< Lunakanawai 9 >

1 HELE aku la o Abimeleka, ke keiki a Ierubaala, i Sekema, i na hoahanau o kona makuwahine, a ohumu pu iho la me lakou a me ka ohana a pau o ka makuakane o kona makuwahine, i ae la,
Abimelek ɗan Yerub-Ba’al ya tafi Shekem wurin’yan’uwan mahaifiyarsa, ya ce musu da kuma dukan dangin mahaifiyarsa,
2 Ke noi aku nei au ia oukou, e olelo aku oukou ma na pepeiao o na kanaka o Sekema, Heaha ka maikai ia oukou, i lilo na kanaka, he kanahiku, i alii maluna o oukou, oia hoi na keiki a pau o Ierubaala, i lilo paha ke kanaka hookahi i alii maluna o oukou? E hoomanao hoi, no ko oukou iwi au, a no ko oukou io.
“Ku tambayi’yan ƙasar Shekem, ‘Wanne ya fi muku, a sa dukan’ya’yan Yerub-Ba’al saba’in maza su yi mulkinku, ko dai mutum guda kawai yă yi mulkinku?’ Ku tuna, ni jininku ne.”
3 Olelo aku la na hoahanau o kona makuwahine nona, ma na pepeiao o na kanaka a pau o Sekema, i keia mau olelo a pau. Hahai aku la ko lakou naau mamuli o Abimeleka; no ka mea, i ae la lakou, Oia ko kakou kaikaina.
Sa’ad da’yan’uwan suka mayar wa’yan ƙasar Shekem wannan, sai suka goyi bayan Abimelek, gama sun ce, “Shi ɗan’uwanmu ne.”
4 Haawi mai la lakou ia ia i kanahiku moni, noloko mai o ka hale o Baalaberita, a me ia o Abimeleka i hoolimalima aku ai i kanaka hewa, lapuwale, a hahai aku la lakou mamuli ona.
Suka ba shi shekel saba’in na azurfa daga haikalin Ba’al-Berit, Abimelek kuwa ya yi amfani da shi ya yi hayar’yan tauri waɗanda suka zama masu binsa.
5 Hele aku la oia i ka hale o kona makuakane, ma Opera, a pepehi aku la i kona poe hoahanau, i na keiki a Ierubaala, he kanahiku kanaka, ma ka pohaku hookahi. Koe no nae o Iotama ke keikikane muli loa a Ierubaala, no ka mea, ua pee oia.
Sai ya tafi gidan mahaifinsa a Ofra kuma a dutse guda ya kashe’yan’uwansa,’ya’yan Yerub-Ba’al. Amma Yotam, autan ɗan Yerub-Ba’al ya tsira ta wurin ɓuya.
6 Akoakoa mai la na kanaka a pau o Sekema, a me ko ka hale a pau o Milo, a hele ae la, a hoalii iho la ia Abimeleka ma ka laau oka, ma ka pakaua o Sekema.
Sa’an nan duka’yan ƙasar Shekem da Bet Millo suka taru kusa da babban itacen wajen ginshiƙi a Shekem don a naɗa Abimelek sarki.
7 A hai ae la lakou ia Iotama, alaila, hele aku la ia, a ku iho la maluna o ka piko o ka mauna o Gerizima, a hookiekie ae la i kona leo, hea aku la, i aku la ia lakou, E hoolohe mai oukou ia'u, e na kanaka o Sekema, a e hoolohe mai hoi ke Akua ia oukou.
Sa’ad da aka gaya wa Yotam wannan, sai ya hau Dutsen Gerizim ya yi kira da ƙarfi ya ce, “Ku saurare ni,’yan ƙasar Shekem, don Allah yă saurare ku.
8 Hele aku la na laau e poni i alii no lakou. I aku la lakou i ka laau oliva, I alii oe maluna o makou.
Wata rana itatuwa suka fita don su naɗa wa kansu sarki. Suka ce wa itacen zaitun, ‘Ka zama sarkinmu.’
