< Iosua 5 >
1 A LOHE na'lii a pau o ka Amora, ka poe i noho ma ia aoao o Ioredane ma ke komohana, a me na'lii a pau o ko Kanaana, ka poe i noho makai, i hoomaloo o Iehova i na wai o Ioredane, mamua o na mamo a Iseraela, a pau kakou i ka hele ae, maule iho la ko lakou naau, aole hoi i koe ke aho iloko o lakou imua o na mamo a Iseraela.
To, da dukan sarakunan Amoriyawa na yammancin Urdun, da dukan sarakunan Kan’aniyawan da suke bakin teku suka ji yadda Ubangiji ya busar da kogin Urdun a gaban Isra’ilawa, har sai da dukansu suka ƙetare, zuciyarsu ta narke, suka karaya sosai har ma suka rasa samun ƙarfin hali su fuskanci Isra’ilawa.
2 Ia manawa, olelo mai la o Iehova ia Iosua, E hana oe i mau pahi oi nau, a e okipoepoe hou i na mamo a Iseraela, o ka lua ia.
A lokacin nan Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Ka yi wuƙaƙe na duwatsu ka yi wa Isra’ilawa kaciya.”
3 Hana iho la o Iosua i mau pahi oi, a okipoepoe mai la i na mamo a Iseraela, ma ka puu omaka.
Sai Yoshuwa ya yi wuƙaƙe na duwatsu, ya yi wa Isra’ilawa kaciya a Gibeyat-Ha’aralot.
4 No keia mea hoi i okipoepoe ai o Iosua ia lakou; o na kanaka a pau i hele mai, mai Aigupita mai, o ka poe kane i makaukau i ke kaua, pau lakou i ka make ma ka waonahele, ma ke ala a lakou i hele ai mawaho mai o Aigupita.
Dalilin da ya sa ya yi haka shi ne, dukan waɗanda suka fito daga Masar, dukan mazan da suka kai shekarun shiga soja, sun mutu a cikin jeji a hanya bayan sun bar Masar.
5 Ua okipoepoeia no na kanaka a pau i hele mai mawaho; aka, o ka poe i hanau ma ka waonahele, i ka puka ana mai mawaho o Aigupita, aole lakou i okipoepoeia.
Dukan mutanen da suka fito daga Masar an yi musu kaciya, amma duk waɗanda aka haifa a jeji a tafiya daga Masar, ba a yi musu ba.
6 Hookahi kanaha makahiki i auwana ai na mamo a Iseraela ma ka waonahele, a pau i ka make ka lahuikaua, ka poe i hele mai mai Aigupita mai, i hoolohe ole i ka leo o Iehova. Hoohiki no o Iehova ia lakou, aole e hoike mai ia lakou i ka aina ana i hoohiki ai i ko lakou mau makua, e haawi mai no lakou, he aina e kahe ana o ka waiu a me ka meli.
Isra’ilawa sun yi tafiya a jeji shekaru arba’in, har sai da dukan mazan da suka kai shekarun shiga soja da suka bar Masar suka mutu, domin ba su yi wa Ubangiji biyayya ba. Gama Ubangiji ya rantse cewa ba zai bar su su ga ƙasar da ya yi wa iyayensu alkawari da rantsuwa cewa zai ba su ba, ƙasar da zuma da madara suke kwarara, ƙasar da take cike da albarka.
7 A o ka lakou poe keiki, ana i hoopuka mai ai, oia ka Iosua i okipoepoe iho ai; no ka mea, ua okipoepoe ole ia lakou, aole lakou i okipoepoeia ma ke ala,
Sai ya sa yaransu ne suka taso a maimakonsu, su ne waɗanda Yoshuwa ya yi wa kaciya. Sun kasance ba kaciya gama ba a yi musu ba a hanya.
8 A i ka wa i hoopau ai lakou i ke okipoepoe ana i kanaka a pau, alaila, noho iho la lakou ma ko la kou wahi i hoomoana'i, a ola lakou.
Kuma bayan da aka yi wa al’ummar kaciya dukansu, sai suka dakata a nan, sai da suka warke.
9 Olelo mai la o Iehova ia Iosua, I keia la ua olokaa wale aku au, mai o oukou aku, i ka hoino ana o Aigupita. Nolaila ua kapaia ka inoa o ia wahi, o Gilegala, a hiki mai i keia la.
Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Yau na kawar muku da zargin Masar.” Saboda haka ake kiran sunan wurin Gilgal har wa yau.
10 Hoomoana no na mamo a Iseraela ma Gilegala, a malama iho la lakou i ka moliaola, i ka la umikumamaha o ka malama, i ke ahiahi, ma na wahi papu o Ieriko.
Da yamman rana ta goma sha huɗu ga wata, lokacin da suke a Gilgal a filin Yeriko, Isra’ilawa suka yi Bikin Ƙetarewa.
11 I ka la mahope iho o ka moliaola, ai no lakou i ka ai o ka aina, a ia la no pulehu lakou i ka berena hu ole.
A kashegarin Bikin, a wannan rana, sai suka ci daga cikin amfanin ƙasar, burodi marar yisti da hatsin da aka gasa.
12 Ia la iho, mahope o ka lakou ai ana i ka ai o ka aina, oki iho la ka mane, aole mane hou na na mamo a Iseraela. A ai no lakou i ka ai o ka aina ma Kanaana ia makahiki.
Kashegari bayan da suka ci amfanin ƙasar kuwa, Manna ta yanke, mutanen Isra’ila kuma ba su ƙara samunta ba. A wannan shekara suka fara cin amfanin ƙasar Kan’ana.
13 Eia hoi kekahi, i ko Iosua noho ana imua o Ieriko, alawa ae la kona maka iluna, nana aku la, aia hoi! ku mai la kekahi kanaka imua ona, me ka pahikaua i unuhiia ma kona lima. Hele aku la o Iosua io na la, i aku la, Ma o makou nei anei oe, ma ko makou enemi paha?
To, da Yoshuwa ya yi kusa da Yeriko, ya tā da idanunsa ya duba, sai ya ga wani mutum tsaye a gabansa riƙe da takobi, sai Yoshuwa ya je wurinsa ya ce masa, “Kai namu ne ko na abokan gābanmu?”
14 I mai la kela, Aole, ua hele mai nei au i alii koa no ko Iehova puali. Moe iho la ko Iosua alo ma ka honua, hoomana aku la, i aku la ia ia, Heaha ka kuu Haku e olelo mai nei i kau kauwa?
Mutumin ya ce, “Babu ko ɗaya, na dai zo ne a matsayin shugaban rundunar sojojin Ubangiji.” Sai Yoshuwa ya kwanta da fuskarsa har ƙasa, ya girmama shi, ya ce masa, “Ranka yă daɗe, wane saƙo kake da shi domin bawanka?”
15 Olelo mai la ke alii koa o ko Iehova puali ia Iosua, E wehe ae oe i kou mau kamaa, mai kou kapnwai aku, no ka mea, he wahi hoano kau e ku nei. A hana no o Iosua pela.
Shugaban rundunar sojojin Ubangiji ya amsa ya ce, “Ka cire takalmanka, gama wurin da kake tsaye, mai tsarki ne.” Sai Yoshuwa ya cire takalmansa.