< Mika 6 >
1 E HOOLOHE mai oukou ano i ka mea a Iehova i olelo mai ai; E ku iluna, e hakaka imua o na mauna, A e hoolohe na puu i kou leo.
Ku saurari abin da Ubangiji ya ce, “Tashi ku gabatar da ƙararku a gaban duwatsu; bari tuddai su ji abin da kuke so ku faɗa.
2 A hoolohe oukou, e na mauna i ka hoopaapaa o Iehova, A me oukou na kumu paa o ka honua: No ka mea, he hoopaapaa ko Iehova me kona poe kanaka, A e hoopaapaa no ia me ka Iseraela.
“Ku saurara, ya ku duwatsu game da tuhumar da Ubangiji yake muku, ku ji, ku daɗaɗɗun tushin duniya. Gama Ubangiji yana da ƙara a kan mutanensa; yana tuhumar Isra’ila.
3 E kuu poe kanaka, heaha ka'u i hana aku ai ia oe? Heaha ka'u i hooluhi ai ia oe? e hoike mai ia'u.
“Ya ku mutanena, me na yi muku? Ta yaya na nawaita muku? Ku amsa mini.
4 No ka mea, ua lawe mai au ia oe mai ka aina o Aigupita mai, A ua hoola au ia oe mai ka hale o na kauwa mai; A ua hoouna aku au imua ou ia Mose, ia Aarona, a me Miriama.
Na fito da ku daga ƙasar Masar na kuma’yantar da ku daga ƙasar bauta. Na aika da Musa yă jagorance ku, haka ma Haruna da Miriyam.
5 E kuu poe kanaka, e hoomanao ano i ka mea a Balaka, ke alii o Moaba, i noonoo ai, A i ka mea hoi a Balaama ke keiki a Beora i olelo mai ai ia ia, mai Sitima mai a Gilegala; I ike oukou i ka pono o Iehova.
Ya ku mutanena, ku tuna abin da Balak sarkin Mowab ya ƙulla da kuma amsar da Bala’am ɗan Beyor ya bayar. Ku tuna da tafiyarku daga Shittim zuwa Gilgal, don ku san ayyukan adalcin Ubangiji.”
6 Me ke aha la wau e hele aku ai imua o Iehova, A kulou iho imua o ke Akua kiekie? E hele anei au imua ona me na mohai kuni, Me na keiki bipi o ka makahiki hookahi?
Da me zan zo a gaban Ubangiji in rusuna a gaban Maɗaukaki Allah? Shin, zan zo ne a gabansa da hadaya ta ƙonawa, da ɗan maraƙi bana ɗaya?
7 E oluolu anei o Iehova i na tausani hipa kane? A me ka umi tausani muliwai aila? E haawi anei au i kuu makahiapo no kuu hala, I ka hua o kuu kino no ka hewa o ko'u uhane.
Ubangiji zai ji daɗin hadayar raguna dubbai da kuma rafuffukan mai dubbai goma? Zan ba da ɗan farina ne don laifina, ko’ya’yan jikina domin zunubin raina?
8 Ua hoike mai no ia ia oe, e ke kanaka, i ka mea maikai; A he aha ka mea a ke Akua i kauoha mai ai ia oe, Ke ole e hana i ka pono, a e aloha i ka lokomaikai, A e hoohaahaa i ka hele ana me ke Akua?
Ya nuna maka, ya mutum, abin da yake mai kyau. Me Ubangiji yake bukata daga gare ka kuwa shi ne ka yi gaskiya ka so aikata jinƙai ka kuma yi tafiya da tawali’u a gaban Allah.
9 Ke kahea mai nei ka leo o Iehova i ke kulanakauhale, A o ka mea naauao e ike i kou inoa; E hoolohe oukou i ka hoopai aua, a me ka mea nana ia i hoike mai.
Ku saurara! Ubangiji yana kira ga birni, a ji tsoron sunana kuwa hikima ce, “Ku kasa kunne ga sandan nan da kuma wannan wanda ya naɗa.
10 Aole anei, i keia wa, na waiwai hewa ma ka hale o ka poe hewa, A me ka epa uuku e hoowahawahaia?
Har yanzu zan manta, ya muguwar gida da dukiyarki da kika samu a muguwar hanya zan kuma manta da bugaggen mudun awo wanda ake zargi?
11 E maemae anei au me na mea kaupaona hewa, A me ka aa paona hoopunipuni?
Zan kuɓutar da mutumin da yake da ma’auni na rashin gaskiya, da kuma buhun ma’aunan ƙarya?
12 No ka mea, ua piha kona poe kanaka waiwai i ka hana ino, A ua olelo wahahee kona poe kanaka, A ua hoopunipuni ko lakou alelo ma ko lakou waha.
Attajiranta masu fitina ne; mutanenta kuma maƙaryata ne harsunansu kuwa suna yaudara.
13 No ia hoi, e hoonawaliwali au ia oe, ma ka hahau ana ia oe, Ma ka hooneoneo ana ia oe no kou hewa.
Saboda haka, zan hallaka ku in lalace ku saboda zunubanku.
14 A e ai iho oe, aole e maona; Aia no iloko ou ka maule ana; A e lawe aku oe, aole e hoopakele, A o ka mea au e hoopakele ai, oia ka'u e haawi aku no ka pahikaua.
Za ku ci amma ba za ku ƙoshi ba, cikinku zai zama babu kome Za ku tattara amma ba za ku yi ajiyar kome ba, gama abin da kuka yi ajiya zan ba wa takobi.
15 E lulu iho no oe, aka, aole oe e ohi mai; E hehi iho oe i na oliva, aole nae e poniia oe i ka aila; A i ka waina hou, aole nae oe e inu i ka waina.
Za ku yi shuki amma ba za ku girba ba; za ku matse zaitun amma ba za ku yi amfani da mai wa kanku ba, za ku tattaka’ya’yan inabi amma ba za ku sha ruwan inabin ba.
16 No ka mea, ua malamaia na kanawai o Omeri, A me na hana a pau a ko ka hale o Ahaba, A ua hele oukou ma ko lakou manao; Nolaila, e hoolilo aku ai au ia oe i neoneo, A i kona poe kanaka i mea hoowahawahaia; A e lawe oukou i ka hoino o kuu poe kanaka.
Kuna kiyaye ƙa’idodin Omri da dukan ayyukan gidan Ahab kun kuma bi al’adunsu. Saboda haka, zan maishe ku kufai in mai da ku abin dariya a cikin mutane, za ku sha reni a wurin al’ummai.”