9 I mai la ka laau oliva ia lakou, E haalele anei au i ko'u momona, ka mea a lakou e hoomaikai ai i ke Akua, a me kanaka, ma o'u nei, a hele e hoalii maluna o na laau?
“Amma itacen zaitun ya ce, ‘In bar mai nawa, wanda da shi ake girmama alloli da mutane, don in zo in yi ta fama da itatuwa?’
10 Alaila, olelo aku la na laau i ka laau fiku, E hele mai oe e noho alii maluna o makou.
“Biye da wannan, sai itatuwan suka ce wa itacen ɓaure, ‘Zo ka zama sarkinmu.’
11 I mai la ka laau fiku ia lakou, E haalele anei au i ko'u ono, a me ko'u hua maikai, a hele e noho alii maluna o na laau?
“Amma itacen ɓauren ya ce, ‘In bar kyawawan’ya’yana da zaƙinsu, in zo in yi ta fama da itatuwa?’
12 Alaila, olelo aku la na laau i ke kumu waina, E hele mai oe, a noho i alii maluna o makou.
“Sa’an nan itatuwan suka ce wa kuringar inabi, ‘Ki zo ki zama sarkinmu.’
13 I mai la ke kumu waina ia lakou, E haalele anei au i ko'u waina, ka mea e lealea ai ke Akua a me kanaka, a hele e noho alii maluna o na laau?
“Amma kuringar ta ce, ‘In bar ruwan inabina, wanda yake faranta zuciyar alloli da mutane, in zo in yi fama da itatuwa?’
14 Alaila, olelo aku la na laau a pau i ka laauooi, E hele mai oe a noho alii maluna o makou.
“A ƙarshe sai dukan itatuwa suka ce wa itacen ƙaya, ‘Ka zo ka zama sarkinmu.’
15 I mai la ka laauooi i na laau, Ina e poni oiaio mai oukou ia'u, i alii maluna o oukou, alaila, e hele mai oukou e kanaho malalo iho o ko'u malu; a i ole hoi, alaila, e puka aku no ke ahi, mai ka laauooi aku, a hoopau i na laau kedera o Lebanona.
“Itacen ƙaya ya ce wa itatuwan, ‘In da gaske ne kuke so ku naɗa ni sarkinku, ku zo ku sha inuwana; in ba haka ba, bari wuta ta fito daga itacen ƙaya ta cinye itacen al’ul na Lebanon!’
16 Ina i hana oukou me ka oiaio, a me ka pono, i ko oukou hoalii ana ia Abimeleka, a ina i hana maikai oukou ia Ierubaala, a me kona poe, a ina i hana oukou ia ia e like me ka pono o kona mau lima:
“To, da a ce kun yi abin bangirma da aniya mai kyau sa’ad da kuka naɗa Abimelek sarki, da kun nuna wa Yerub-Ba’al da iyalinsa ladabi, da kuma kun yi masa abin da ya cancanci shi,
17 (No ka mea, kaua no ko'u makuakane no oukou, a kiola aku la i kona ola iho, a hoopakele ia oukou, mai ka lima ae o ko Midiana;
a yi tunani cewa mahaifina ya yi yaƙi saboda ku, ya yi kasai da ransa don yă cece ku daga hannun Midiyawa
18 A ua ku mai oukou i keia la, e ku e i ko ka hale o ko'u makuakane, a ua luku mai i kana poe keikikane, he kanahiku, maluna o ka pohaku hookahi, a ua hoolilo ia Abimeleka, i ke keiki a kana haia wahine, i alii maluna o kanaka o Sekema, no ka mea, o ko oukou hoahanau ia; )
(amma ga shi yau kun tayar wa iyalin mahaifina, kuka kashe’ya’yansa saba’in a dutse guda, kuka kuma naɗa Abimelek, ɗan baiwa, sarki a kan’yan ƙasar Shekem domin shi ɗan’uwanku ne)
19 Nolaila, ina i hana oukou i keia la me ka oiaio, a me ka pono ia Ierubaala, a me ko kona hale, alaila, e olioli oukou ia Abimeleka, a e olioli no hoi oia ia oukou:
in har kun aikata wannan cikin bangirma da kuma aminci wajen Yerub-Ba’al da iyalinsa a yau, bari Abimelek yă zama farin cikinku, ku kuma nasa!
