< Nehemia 8 >
1 HOAKOAKOAIA mai la ka ahakanaka a pau e like me ke kanaka hookahi ma kahi akea ma ke alo o ka puka wai; a olelo aku la lakou ia Ezera i ke kakauolelo e lawe mai i ka buke o ke kanawai o Mose, ka mea a Iehova i kauoha mai ai i ka Iseraela.
sai dukan mutane suka taru kamar mutum guda a dandali a gaban Ƙofar Ruwa. Suka faɗa wa Ezra malamin Doka yă fitar da Littafin Dokar Musa, wanda Ubangiji ya umarta domin Isra’ila.
2 A lawe mai la o Ezera ke kahuna i ke kanawai imua o ka ahakanaka o na kane a me na wahine a me na mea a pau i hiki ia lakou ke lohe a e manao iho, i ka la mua o ka malama ehiku.
Saboda haka a rana ta farko ga watan bakwai, Ezra firist, ya kawo Doka a gaban taro, wanda ya ƙunshi maza da mata da dukan waɗanda za su iya fahimta.
3 Heluhelo iho la oia iloko olaila ma ke alo o kahi akea e kupono ana i ka puka wai, mai ka wanaao a hiki i ke awakea, imua o na kane a me na wahine, a me ka poe i hiki ia lakou ke noonoo; a ma ka buke no o ke kanawai na pepeiao o ka ahakanaka a pau.
Ya karanta Dokar da ƙarfi daga safe har tsakar rana yayinda yake a kan dandali da yake fuskantar dandali a gaban Ƙofar Ruwa, gaban maza, mata da kuma sauran mutanen da za su iya fahimta. Dukan mutane kuwa suka saurara a hankali ga karatun Littafin Dokar.
4 Ku ae la o Ezera ke kakauolelo ma ka awai laau, ka mea a lakou i kukulu ai no keia hana; a ku pu ae la me ia o Matitia a me Sema a me Anaia a me Uria a me Hilekia a me Maaseia ma kona lima akau; a ma kona lima hema, o Pedaia, a me Misaela, a me Malekia, a me Hasuma a me Hasebadana, Zekaria, Mesulama.
Ezra malamin Doka ya tsaya a kan dakalin itacen da aka yi saboda wannan hidima. Kusa da shi a damansa, Mattitiya, Shema, Anahiya, Uriya, Hilkiya da Ma’asehiya suka tsaya; a hagunsa kuma Fedahiya, Mishayel, Malkiya, Hashum, Hashbaddana, Zakariya da Meshullam suka tsaya.
5 Wehe ae la o Ezera i ka buke imua o na maka o ka ahakanaka a pau; (no ka mea, maluna ae no ia o ka ahakanaka a pau; ) a i kona wehe ana, ku ae la ka ahakanaka a pau iluna:
Sai Ezra ya buɗe littafin. Dukan mutane kuwa suka gan shi domin yana tsaye a bisa fiye da inda mutane suke tsaye; yayinda ya buɗe littafin kuwa, dukan mutane suka miƙe tsaye.
6 A hoomaikai aku la o Ezera ia Iehova i ke Akua nui: a pane mai la ka ahakanaka a pau, Amene, Amene, me ka hapai ana i ko lakou mau lima iluna; a kulou iho la lakou, a hoomana aku la ia Iehova ilalo no ko lakou alo ma ka honua.
Ezra ya yabi Ubangiji, Allah mai girma; dukan mutane kuwa suka tā da hannuwansu suka amsa, “Amin! Amin!” Sa’an nan suka sunkuya suka yi wa Ubangiji sujada da fuskokinsu har ƙasa.
7 A o Iesua, a me Bani, a me Serebia, lamina, Akuba, Sabetai, Hodia, Maaseia, Kelita, Azaria, Iozabada, Hanana, Pelaia, a me na Levi, hoakaka aku la lakou i ka ahakanaka i ke kanawai; aia hoi ka ahakanaka ma ko lakou wahi.
Lawiyawa, wato, su Yeshuwa, Bani, Sherebiya, Yamin, Akkub, Shabbetai, Hodiya, Ma’asehiya, Kelita, Azariya, Yozabad, Hanan da Felahiya, suka koyar da mutane a cikin Dokar yayinda mutane suke a tsaye a can.
8 Heluhelu iho la lakou ma ka buke o ke kanawai o ke Akua me ka pololei, hoakaka'ku no i ke ano, a hoomoakaka hoi i ka heluhelu ana.
Suka karanta daga Littafin Dokar Allah, suna sa kowa ya gane, suna kuma ba da fassarar domin mutane su fahimci abin da ake karatu.
9 A o Nehemia ke kiaaina, a me Ezera ke kahuna, ke kakauolelo, a me na Levi ka poe e ao aku ana i na kanaka, olelo aku la i ka poe kanaka a pau, He la hoano no keia no Iehova ko oakou Akua; mai u, aole hoi e uwe. No ka mea, uwe iho la ka ahakanaka a pau i ko lakou lohe ana i na olelo o Ke kanawai.
