< Iosua 9 >

1 A LOHE na'lii a pau loa ma keia aoao o Ioredane, ma na mauna, a ma na awawa, a makai ma kahi e pili ana i ka moana nui ma ke alo o Lebanona, o ka Heta, a me ka Amora, a me ko Kanaana, a me ka Pereza, a me ka Heva, a me ka Iebusa,
To, sa’ad da dukan sarakunan yammancin Urdun suka ji waɗannan abubuwa, sai waɗanda suke kan tudu, da na cikin kwari a yammanci, da dukan waɗanda suke gefen Bahar Rum har zuwa Lebanon (sarakunan Hittiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa)
2 Alaila, hoakoakoa mai la lakou e kaua lokahi mai ia Iosua, a me ka Iseraela.
suka haɗa kansu don su yaƙi Yoshuwa da Isra’ila.
3 A lohe ka poe i noho ma Gibeona i ka mea a Iosua i hana'i ia Ieriko a me Ai,
Amma da mutanen Gibeyon suka ji abin da Yoshuwa ya yi wa Yeriko da Ai,
4 Alaila hana maalea iho la lakou, a hele aku la, hoomakaukau iho la i o na lakou; a lawe no hoi lakou i na puolo kahiko ma ko lakou mau hoki, a me na hueili waina kahiko, a ua haehae, a ua pahonoia;
sai suka shirya wata dabara ta ruɗu, suka shirya ɗan abinci don tafiya, suka ɗauki tsofaffin buhuna a kan jakunansu da tsofaffin salkuna na ruwan inabi, yagaggu da suka sha ɗinki.
5 A me na kamaa kahiko, a hawele iho la ma ko lakou kapuwai, a aahu iho la i ka lole kahiko; a o ka berena, ka lakou ai, ua maloo a okaoka.
Suka sa tsofaffin takalman da suka sha gyara, suka sa tsofaffin tufafi. Dukan abincinsu na tafiya ya bushe ya yi fumfuna.
6 A hele mai la lakou io Iosua la, ma kahi a lakou i hoomoana'i ma Gilegala, i mai la ia ia, a me na kanaka o ka Iseraela, Ua hele mai nei makou, mai ka aina loihi mai; no ia mea, e hana kakou i olelo kuikahi.
Sai suka je wurin Yoshuwa a sansanin Gilgal suka ce masa da mutanen Isra’ila, “Daga ƙasa mai nisa muka fito, yanzu fa, sai ku yi alkawari da mu.”
7 I aku la na kanaka o ka Iseraela i ka poe Heva, Ke noho nei paha oukou iwaena o makou: pehea la makou e hana'i me oukou i olelo kuikahi?
Mutanen Isra’ila kuwa suka ce wa Hiwiyawa, “Wataƙila kuna kusa da mu, ta yaya za mu yi alkawari da ku?”
8 I mai la lakou ia Iosua, He poe kauwa makou nau. I aku la o Iosua ia lakou, Owai oukou? a mai hea mai oukou i hele mai nei?
Suka ce wa Yoshuwa, “Mu bayinku ne.” Amma Yoshuwa ya tambaye su ya ce, “Ku wane ne, kuma daga ina kuka zo?”
9 I mai la lakou ia ia, O kau poe kauwa nei, ua hele mai makou, mai ka aina loihi loa mai, no ka inoa o Iehova o kou Akua: no ka mea, ua lohe makou i kona kaulana ana, a me na mea a pau ana i hana'i ma Aigupita,
Suka amsa suka ce, “Bayinka sun zo ne daga ƙasa mai nisa gama Ubangiji Allahnka ya yi suna sosai. Gama mun ji labarin abubuwan da ya yi. Dukan abubuwan da ya yi a Masar
10 A me na mea a pau ana i hana aku ai i na'lii elua o ka Amora, mao aku o Ioredane, ia Sihona, ke alii o Hesebona, a me Oga, ke alii o Basana, aia ma Asetarota.
da kuma duk abubuwan da ya yi wa sarakuna biyu na Amoriyawa gabas da Urdun, Sihon sarkin Heshbon, da Og sarkin Bashan wanda ya yi mulki a Ashtarot.
11 Nolaila i olelo mai ai ko makou poe lunakahiko, a me ka poe a pau i noho i ko makou aina, i mai la ia makou, E lawe oukou ma ko oukou lima i o na oukou ma ke ala, a e hele e halawai me lakou, a e i aku ia lakou, O ka oukou kauwa makou, e hana kakou i olelo kuikahi.
Dattawanmu da duk mazaunan ƙasar, suka ce mana, ‘Ku ɗauki abincin tafiyar da za ku riƙe; ku je ku same su ku ce musu, “Mu bayinku ne, ku yi alkawari da mu.”’
12 O keia berena a makou, o ka makou o noloko mai o ko makou hale, ua hoomakaukau hou ia no makou, i ko makou la i hele mai ai e halawai me oukou, aia hoi, ua maloo, a ua helelei.
Abincin tafiyan nan namu yana da ɗumi lokacin da muka kintsa tashi daga gida a ranar da za mu kama hanya zuwa wurinku. Amma yanzu duba yadda ya bushe, ya yi fumfuna.
13 O keia mau hueili waina hoi, a makou i ukuhi hou ai, aia, ua nahaehae. A o keia mau aahu o makou, a me ko makou kamaa, ua weluwelu, no ka loihi loa o ke ala.
Waɗannan salkuna kuma da muka cika ruwan inabi, sababbi ne amma duba yadda suka yayyage. Tufafinmu da takalmanmu duk sun yayyage don doguwar tafiya.”