20 A i ole, alaila, e puka mai ke ahi mai Abimeleka mai, a e hoopau i na kanaka o Sekema, a me ko ka hale o Milo; a e puka mai ke ahi mai na kanaka mai o Sekema, a mai ka hale mai o Milo, a e hoopau ia Abimeleka.
Amma in ba haka ba, bari wuta ta fito daga Abimelek ya cinye ku,’yan ƙasar Shekem da Bet Millo, bari wuta kuma daga wurinku’yan ƙasar Shekem da Bet Millo ta cinye Abimelek!”
21 Holo aku la o Iotama, a pee aku la, a hele aku i Beera, a noho iho la malaila, no ka makau ia Abimeleka i kona hoahanau.
Sa’an nan Yotam ya gudu, ya tsere zuwa Beyer ya zauna a can gama yana tsoron ɗan’uwansa Abimelek.
22 A noho alii o Abimeleka maluna o ka Iseraela, i ekolu makahiki,
Bayan Abimelek ya yi shekara uku yana mulki a Isra’ila,
23 Alaila, haawi mai la ke Akua i manao hewa mawaena o Abimeleka, a me na kanaka o Sekema; a hana hoopunipuni aku la na kanaka o Sekema ia Abimeleka:
sai Allah ya aiko da mugun ruhu tsakanin Abimelek da’yan ƙasar Shekem, waɗanda suka ci amanar Abimelek.
24 I kau mai ka lokoinoia o na keiki a Ierubaala, he kanahiku, a me ko lakou koko, i kau mai ia maluna o Abimeleka, o ko lakou kaikaina, ka mea i luku mai ia lakou, a maluna hoi o na kanaka o Sekema, ka poe i hooikaika i kona lima e luku i kona poe hoahanau.
Allah ya yi haka saboda kisan’ya’ya saba’in na Yerub-Ba’al, don a ɗauki fansar jininsu a kan Abimelek ɗan’uwansu da kuma’yan ƙasar Shekem, waɗanda suka taimake shi kisan’yan’uwansa.
25 Hoonoho iho la na luna o Sekema i poe hoohalua ia ia, maluna iho o na mauna; a hoohalua aku la lakou i ka poe a pau i hele ae ma ia ala io lakou la, a ua haiia ia Abimeleka.
Cikin hamayya da shi waɗannan’yan ƙasar Shekem suka sa mutane a kan tuddai don su yi kwanton ɓauna a kan su yi fashi ga duk wanda ya wuce a can, wannan fa ya kai kunnen Abimelek.
26 Hele mai la o Gaala ke keiki a Ebeda, oia, a me kona poe hoahanau, hele ae la lakou, a Sekema; a hilinai na kanaka o Sekema ia ia.
To, Ga’al ɗan Ebed ya tafi tare da’yan’uwansa zuwa Shekem,’yan ƙasarta kuwa suka dogara da shi.
27 Hele aku la lakou i na mahinaai, hoiliili ae la i ko ka malawaina o lakou, hahi iho la, a hula ae la, a komo aku la iloko o ka hale o ko lakou akua, ai iho la, a inu, a hoino aku la ia Abimeleka.
Bayan sun tafi gonaki suka tattara inabi suka matse su, sai suka yi biki a haikalin allahnsu. Yayinda suke ci da sha, sai suka la’anci Abimelek.
28 I mai la Gaala, ke keiki a Ebeda, Owai o Abimeleka, a owai hoi o Sekema, i malama aku kakou ia ia? Aole anei ia ke keiki a Ierubaala, a o Zebula kona luna? E malama oukou i kanaka o Hamora, i ka makuakane o Sekema. No ke aha kakou e malama ia ia nei?
