< Ioba 33 >
1 NOLAILA ke noi aku nei au ia oe, e Ioba, e hoolohe mai i ka'u mau olelo, A e haliu mai i ka'u mau huaolelo a pau.
“Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
2 Aia hoi, ano, ke wehe nei au i kuu waha, Ke olelo aku nei kuu elelo ma kuu waha.
Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
3 Ma ka pono o kuu naau ka'u olelo; A e olelo akaka kuu lehelehe i ka naauao.
Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
4 Na ka Uhane o ke Akua owau i hana, Na ka hanu hoi o ka Mea mana owau i hoola.
Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
5 Ina e hiki ia oe ke ekemu mai ia'u, E hooponopono oe imua o'u, e kupaa.
Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
6 Aia hoi, no ke Akua no wau e like me oe; Ua hanaia hoi au mai ka lepo mai.
Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
7 Aia hoi, aole ko'u makau e hooweliweli ia oe, Aole e hookaumahaia ko'u lima maluna ou.
Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
8 He oiaio, ua olelo mai oe maloko o kuu pepeiao, A ua lohe au i ka leo o kau mau olelo;
“Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
9 Ua maemae wau, me ka hala ole, Ua maemae wau, aohe hewa iloko o'u.
‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
10 Aia hoi, ua imi no ia i na mea ku e ia'u, Ua manao mai ia ia'u he enemi nona;
Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
11 Ua hookomo no ia i kuu mau wawae ma ka laau kupee, Ua hoohalua no ia i ko'u mau aoao a pau.
ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
12 Aia hoi, ma keia ua pono ole oe; E olelo aku au ia oe, no ka mea, ua oi ke Akua mamua o ke kanaka.
“Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
13 No ke aha la oe i hakaka pu ai me ia? No ka mea, aole ia i hoike mai i kana mau mea a pau.
Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
14 No ka mea, hookahi ka ke Akua olelo ana mai, A elua hoi, aole nae i manaoia oia.
Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
15 Ma ka moeuhane, ma ka hihio i ka po, I ke kau ana o ka hiamoe nui maluna o kanaka, I ka hiamoe ana maluna o kahi moe;
A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
16 Alaila wehe ae la ia i na pepeiao o kanaka, A hoopaa mai ia i ke ao ana o lakou,
mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
17 I hoololi ai ia i ka ke kanaka hana, A e hookaa i ke kiekie mai ke kanaka aku.
don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
18 Ua hoopakele no ia i kona uhane mai ka luakupapau mai, A i kona ola hoi mai ka make ana i ka pahikaua.
don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
19 Ua hoopaiia oia i ka eha maluna o kona wahi moe, A o ka haukeke o kona mau iwi, ua ikaika ia.
“Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
20 Ua hoopailua kona naau i ka berena, A o kona uhane i ka ai maikai.
yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
21 Ua hoopauia kona io mai ka maka aku, A ua ahuwale mai kona mau iwi i ike ole ia.
Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
22 A ua hookokokeia kona uhane i ka luakupapau, A o kona ola i na mea hoopau.
Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
23 Ina me ia he anela, he hoikeolelo, Hookahi noloko mai o ke tausani, E hoike aku i ke kanaka i kona pono;
Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
24 A aloha mai oia ia ia, a i iho la, E hoopakele ia ia mai ka iho ana i ka lua; Ua loaa ia'u ka uku hoola.
yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
25 E hana hou ia kona io me ia i ka wa kamalii, E hoi hou no ia i na la o kona wa opio:
Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
26 E pule aku no ia i ke Akua, a e oluolu no oia ia ia: A e ike aku ia i kona maka me ka hauoli; A e hoihoi aku no ia no ke kanaka i kona pono.
Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
27 E nana mai no ia i na kanaka, A e olelo iho kekahi, Ua hewa au, A ua hookahuli au i ka pono, aole nae i hooukuia mai au;
Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
28 E hoopakele no ia i kona uhane mai ka hele ana i ka lua, A e ike kona mau maka i ka malamalama.
Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
29 Aia hoi, o keia mau mea a pau i hana pinepine ai ke Akua me ke kanaka,
“Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
30 E hoihoi mai i kona uhane mai ka lua mai, E hoomalamalamaia i ka malamalama o ka poe e ola ana.
Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
31 E haliu mai oe, e Ioba, e hoolohe mai ia'u: E noho malie, a na'u e olelo aku.
“Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
32 Ina he wahi mea, e ekemu mai oe ia'u, E olelo mai, no ka mea ke makemake nei au i kou hoaponoia.
In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
33 A i ole hoi, e hoolohe mai oe ia'u, E noho malie, a e ao aku au ia oe i ka noeau.
Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”