< Iona 1 >

1 A HIKI mai ka olelo a Iehova ia Iona, ke keiki a Amitai, i mai la,
Maganar Ubangiji ta zo wa Yunana ɗan Amittai cewa,
2 E ku oe, e hele i Nineva, i kela kulanakauhale nui, e kahea aku ia ia; no ka mea, ua pii mai ko lakou hewa imua o'u.
“Tafi babban birnin nan Ninebe ka yi mata wa’azi, saboda muguntarta ta haura zuwa gabana.”
3 Aka, ku ae la o Iona e holo i Taresisa, mai ke alo aku o Iehova, a iho aku la i Iopa; a loaa ia ia ka moku e holo ana i Taresisa: a haawi aku ia i ka uku, a komo iho la ia iloko ona e holo pu me lakou i Taresisa mai ke alo aku o Iehova.
Amma Yunana ya gudu daga Ubangiji ya nufi Tarshish. Ya gangara zuwa Yaffa, inda ya sami jirgin ruwa mai shirin tashi daga tashar. Bayan ya biya kuɗin tafiya, sai ya shiga jirgi ya kama hanya zuwa Tarshish don yă tsere wa Ubangiji.
4 A hoouna mai o Iehova i ka makani nui ma ke kai, a he ino nui ma ke kai, a aneane nahaha ka moku.
Sai Ubangiji ya aika da babban iska a bisan teku, hadiri ya tsananta ƙwarai har jirgin ya yi barazanar farfashewa.
5 Alaila, makau iho la na hooholo moku, a kahea aku kela kanaka keia kanaka i kona akua, a hoolei ka waiwai ma ka moku iloko o ke kai, e hoomama i ka moku no ia mau mea. A ua iho o Iona ilalo i ka aoao hope o ka moku, a moe iho, a ua pauhia i ka hiamoe.
Dukan matuƙan jirgin suka tsorata, kowannensu kuma ya yi kuka ga allahnsa, suka kuma jefar da kayan jirgi a cikin teku domin su rage nauyin jirgin. Ana cikin haka, ashe, Yunana ya sauka can ƙarƙashin jirgi ya je ya kwanta, yana ta sharar barcinsa.
6 A hele aku ke kahu moku ia ia, a i aku la ia ia, Heaha kau, e ka mea hiamoe? e ala, e hea aku i kou Akua, malia paha e manao mai ke Akua ia kakou i make ole ai kakou.
Sai kyaftin ɗin ya je wajensa ya ce masa, “Don me kake barci? Tashi ka kira bisa ga allahnka! Mai yiwuwa yă ji mu, yă cece mu don kada mu hallaka.”
7 A olelo ae la lakou, kela mea keia mea i kona hoa, Ina kakou e hailona, i ike ai kakou i ka mea nona i hiki mai ai keia ino maluna o kakou. A hailona lakou, a lilo ka hailona no Iona.
Matuƙan jirgin suka ce wa juna, “Ku zo, mu jefa ƙuri’a mu ga wa ke da alhakin wannan masifa.” Sai suka jefa ƙuri’a, ƙuri’ar kuwa ta fāɗa a kan Yunana.
8 Alaila, i aku la lakou ia ia, Ke noi aku nei makou, e hai mai oe ia makou i ka mea nona i hiki mai ai keia ino maluna o kakou? Heaha kau oihana? Mai hea mai oe? Owai kou aina? a no ka lahuikanaka hea oe?
Saboda haka suka tambaye shi suka ce, “Yanzu, gaya mana, dalilin da ya sa wannan masifa ta zo mana? Mene ne aikinka? Daga ina ka fito? Ina ne ƙasarka? Daga wacce kabila ce ka fito?”
9 I mai la oia ia lakou, He Hebera no wau; a ke makau nei au ia Iehova ke Akua o ka lani, nana i hana ke kai, a me ka aina maloo.
Sai ya amsa, “Ni mutumin Ibraniyawa ne, ina kuma bauta wa Ubangiji Allah na sama, wanda ya yi teku da tuddai.”
10 Alaila, makau iho la na kanaka i ka makau nui, a i aku la ia ia, No ke aha la oe i hana mai ai i keia? No ka mea, ua ike na kanaka, ua holo ia mai ke alo aku o Iehova, no ka mea, ua hai mai kela ia lakou.
Sai matuƙan jirgin suka tsorata ƙwarai, suka ce masa, “Wane irin mugun abu ne ka aikata haka?” (Sun gane cewa yana gudu ne daga wurin Ubangiji, domin ya riga ya faɗa musu.)
11 Alaila, i aku la lakou ia ia, Heaha ka makou e hana aku ai ia oe, i malie iho ai ke kai no kakou? no ka mea, ua nui ae ka inoino o ke kai.
Sai tekun ya daɗa rikicewa. Sai suka tambaye shi, “Me za mu yi da kai domin tekun yă daina hauka?”
12 A i mai la kela ia lakou, E lawe oukou ia'u, a e kiola ia'u iloko o ke kai, a e malie iho ke kai ia oukou: no ka mea, ua ike au, no'u nei i hiki mai ai keia ino nui maluna o oukou.
Ya amsa musu ya ce, “Ku ɗauke ni ku jefa a cikin teku, tekun zai kwanta. Na san cewa laifina ne ya jawo wannan babban hadirin da ya auka muku.”
13 A hoe ikaika aku la na kanaka e hoi hou i ka aina; aole lakou e hiki: no ka mea, ua nui ae ka inoino o ke kai ia lakou.
Maimakon mutanen su yi haka, sai suka yi ƙoƙari su tura jirgin ruwan zuwa bakin teku. Amma ba su iya ba, saboda iskar ta sa tekun ya yi ta ƙara hauka.
14 No ia mea, kahea aku la lakou ia Iehova, i aku la, Ke noi aku nei makou ia oe, e Iehova, ke noi aku nei makou, mai lukuia makou no ke ola o keia kanaka, a mai hoopai ia makou i ke koko hala ole: no ka mea, ua hana mai oe, e Iehova, e like me kou makemake.
Sai suka yi kuka ga Ubangiji suka ce, “Ya Ubangiji, in ka yarda kada ka bar mu mu mutu saboda ran mutumin nan. Kada ka yi mana hukuncin masu kisankai, gama kai ne, ya Ubangiji, ka ga ya gamshe ka.”
15 Nolaila, kaikai ae la lakou ia Iona a kiola aku la ia ia iloko o ke kai: e malie iho la ke kai mai kona kupikipikio ana.
Sa’an nan suka ɗauki Yunana suka jefar da shi daga jirgin, sai tekun ya kwanta.
16 Alaila, makau nui loa iho la na kanaka ia Iehova, a kaumaha aku lakou i mohai ia Iehova, a hoohiki i na hoohiki ana.
Ganin haka sai mutanen suka cika da tsoron Ubangiji, suka kuma miƙa wa Ubangiji hadaya, suka yi wa’adi da shi.
17 A ua hoomakaukau o Iehova i ia nui e ale iho ia Iona. A ekolu ao, a ekolu po o Iona ileko o ka opu o ka ia.
Amma Ubangiji ya tanada wani babban kifi da zai haɗiye Yunana, Yunana kuwa ya yi yini uku da dare uku a ciki cikin kifin.

< Iona 1 >