Sa’an nan Ga’al ɗan Ebed ya ce, “Wane ne Abimelek, kuma wane ne Shekem, da za mu bauta masa? Shi ba ɗan Yerub-Ba’al ba ne, kuma ba Zebul ne mataimakinsa ba? Ku bauta wa mutanen Hamor, mahaifin Shekem! Me ya sa za mu bauta wa Abimelek?
29 Ina e noho ana keia poe kanaka malalo iho o ko'u lima! alaila, kipaku aku au ia Abimeleka. I aku la oia ia Abimeleka, E hoomahuahua oe i kou poe koa, a e puka mai iwaho.
Da a ce waɗannan mutane suna a ƙarƙashina mana! Da zan hamɓarar da shi. In ce wa Abimelek, ‘Ka tara dukan mayaƙanka!’”
30 A lohe o Zebula, ka luna o ia kulanakauhale, i na olelo a Gaala, ke keiki a Ebeda, wela iho la kona huhu.
Sa’ad da Zebul gwamnar birnin ya ji abin da Ga’al ɗan Ebed ya ce, sai ya fusata.
31 Hoouna aku la ia i mau elele ia Abimeleka, me ka wahahee aku, i aku la, Aia hoi, o Gaala, ke keiki a Ebeda, a me kona poe hoahanau, ua hele mai i Sekema; aia hoi e hoopilikia ana lakou i ke kulanakauhale, e ku e ia oe.
Asirce sai ya aiki manzanni wajen Abimelek, yana cewa, “Ga’al ɗan Ebed da’yan’uwansa sun zo Shekem suna kuma zuga birnin sun tayar maka.
32 Nolaila, e ala oe i ka po, o oe, a me na kanaka pu me oe, a e hoohalua ma ke kula.
To, in dare ya yi, sai ka zo da mutanenka ku yi kwanto a filaye.
33 A i kakahiaka, i ka puka ana a ka la, alaila, e ala koke oe a e kaua aku i ua kulanakauhale la, aia puka mai ia iwaho, a me ka poe kanaka me ia, e ku e ia oe, alaila, e hana aku oe ia lakou i ka mea i loaa i kou lima.
Kashegari da safe, sai ku tashi ku fāɗa wa birnin. Sa’ad da Ga’al da mutanensa suka faɗa maka, sai ka yi abin da ka iya yi da su.”
34 Ala mai la o Abimeleka i ka po, a me na kanaka a pau pu me ia, a hoohalua lakou ia Sekema, eha poe lakou.
Saboda haka Abimelek da dukan mutanensa suka tashi da dare suka ɓuya kusa da Shekem a ƙungiyoyi huɗu.
35 Hele aku la o Gaala, ke keiki a Ebeda iwaho, a ku ma kahi e komo ai i ka puka o ke kulanakauhale. Ala mai la o Abimeleka, mai kona hoohalua ana, a me na kanaka pu me ia.
To, Ga’al ɗan Ebed ya riga ya fita waje yana tsaye a ƙofar birni daidai Abimelek da mayaƙansa suka fito daga inda suka ɓuya.
36 A ike aku la o Gaala i na kanaka, i ae la ia ia Zebula, Aia hoi, ke iho mai la na kanaka, mai ka piko o ka mauna mai. I ae la o Zebula ia ia, O ke aka o na mauna kau e ike nei, me he poe kanaka la.
Sa’ad da Ga’al ya gan su, sai ya ce wa Zebul, “Duba, ga mutane suna gangarowa daga kan duwatsu!” Zebul ya ce, “Kana ɗaukan inuwan duwatsu kana ce mutane.”
37 Olelo hou aku o Gaala, i aku la, Aia, ke iho mai nei na kanaka mawaena pono o ka aina, a aia kekahi poe, ke hele mai la, ma ka laau oka o Meonenima.
Amma Ga’al ya sāke magana ya ce, “Duba, mutane suna gangarowa daga tsakiyar filaye, kuma wata ƙungiya tana zuwa daga wajen itacen masu duba.”
