< Ioela 3 >

1 NO ka mea, aia hoi, i kela mau la, a i kela manawa, I ka wa e hoi hou mai ai au i ka pio ana o ka Iuda, a me ko Ierusalema,
“A waɗancan kwanaki da kuma a wancan lokaci, sa’ad da zan maido da arzikin Yahuda da Urushalima,
2 E hoakoakoa hoi au i na lahuikanaka a pau, A e lawe mai la lakou ilalo i ke awawa o Iehosapata, A e hookolokolo au me lakou no kuu poe kanaka, A no kuu hooilina, no ka Iseraela, Ka poe a lakou i hoopuehu aku ai iwaena o na lahuikanaka, A i puunaue hoi i kuu aina.
zan tattara dukan al’ummai in kuma kawo su Kwarin Yehoshafat Can zan yi musu shari’a game da gādona, mutanena Isra’ila, gama sun warwatsar da mutanena a cikin al’ummai sun kuma raba ƙasata.
3 A ua hailona lakou no kuu poe kanaka; Ua haawi lakou i keikikane no ka wahine moe kolohe, A kuai aku i kaikamahine no ka waina, i inu ai lakou.
Sun jefa ƙuri’a a kan mutanena suna kuma sayar da yara maza don karuwanci, sun sayar da’yan matan domin ruwan inabi wanda za su sha.
4 A heaha hoi ka oukou ia'u, e Turo, a me Zidona? A me na palena a pau o Pilisetia? E hoihoi mai anei oukou i ka uku ia'u? Ina e hoihoi mai oukou i ka uku ia'u, Owau no kekahi e hoihoi koke loa aku i ko oukou uku maluna o ko oukou poo.
“Yanzu mene ne damuwarku da ni, ya Taya da Sidon da kuma dukan mazaunan yankunan Filistiya? Kuna ƙoƙari ku sāka mini don abin da na yi ne? In kuna sāka mini ne, to, da gaggawa zan mayar muku da sakayya a kanku.
5 No ka mea, ua lawe aku oukou i kuu kala, a me kuu gula, A ua hali aku oukou i kuu mau mea makamae iloko o ko oukou mau luakini.
Gama kun kwashe azurfata da zinariyata kun kuma washe dukiyata mafi kyau kun kai cikin haikalinku.
6 A o na keiki a Iuda, a me ko Ierusalema ka oukou i kuai aku i ka poe Helene, I hali loihi aku ia lakou mai ko lakou palena aku.
Kun sayar da mutanen Yahuda da na Urushalima ga mutanen Hellenawa, don ku aika da su nesa da ƙasarsu.
7 Aia hoi, e hoala mai au ia lakou mai kahi a oukou i kuai aku ai ia lakou, A e hoihoi aku au i ko oukou uku maluna o ko oukou poo;
“Duba, zan dawo da su daga wuraren da kuka sayar da su, in kuma yi muku abin da kuka yi musu.
8 A e kuai aku au i ka oukou poe kaikamahine, A i ka oukou poe keikikane i ka lima o na keiki a Iuda, A o lakou hoi e kuai aku ia lakou la i na Seba, I ka lahuikanaka mamao aku; No ka mea, oia ka Iehova i olelo mai.
Zan sayar da’ya’yanku maza da mata ga mutanen Yahuda, su kuma za su sayar da su ga mutanen Sabenawa, al’umma da take nesa da ku.” Ubangiji ya faɗa.
9 E hai aku oukou i keia iwaena o na lahuikanaka; E hoomakaukau oukou no ke kaua, E hoala mai i ka poe ikaika, E hookokoke mai na kanaka kaua a pau; E pii mai lakou:
Ku yi shelar wannan ga al’ummai. Ku yi shirin yaƙi! Ku tā da jarumawa! Bari mayaƙa su ja kusa su kai hari.
10 E kui oukou i ko oukou mau oopalau i pahikaua, A i ka oukou mau pahi paipai i mau ihe; A e olelo iho ka mea nawaliwali, Ua ikaika wau.
Ku bubbuge garemaninku su zama takuba da kuma laujenku su zama māsu. Bari raunana su ce, “Ni mai ƙarfi ne!”