Sa’an nan Nehemiya gwamna, Ezra firist da kuma wanda yake malamin Doka, da Lawiyawa waɗanda suke koyar da mutane, suka ce musu duka, “Wannan rana mai tsarki ce ga Ubangiji Allahnku. Kada ku yi makoki ko kuka.” Gama dukan mutane suna ta kuka yayinda suke sauraran kalmomin Dokar.
10 I aku la oia ia lakou, E hele aku oukou e ai i na mea momona, e inu hoi i na mea ono, a e haawi aku i kauwahi na ka poe i makaukau ole kahi mea no lakou; no ka mea, he la hoano keia no ko kakou Haku: a mai noho a kaumaha; no ka mea, o ka olioli o Iehova oia no ko oukou pakaua.
Nehemiya ya ce, “Ku koma gidajenku ku ci abinci mai kyau, ku sha abin sha mai zaƙi, ku kuma aika wa wanda ba shi da shi. Wannan rana mai tsarki ce ga Ubangijinmu. Kada ku yi baƙin ciki, gama farin cikin Ubangiji shi ne ƙarfinku.”
11 Pela i hoomalielie aku ai na Levi i ka ahakanaka a pau, i aku la, E hamau, no ka mea, he la hoano keia; mai noho a kaumaha.
Lawiyawa suka rarrashi mutane duka suna cewa, “Ku natsu, gama wannan rana ce mai tsarki. Kada ku yi baƙin ciki.”
12 A hele aku la ka ahakanaka a pau e ai, a e inu, a e haawi aku i kauwahi, a e hana i ka olioli nui, no ka mea, ua ike lakou i na olelo i haiia'ku ai ia lakou.
Sa’an nan dukan mutane suka koma gidajensu suka ci, suka sha, suka aika wa wanda ba shi da abinci, gama yanzu sun fahimci kalmomin da aka karanta musu.
13 Ai ka lua o ka la houluuluia mai la ka poe koikoi o na makua o ka ahakanaka a pau, o na kahuna a me na Levi io Ezera la i ke kakauolelo, e ike i na olelo o ke kanawai.
A rana ta biyu ga wata, shugabannin iyalai, tare da firistoci da Lawiyawa, suka taru kewaye da Ezra malamin Doka don su mai da hankali ga kalmomin Dokar.
14 A loaa ia lakou ka mea i kakauia'i ma ke kanawai, ka mea a Iehova i hauoha mai ai ma o Mose la, i noho ka Iseraela iloko o na kauhalelewa i ka ahaaina o ka hiku o ka malama:
Suka tarar a rubuce a cikin Doka wadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa, cewa Isra’ilawa su zauna a bukkoki a lokaci bikin watan bakwai
15 A i kala aku ai lakou a hai aku ma na kulanakauhale a pau o lakou, a ma Ierusalema, me ka i ana'ku, Ou haele aku i ka mauna, a e lawe mai i na lala oliva, a me na lala o ka oliva ulu wale, a me na lala hadasa, a me na lala loulu, a me na lala o ka laau ulu nui, e hana i na hale malumalu e like me ka mea i kakauia'i.
kuma cewa ya kamata su yi shelar wannan magana, su kuma yaɗa ta a duk garuruwansu da kuma cikin Urushalima cewa, “Ku fita zuwa cikin ƙasar tudu ku kawo rassa daga itatuwan zaitun da na zaitun jeji, da kuma daga dargaza, da dabino da itatuwa masu ganye, don yin bukkoki”, kamar yadda yake a rubuce.
16 A haele aku la ka ahakanaka, a lawe mai la, a hana iho la no lakou i na hale malumalu, kela kanaka keia kanaka maluna iho o kona hale, a ma ko lakou mau kahua, a ma na kahua o ka hale o ke Akua, a ma kahi akea o ka puka wai, a ma kahi akea o ka puka o Eperaima.
Sai mutanen suka fita suka dawo da rassa suka kuma yi wa kansu bukkoki a bisa rufin ɗakunansu, a cikin filaye, a shirayin gidan Allah, da ciki dandalin da yake kusa da Ƙofar Ruwa, da kuma a dandalin da yake a Ƙofar Efraim.
17 A o ka ahakanaka a pau i hoi mai la mai ka lawe pio ana mai, hana iho la lakou i na hale malumalu, a noho no hoi iloko o na hale malumalu; no ka mea, aole i hana ka Iseraela pela mai na la mai o Iosua ke keiki a Nuna a hiki mai i neia la. A nui loa iho la ka hanoli ana.
Dukan jama’ar da suka komo daga zaman bauta suka yi bukkoki suka kuma zauna a cikinsu. Daga kwanakin Yoshuwa ɗan Nun har yă zuwa yau, Isra’ilawa ba su taɓa yin bikinsa haka ba. Mutane suka cika da farin ciki sosai.
18 A heluhelu iho la oia ma ka buke o ke kanawai o ke Akua i kela la i keia la, mai ka la mua mai a hiki i ka la hope. Hana iho la lakou i ka ahaaina i na la ehiku, a i ka walu o ka la he halawai, e like me ka mea i kauohaia'i.
Kowace rana, daga rana farko zuwa ƙarshe, Ezra ya karanta daga Littafin Dokar Allah. Suka yi bikin kwana bakwai, a rana ta takwas kuma suka yi muhimmin taro bisa ga ƙa’ida.