38 Alaila, olelo mai o Zebula ia ia, Auhea hoi kou waha, ka mea au i olelo ai, Owai o Abimeleka, i hookauwa aku kakou nana? Aole anei keia ka poe kanaka au i hoowahawaha ai? O ko'u manao, e hele aku oe iwaho, a kaua aku ia lakou.
Sa’an nan Zebul ya ce masa, “Ina bakin da ka yi ɗin, kai da ka ce, ‘Wane ne Abimelek da za mu bauta masa.’ Ba mutanen ne ka yi musu ba’a ba? Fita, ka yaƙe su mana!”
39 Hele aku la o Gaala imua o na kanaka o Sekema, a kaua aku la ia Abimeleka.
Saboda haka Ga’al ya fito da’yan ƙasar Shekem suka yaƙi Abimelek.
40 Hahai mai la o Abimeleka ia ia, a hee ae la keia imua ona, a nui ka poe i oia, a hina ilalo, a hiki i ke komo ana i ka puka.
Abimelek ya kore shi, mutane da yawa suka ji ciwo a yaƙin, har zuwa ƙofar birnin.
41 Noho iho la o Abimeleka ma Aruma. Kipaku aku la o Zebula ia Gaala, a me kona poe hoahanau, i noho ole lakou ma Sekema.
Abimelek ya zauna a Aruma, Zebul kuwa ya kori Ga’al da’yan’uwansa daga Shekem.
42 A ia la iho, hele aku la na kanaka, a i kahi papu, a ua haiia ia Abimeleka.
Kashegari mutanen Shekem suka tafi gonaki, aka kuwa gaya wa Abimelek.
43 Alaila mahele ae la ia i kanaka, ekolu poe, hoohalua iho la ma kahi papu. Nana aku la oia, aia hoi, ua puka mai na kanaka, mailoko mai o ke kulanakauhale. Ala ae la keia e ku e ia lakou, a luku aku la ia lakou.
Saboda haka ya ɗauki mutanensa, ya raba su ƙungiya uku, sa’an nan ya yi kwanto a gonakin. Sa’ad da ya ga mutanen suna fitowa daga birni, sai ya yi wuf ya fāɗa musu.
44 A o Abimeleka a me ka poe pu me ia, hoouka iho la lakou, a ku ma kahi e komo aku i ka puka o ke kulanakauhale. A lele aku la kela mau poe elua, maluna o na mea a pau ma ke kula, a luku iho la ia lakou.
Abimelek da ƙungiyoyin da suke tare da shi suka yi maza suka yi tsaya a ƙofar birnin. Sa’an nan ƙungiyoyi biyu suka ruga suka fāɗa wa waɗanda suke a gonaki suka karkashe su.
45 Kaua aku la o Abimeleka i ke kulanakauhale, a po ia la, a hoopio iho la ia kulanakauhale, a luku ae la i na kanaka a pau maloko, a wawahi aku la i ke kulanakauhale, a lulu iho la i ka paakai malaila.
Dukan yinin, Abimelek ya matsa yaƙi da birnin sai da ya cinye ta ya kuma kashe mutanenta. Sa’an nan ya hallaka birnin ya barbaza gishiri a kanta.
46 A lohe na kanaka a pau o ka halekiai o Sekema, alaila komo lakou iloko o kahi kaua o ka hale akua o Berita.
Da jin haka, sai’yan ƙasa a hasumiyar Shekem suka shiga wurin mafaka a hankalin El-Berit.
47 Haiia'ku la ia Abimeleka, ua akoakoa na kanaka a pau o ka halekiai o Sekema.
Da Abimelek ya ji dukan mutanen hasumiyar Shekem sun taru a can,
48 Pii aku la o Abimeleka i ka mauna o Zalemona, oia, a me na kanaka a pau pu me ia; a lawe o Abimeleka i ke koi lipi ma kona lima, a kua iho la i lala laau, a hapai ae la, a kau iluna o kona a-i, a olelo aku la i kanaka, O ka mea a oukou i ike mai ai ia'u, e hana ana, e wikiwiki oukou e hana, e like me au nei.
sai Abimelek da dukan mutanensa suka haura zuwa Dutsen Zalmon. Sai ya ɗauki gatari ya sassare waɗansu rassa, waɗanda ya sa a kafaɗunsa. Ya umarci mutanen da suke tare da shi ya ce, “Sauri, ku yi abin da kuka ga na yi!”