11 E akoakoa oukou, e hele mai, e na lahuikanaka a pau, E hoakoakoaia oukou a puni; Ilaila hoi oe, e Iehova, e huiho ilalo i kou poe ikaika.
Ku gaggauta, dukanku al’ummai daga kowane ɓangare, ku tattaru a can. Ka sauko da mayaƙanka, ya Ubangiji!
12 E hoalaia na lahuikanaka, A e pii mai i ke awawa o Iehosapata; No ka mea, malaila wau e noho iho ai, e hooponopono i na lahuikanaka a pau e puni ana.
“Bari a tā da dukan al’ummai; bari su kutsa zuwa Kwarin Yehoshafat gama a can zan zauna in shari’anta dukan al’ummai daga kowane ɓangare.
13 E hookomo oukou i ka pahikakiwi, No ka mea, ua oo ka ai; E hele mai oukou, e iho ilalo; No ka mea, ua piha ke kaomi waina, ua piha a hu iwaho na waihona waina; No ka mea, ua nui ko lakou hewa.
Ku fito da lauje, gama girbi ya nuna. Ku zo, ku tattaka inabin, gama wurin matsewar ruwan inabi ya cika randunan tarawa kuma sun cika har suna zuba, muguntarsu da girma take!”
14 Nui ka poe, he nui ka poe ma ke awawa o ka hoopai ana: No ka mea, ua kokoke ka la o Iehova ma ke awawa o ka hoopai ana:
Dubun dubbai suna a cikin kwarin yanke shawara! Gama ranar Ubangiji ta yi kusa a cikin kwarin yanke shawara.
15 E pouli ka la a me ka mahina, A e hoonalowale na hoku i ko lakou malamalama.
Za a duhunta rana da wata, taurari kuma ba za su ba da haske ba.
16 E uwo mai o Iehova mai Ziona mai, A e hoopuka mai i kona leo mai Ierusalema mai; A e haalulu ka lani a me ka honua: A o Iehova ka puuhonua no kona poe kanaka, A me kahi paa no na mamo a Iseraela.
Ubangiji zai yi ruri daga Sihiyona tsawa kuma daga Urushalima; duniya da sararin sama za su yi rawan jiki. Amma Ubangiji zai zama mafakar mutanensa, mafaka ga mutanensa Isra’ila.
17 Pela e ike ai oukou, owau no o Iehova ko oukou Akua, E noho ana ma Ziona, kuu mauna hoano: A e lilo o Ierusalema i hemolele, Aole e hele hou na malihini mawaena ona.
“Sa’an nan za ku san cewa ni, Ubangiji Allahnku, ina zaune a Sihiyona, dutsena mai tsarki. Urushalima za tă zama mai tsarki; baƙi ba za su ƙara mamaye ta ba.
18 A i kela la e hookulu na mauna i ka waina hou, A e hookahe mai na puu i ka waiu, A e kahe ka wai ma na kahawai a pau o Iuda, A e puapuai mai ka waipuna mai ka hale o Iehova mai, A e kahe aku ka wai ma ke awawa o Sitima.
“A wannan rana duwatsu za su ɗiga da sabon ruwan inabi, tuddai kuma za su malmalo madara; dukan rafuffukan Yahuda za su yi ta gudano da ruwa. Maɓulɓula kuma za tă fito daga gidan Ubangiji haka ma ruwa a kwarin itatuwan ƙirya.
19 A e lilo o Aigupita i neoneo, A o Edoma i waonahele neoneo, no ka hana ino ia o na mamo a Iuda, No ka mea, ua hookahe lakou i ke koko hala ole iloko o ko lakou aina.
Amma Masar za tă zama kango, Edom kuma hamada marar amfani, saboda kama-karyar da aka yi wa mutanen Yahuda, a ƙasar da aka zub da jinin marasa laifi.
20 Aka, e noho mau loa ana o ka Iuda, A o ko Ierusalema ia hanauna aku, ia hanauna aku.
Za a zauna a Yahuda har abada Urushalima kuma daga tsara zuwa tsara.
21 No ka mea, e huikala aku au i ko lakou koko, a'u i huikala ole aku ai: A e noho ana o Iehova ma Ziona.
Alhakin jininsu, wanda ban gafarta ba, zan gafarta.”

< Ioela 3 >