14 Lawe no na kanaka i ka lakou ai, aole hoi i ninau aku ma ka waha o Iehova.
Mutanen Isra’ila suka ɗiba daga cikin abincin tafiyar amma ba su nemi nufin Ubangiji ba.
15 Hoomalu aku la o Iosua ia lakou, a hana iho la i olelo kuikahi me lakou, e ola'i lakou; a hoohiki aku la na luna o ka Iseraela ia lakou.
Sa’an nan Yoshuwa ya yi alkawari zaman salama da su, cewa ba zai kashe su ba, sai shugabannin mutanen Isra’ila kuwa suka tabbatar musu da haka ta wurin yin rantsuwa.
16 A mahope iho, i ka pau ana o na la ekolu, mai ka wa mai o ka lakou hana ana i ka olelo kuikahi, alaila lohe o Iosua ma, he kamaaina lakou, a ua noho pu me lakou.
Kwana uku bayan sun yi alkawari da Gibeyonawa, sai Isra’ilawa suka ji cewa Gibeyonawa maƙwabtansu ne, waɗanda suke zaune kurkusa da su.
17 Hele ae la na mamo a Iseraela, a po akolu hiki i ko lakou mau kulanakauhale. Eia ko lakou mau kulanakauhale, o Gibeona, o Hepira, o Beerota a me Kiriatiarima.
Saboda haka Isra’ilawa suka tashi a rana ta uku suke je biranen mutanen, wato, Gibeyon, Kefira, Beyerot da Kiriyat Yeyarim.
18 Aole i pepehi aku na mamo a Iseraela, no ka mea, ua hoohiki ia lakou na luna o ka Iseraela, ma Iehova, ke Akua o Iseraela. Ohumu iho la na kanaka a pau i na luna.
Amma Isra’ilawa ba su kai musu hari ba domin shugabanninsu sun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila. Mutane Isra’ila duka kuwa suka yi gunaguni a kan shugabannin.
19 Aka, olelo mai la na luna a pau i kanaka a pau, Ua hoohiki no makou ia lakou, ma Iehova, ke Akua o Iseraela. Nolaila aole pono e hoopa aku kakou ia lakou.
Amma shugabanni suka amsa musu suka ce, “Mun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, saboda haka ba za mu taɓa su ba yanzu.
20 Eia ka kakou e hana aku ai ia lakou. E hoola no kakou ia lakou, o huhuia mai kakou, no ka hoohiki ana a makou i hoohiki ai ia lakou.
Ga abin da za mu yi musu, za mu bar su da rai don kada fushin Allah yă sauka a kanmu gama mun riga mun rantse musu.”
21 I mai la na luna i ka Iseraela, E ola no lakou, aka, e lilo no lakou i poe kalai laau, a i poe huki wai, no ke anainakanaka a pau, e like me ka na luna i olelo aku ai ia lakou.
Suka ƙara da cewa, “Mu bar su da rai, amma bari su zama masu yankan itace da masu ɗibo mana ruwa.” Haka shugabannin suka cika alkawarinsu.
22 Kii aku la o Iosua ia lakou, ninau aku la, me ka i ana aku ia lakou, No ke aha la oukou i nolu mai ai a puni makou, me ka olelo mai, Ua loihi aku makou, mai o oukou aku; a eia hoi oukou, ke noho nei iwaena o makou?
Yoshuwa kuwa ya aika aka kira Gibeyonawa ya ce musu, “Don me kuka ruɗe mu kuka ce, ‘Mun zo ne daga wuri mai nisa,’ bayan kuwa kuna nan kurkusa da mu?
23 No ia mea e poino auanei oukou, aole loa e kuuia kekahi o oukou; e lilo no oukou i poe kauwa, a i poe kalai laau, a i poe huki wai, no ka hale o ko'u Akua.
Yanzu ku la’anannu ne. Ba za ku daina zama mana masu yankan itace da kuma masu ɗebo ruwa domin haikalin Allahnmu ba.”
24 Olelo mai lakou ia Iosua, i mai la, No ka hai maopopo ia mai i kau poe kauwa nei, ka mea a Iehova kou Akua i kauoha mai ai i kana kauwa ia Mose, e haawi mai i ka aina a pau no oukou, a e luku hoi i na kanaka a pau o ka aina, imua o oukou; nolaila, i makau loa ai makou i ko makou ola, no oukou, a ua hana hoi i keia mea.
Suka amsa wa Yoshuwa suka ce, “An gaya wa bayinka dalla-dalla yadda Ubangiji Allahnka ya umarci bawansa Musa yă ba ka ƙasar duka, ka kuma kashe duk masu zama a cikinta, muka ji tsoro cewa za ka kashe mu shi ya sa muka yi haka.
25 Eia hoi makou iloko o kou lima; a o ka mea pono a pololei hoi i kou manao, o kau ia e hana mai ai ia makou.
Yanzu, a hannunka muke, ka yi duk abin da ka ga ya yi maka kyau.”
26 A pela no ia i hana aku ai ia lakou, a hoopakele ia lakou, mai ka lima ae o na mamo a Iseraela, i pepehi ole aku lakou.
Yoshuwa kuwa ya cece su daga hannun Isra’ilawa, har ba su kashe su ba.
27 Ia la, hoolilo iho la o Iosua ia lakou i poe kalai laau, a i poe huki wai no na kanaka, a no ke kuahu o Iehova, ma kahi ana i makemake ai, pela no, a hiki loa mai i neia la.
A ranar Yoshuwa ya sa Gibeyonawa suka zama masu yankan itace da ɗebo ruwa wa jama’ar Isra’ila da kuma domin haikalin Ubangiji a inda Ubangiji zai zaɓa. Abin da suke ke nan har wa yau.

< Iosua 9 >