49 Oki iho la na kanaka a pau, o kela kanaka o keia kanaka, i kana lala, a hahai lakou ia Abimeleka, a waiho iho la ia mau mea ma ka hale kaua, a puhi iho la i ka hale kaua i ke ahi maluna o lakou. Pela i make ai na kanaka a pau o ka halekiai o Sekema, hookahi tausani kane a me na wahine.
Saboda haka mutanen suka sassare rassan itatuwa suka bi Abimelek. Suka tattara su a jikin mafakar suka kuma cinna mata wuta a kan mutanen da suke a ciki. Ta haka dukan mutanen da suke cikin hasumiyar Shekem, wajen maza da mata dubu ɗaya suka mutu.
50 Alaila, hele aku la o Abimeleka, a Tebeza, a kaua aku la ia Tebeza, a hoopio iho la ia wahi.
Biye da wannan Abimelek ya tafi Tebez, ya kewaye ta ya kuma cinye ta da yaƙi.
51 Aia maloko o ia kulanakauhale he halekaua ikaika, a malaila no i pee aku ai na kane a pau a me na wahine, a me na mea a pau o ke kulanakauhale, a pani iho la mahope o lakou, a pii aku la i kahi maluna o ka halekaua.
A cikin birnin, akwai wata hasumiya mai ƙarfi, inda dukan maza da mata, dukan mutanen birnin, suka ɓuya. Suka kulle kansu, suka kuma hau rufin hasumiyar.
52 Hele mai la o Abimeleka i ka halekaua, a kaua mai la ia, a hele kokoke mai i ka puka o ka halekaua, e puhi ia mea i ke ahi.
Abimelek ya je wajen hasumiya ya kuma auka mata. Amma da ya yi kusa da ƙofar hasumiyar don yă cinna mata wuta,
53 A hoolei iho la kehahi wahine i ka pohaku kaa palaoa maluna iho o ke poo o Abimeleka, a wawahi i kona iwipoo.
sai wata mata ta saki ɗan dutsen niƙa a kan Abimelek ta fasa ƙoƙon kansa.
54 Alaila, hea koke ae la ia i ke kanaka ui i lawe i kona kahiko kaua, i aku la ia ia, E unuhi oe i kou pahi a e pepehi mai ia'u, i olelo ole mai ai na kanaka no'u, Na ka wahine ia i pepehi. Hou aku la kona kanaka ia ia, a make ia.
Da sauri ya kira mai riƙon masa makami ya ce, “Zaro takobinka ka kashe ni, don kada a ce ‘Mace ce ta kashe shi.’” Saboda haka bawansa ya soke shi, ya mutu.
55 A ike na kanaka o ka Iseraela ua make o Abimeleka, alaila hoi aku kela kanaka, keia kanaka i kona wahi.
Sa’ad da Isra’ilawa suka ga Abimelek ya mutu, sai suka tafi gida.
56 Pela i hoopai ai ke Akua i ka hewa o Abimeleka, ana i hana aku ai i kona makuakane, i kona pepehi ana i kona poe hoahanau he kanahiku.
Ta haka Allah ya sāka muguntar da Abimelek da ya yi wa mahaifinsa ta wurin kisan’yan’uwansa saba’in.
57 A hoopai no hoi ke Akua i ka hewa a pau o na kanaka o Sekema maluna o ko lakou poo iho. A maluna o lakou i hiki mai ai hoi ka hoino a Iotama, ke keiki a Ierubaala.
Allah kuma ya sa muguntar mutanen Shekem suka koma kansu. La’anar Yotam ɗan Yerub-Ba’al kuma ta kama su.

< Lunakanawai 9 >