< Halelu 107 >
1 E MILILANI aku ia Iehova, no ka mea, ua maikai ia; Ua mau loa no hoi kona lokomaikai.
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 E olelo mai no ka poe i hoolapanaiia e Iehova, Ka poe hoi ana i hoolapanai ai, mai ka lima mai o ka enemi.
Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
3 No ka mea, ua hooili mai oia ia lakou mai na aina mai, Mai ka hikina, a me ke komohana mai, E mai ke kukulu akau, a mai ke kai mai.
su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
4 Kuewa wale lakou ma ka waonahele, Ma ke ala waoakua hoi; Aole i loaa ia lakou ke kulanakauhale kahi e noho ai.
Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
5 Pololi iho la lakou, a makewai hoi, A maule ko lakou uhane iloko o lakou.
Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
6 Alaila, kahea aku lakou ia Iehova iloko o ko lakou pilikia, A hoopakele mai oia ia lakou i ko lakou popilikia ana.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
7 Alakai mai la oia ia lakou ma ke ala pono, I hiki ai lakou i ke kulanakauhale, kahi e noho ai.
Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
8 E mililani aku na kanaka ia Iehova no kona lokomaikai, A no kana mau hana kupanaha i na keiki a kanaka!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
9 No ka mea, nana no i hookena i ka uhane makewai, A nana hoi i hoomaona i ka uhane pololi i ka maikai.
gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
10 O ka poe i noho ma ka pouli, ma ka malu hoi o ka make, A paa no hoi i ka popilikia a me ka hao;
Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
11 No ka mea, ua kipi lakou i na olelo a ke Akua, A ua hoowahawaha i ke ao ana mai o ka Mea kiekie;
gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
12 Alaila hookulou oia i ko lakou naau i ka luhi, Hina iho la lakou ilalo, aohe mea nana e kokua.
Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
13 Alaila, hea aku lakou ia Iehova i ko lakou pilikia ana, A hoola mai oia ia lakou i ko lakou popilikia ana.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
14 Hoopuka mai la oia ia lakou mailoko mai o ka pouli a me ka malu o ka make, A uhai hoi i ko lakou mea i paa ai.
Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
15 E hoalohaloha aku na kanaka ia Iehova, no kona lokomaikai, A no kana mau hana kupanaha i na keiki a kanaka!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
16 No ka mea, ua wawahi oia i na pani keleawe o na pukapa A ua uhai no hoi oia i na kaola kipuka hao.
gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
17 O ka poe i lalau ma ka aoao o ka poe hewa, A me ka lawehala, ua hoopilikiaia lakou.
Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
18 Hoopailua no ko lakou uhane i na mea ai a pau; A hookokoke no lakou i na pukapa o ka make.
Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
19 Alaila, hea aku no lakou ia Iehova i ko lakou pilikia ana, A hoola mai no oia ia lakou i ko lakou popilikia.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
20 Haawi mai la oia i kana olelo, a hoala iho la ia lakou, A hoopakele no hoi ia lakou, mai ko lakou lua aku.
Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
21 E hoalohaloha aku na kanaka ia Iehova no kona lokomaikai, A no kana mau hana kupanaha i na keiki a kanaka!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
22 E mohai aku no hoi lakou i ka mohai o ke aloha, A e hoike aku i kana mau hana me ka hauoli.
Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
23 O ka poe iho ilalo i ka moana, ma na moku, A hana i ka hana ma na moana nui;
Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
24 Ua ike no keia poe i na hana o Iehova, A mo kana mau mea kupanaha ma ka hohonu.
Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
25 No ka mea, olelo wale mai oia, a hoala i ka makani kupikipikio, A piipii aku la na ale.
Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
26 Pii aku la lakou i ka lani, a iho ilalo i ka hohonu: A hehee ko lakou uhane i ka ino.
Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
27 Hikaka lakou i o, a ia nei, a kunewanewa hoi e like me ke kanaka ona, A pau wale aku no ko lakou akamai.
Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
28 Alaila, hea aku lakou ia Iehova i ko lakou pilikia ana, A hoopakele mai oia ia lakou, mailoko mai o ko lakou popilikia.
Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
29 Hoolilo no oia i ka ino i pohu, A malie loa iho la na ale.
Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
30 Alaila, lealea lakou, no ka mea, ua malie; A hoopae no oia ia lakou ma ke awa a lakou e makemake ai.
Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
31 E mililani aku na kanaka ia Iehova no kona lokomaikai, A no kana mau hana kupanaha i na keiki a kanaka!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
32 E hapai no hoi ia ia ma ka ahakanaka, A e halelu aku ia ia ma ke anaina o ka poe kahiko.
Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
33 Hoolilo no oia i na muliwai i waonahele, A me na waipuna i aina maloo;
Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
34 A me ka aina hua nui, i aina hua ole, No ka hewa o ka poe e noho ana malaila.
ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
35 A hoolilo no hoi oia i ka waonahele, i wai lana, A me ka aina maloo hoi i wai puna.
Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
36 Malaila no oia e hoonoho ai i ka poe pololi, A hoomakaukau no hoi lakou i kulanakauhale, kahi e noho ai;
a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
37 A lulu no hoi lakou ma na mahinaai, A kauu iho no i na mala waina, A haawiia mai ka hua i hoohuaia'i.
Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
38 Hoomaikai mai la oia ia lakou, a kawowo nui ae la; Aole ia i hoemi i ka lakou poe holoholona.
ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
39 A mahope, hooemiia lakou, a hoohaahania no hoi, No ka hookaumahaia, a me ka hewa, a me ka pilikia.
Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
40 Ninini mai oia i ka hoomaau maluna o na'lii, A alakai no hoi oia ia lakou ma kahi mehameha, ala ole.
shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
41 Hookiekie nae oia i ka poe hune mailoko aku o ka pilikia, A hoolilo i kona mau ohana, me he ohana hipa la.
Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
42 E ike aku no ka poe pono, a e lealea lakou; A e paa no ka nuku o ka hewa a pau.
Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
43 Owai la ka mea akamai, a malama i keia mau mea! O lakou ka i hoomaopopo i ka lokomaikai o Iehova.
Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.