahu iho la oia ia lakou; A me na rana hoi, a hooki loa oia mau mea ia lakou.
Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
46 Haawi ae la oia i ka lakou ai na ke poko, A me ka mea a lakou i hooikaika'i na ka uhini.
Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
47 Pepehi mai la oia i ka lakou kumuwaina i ka huahekili, A me ka lakou sukamora i ka hau.
Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
48 Hoolilo ae la oia i na bipi a lakou i ka huahekili, A me na holoholona a lakou i ka uila.
Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
49 Hoouka ae la oia maluna o lakou, i ka wela o kona huhu, A me ka ukiuki, a me ka inaina, a me ka popilikia, A hoouna mai no hoi i na elele ino.
Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
50 Hoomakaukau iho la oia i ke ala no kona huhu, Aole ia i kaohi i ko lakou uhane mai ka make mai; Aka, haawi no oia i ko lakou ola i ka mai ahulan;
Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
51 A pepehi no hoi i na hiapo a pau o Aigupita, O na poo ikaika ma na halelewa o Hama.
Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
52 Kai mai la oia i kona poe kanaka me he poe hipa la, A alakai no hoi ia lakou ma ka waonahele me he ohana la.
Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
53 Alakai oia ia lakou i ka malu, i ole ai lakou e makau: Aka, poi mai ke kai maluna o ko lakou poe enemi.
Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
54 Hoohele oia ia lakou i kona aina hoano, I keia mauna hoi a kona lima akau i hookumu ai.
Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
55 Kipaku aku la oia i ko na aina e, mai ko lakou alo aku, Mahele ae la oia ma ke kaula-ana i ka ilina no lakou, A hoonoho iho la i na ohana o ka Iseraela iloko o ko lakou mau halelewa.
Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
56 Aka, hoao lakou i ke Akua kiekie, a kipi aku la, Aole hoi i malama i kana mau kauoha:
Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
57 Huli hope lakou, a hoopunipuni e like me na makua o lakou; Ua huli lakou ihope, e like me ke kakaka lauwili.
Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
58 Hoonaukiuki lakou ia ia i ko lakou wahi kiekie, A hoolili no hoi ia ia i ko lakou poe kii kalaiia.
Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
59 A lohe ke Akua alaila, huhu mai la ia, A hoopailua loa no hoi i ka Iseraela.
Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
60 Nolaila, haalele iho la oia i ka halelewa o Silo, I ka halelole hoi kahi ana i noho ai iwaena o na kanaka,
Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
61 A haawi no hoi i kona mea hanohano i ke pio ana, A me kona mea nani iloko o ka lima o ka enemi.
Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
62 Hoolilo no oia i kona poe kanaka i ka pahikaua, A huhu mai la i kona hooilina.
Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
63 Hoopau no ke ahi i kona poe kanaka ui; Aole nae i kanikau na wahine puupaa.
Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
64 Haule no hoi kona poe kahuna i ka pahikaua; Aole nae i kanikau kona poe wahiue kanemake.
aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
65 Alaila ala ae la ka Haku me he mea la mai kona hiamoe ana, Me he kanaka ikaika la hoi i ona i ka waina.
Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
66 Alaila, pehi ae la oia i kona poe enemi ma ko lakou hope; Haawi no ia i hilahila mau loa lakou.
Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
67 Hoowahawaha oia i ka halelewa o Iosepa, Aole hoi i wae i ka ohana o Eperaima:
Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
68 Aka, wae no ia i ka ohana o Iuda, I ka mauna hoi o Ziona ana i aloha'i.
amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
69 Hana oia i kona wahi hoano e like me na wahi kiekie, E like hoi me ka honua ana i hookumu mau loa'i.
Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
70 Wae mai la oia ia Davida i kana kauwa, A lawe ae la ia ia, mai na pahipa ae:
Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
71 Mai ka hahai ana i na hipa mea keiki, ua lawe oia ia ia, E hanai i ka Iakoba, i na kanaka ona, I ka Iseraela hoi, i kona hooilina.
daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
72 Hanai mai la oia ia lakou e like me ka pono o kona naau; A alakai ae la ia lakou ma ke akamai o kona mau lima.
Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.