< Halelu 2 >

1 NO ke aha la e kupikipikio ai ko ka aina e? A e noonoo ai ka poe kanaka i ka mea lapuwale?
Me ya sa ƙasashe suke haɗa baki mutane kuma suke ƙulla shawarwarin banza?
2 Ua ku e aku na'lii o ka honua, Ua ohumu pu aku no hoi na luna, Ia Iehova, a i kona Mea i poniia,
Sarakunan duniya sun ɗauki matsayi masu mulki sun taru gaba ɗaya suna gāba da Ubangiji da kuma Shafaffensa.
3 E moku aku kakou i ka laua mau mea paa, A e hoolei aku hoi mai o kakou aku nei i ka laua mau kaula.
Suna cewa, “Bari mu tsittsinke sarƙoƙinsu, mu kuma’yantar da kamammu daga kangin bautar Allah.”
4 O ka Mea e noho ana ma ka lani, e aka mai no ia: A e hoomahua mai no hoi o ka Haku ia lakou.
Mai zama a kursiyi a sama yana dariya; Ubangiji yana musu ba’a.
5 Alaila e olelo mai oia ia lakou i kona inaina, A e hoomakaua mai hoi ia lakou i kona huhu nui.
Sa’an nan ya tsawata musu cikin fushinsa ya kuma razanar da su cikin hasalarsa, yana cewa,
6 Ua poni ae nei au i ka'u Alii maluna o Ziona, Maluna iho o ko'u mauna hoano.
“Na kafa Sarkina a kan kursiyi a kan Sihiyona, dutsena mai tsarki.”
7 E hai aku au i ke kauoha: Ua olelo mai la o Iehova ia'u, O oe no ka'u Keiki; I keia la no, ua hoohanau aku wau ia oe.
Sarki ya yi shelar umarnin Ubangiji. Ubangiji ya ce mini, “Kai Ɗana ne; yau na zama Mahaifinka.
8 E noi mai oe ia'u, a e haawi aku au ia oe I na lahuikanaka i hooilina nou, A i waiwai hoi nou na welelau o ka honua.
Ka tambaye ni zan kuwa sa al’ummai su zama gādonka, iyakokin duniya su zama mallakarka.
9 E uhai oe ia lakou me ke kookoo hao: E ulupa hoi oe ia lakou me he ipulepo la.
Za ka yi mulkinsu da sandan ƙarfe; za ka farfashe su kucu-kucu kamar tukunyar laka.”
10 No ia hoi, e hoonaauao oukou, e na alii; E aoia'ku no hoi oukou, e na lunakanawai o ka honua.
Saboda haka, ku sarakuna, ku yi wayo; ku shiga hankalinku, ku masu mulkin duniya.
11 E malama ia Iehova me ka weliweli, E hauoli hoi oukou me ka haalulu.
Ku bauta wa Ubangiji da tsoro ku kuma yi farin ciki kuna rawar jiki.
12 E honi aku i ke Keiki, o huhu mai ia, O make hoi oukou ia aoao, ke hoa iki ia mai kona inaina. Pomaikai wale ka poe a pau i hilinai aku ia ia.
Ku sumbaci Ɗan, don kada yă yi fushi ku hallaka a abubuwan da kuke yi, gama fushinsa zai iya kuna farat ɗaya. Masu farin ciki ne dukan waɗanda suke neman mafaka daga gare shi.

< Halelu 2 >