< Isaia 9 >
1 I ka wa i hoowahawahaia'i ka aina o Zebuluna, a me ka aina o Napetali, A mahope iho, hoonani oia i kahi maikai, Ma kela aoao o Ioredane, o Galilaia no na kanaka e.
Duk da haka, babu sauran baƙin ciki ga waɗanda suke shan azaba. Dā ya ƙasƙantar da ƙasar kabilan Zebulun da ƙasar Naftali, amma nan gaba zai girmama Galili na Al’ummai, ta hanyar teku wadda take ta Urdun.
2 O na kanaka i hele ma ka pouli, E ike auanei lakou i ka malamalama nui; O ka poe i noho ma ka aina o ke aka o ka make, E alohi mai auanei ka malamalama maluna o lakou.
Mutanen da suke tafiya cikin duhu sun ga babban haske; a kan waɗanda suke zama a ƙasar inuwar mutuwa haske ya haskaka.
3 Ua hoonui oe i ka lahuikanaka, Ua hoomahuahua oe i ko lakou olioli; Ke olioli nei lakou imua ou, E like me ka olioli ana i ka hooiliili ai ana, E like hoi me ka hauoli ana o ka poe puunauwe i ka waiwai pio.
Ka fadada al’umma ka kuma ƙara farin cikinsu; suna farin ciki a gabanka yadda mutane sukan yi murna a lokacin girbi, kamar yadda mutane sukan yi farin ciki sa’ad da suke raba ganima.
4 No ka mea, o kona auamo kaumaha, O ka laau i hahau i kona kua, A me ke kookoo o ka mea hookaumaha ia ia, Ua haki oe ia mau mea me ia i ka la o Midiana.
Gama kamar yadda yake a kwanakin da aka ci Midiyan da yaƙi, kuka ji tsoro nauyin da ya nawaita musu, sandar da yake a kafaɗunsu, sandar masu zaluncinsu.
5 No ka mea, o na palewawae a pau o ka mea i kahikoia i ka palewawae e wawalo ana, A me na aahu i opeope pu ia me ke koko, E lilo no ia mau mea i mea e puhiia, I wahie hoi no ke ahi.
Kowane takalmin jarumin da aka yi amfani da shi a yaƙi da kuma kowane rigar da ka naɗe cikin jini zai kasance an ƙone shi zai kuma zama abin hura wuta.
6 No ka mea, ua hanauia mai, he keiki no kakou, No kakou i haawiia mai ai, he keikikane, Maluna o kona poohiwi ke aupuni; A e kapaia kona inoa, o Kupaianaha, O Kakaolelo, o Keakuamana, O Kamakuamauloa, o Kealiiokamalu.
Gama a gare mu an haifa mana yaro, a gare mu an ba da ɗa, gwamnati za tă kasance a kafaɗarsa. Za a ce da shi Mashawarci Mai Banmamaki, Allah Maɗaukaki Uban Madawwami, Sarkin Salama.
7 Aole e pau ka mahuahua ana o kona aupuni, a me ka malu; Ma ka nohoalii o Davida ia, A ma kona aupuni no hoi, E hoala hou ia mea, a e hookupaa ia ia, Me ka hooponopono, a me ka maikai, Mai keia wa aku, a i ke ao pau ole. Na ka ikaika o Iehova o na kaua e hana i keia.
Game da girmar gwamnatinsa da salama babu iyaka. Zai gāji sarki Dawuda, yă yi mulki a matsayinsa, zai kafa mulkinsa a kan adalci da gaskiya, tun daga yanzu har zuwa ƙarshen zamani. Ubangiji Maɗaukaki ne ya yi niyyar aikata wannan duka.
8 Ka olelo a ka Haku i hoouna aku ai no Iakoba, A haule hoi ia maluna o ka Iseraela.
Ubangiji ya aika da saƙon gāba da Yaƙub; zai auka wa Isra’ila.
9 E ike auanei na kanaka a pau o Eperaima, A me ka poe noho ma Samaria, Ka poe i olelo me ka hookiekie, a me ka hookano o ka naau,
Dukan mutane za su san shi, Efraim da mazaunan Samariya, waɗanda suke magana da fariya suna kuma ɗaga kai,
10 Ua hiolo na pohaka lepo, A na makou e kukulu, he pohaka i kalaiia; Ua kuaia ilalo na laau sukomorea, A na makou no e kanu i na laau kedera.
“Tubalai sun zube a ƙasa, amma za mu sāke gina su da dutse; an sassare itatuwan ɓaure, amma za mu maya su da al’ul.”
11 Na Iehova no e hoala mai i na enemi o Rezina, e ku e ia ia, E paipai oia i kona poe enemi:
Amma Ubangiji ya ƙarfafa maƙiyan Rezin gāba da su ya kuma ingiza abokan gāba.
12 O na Suria ma ka hikina, a ma ke komohana hoi o na Pilisetia, A e hoopaa no i ka Iseraela me ka waha hamama: Aole nae i huli aka kona huhu no keia mau mea a pau, Ke o mai nei no oia i kona lima i keia manawa.
Arameyawa daga gabas da Filistiyawa daga yamma sun cinye Isra’ila da buɗaɗɗen baki. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
13 Aole nae i hoi hou na kanaka, I ka mea nana lakou i hahau, Aole lakou i imi ia Iehova o na kaua.
Amma mutanen ba su juyo wurin wanda ya buge su ba, balle su nemi Ubangiji Maɗaukaki.
14 Nolaila e oki ai o Iehova, mai ka Iseraela aku, I ke poo, a me ka huelo, I ka lala pama, a me ke naku, ma ka la hookahi.
Saboda haka Ubangiji zai yanke Isra’ila kai da wutsiya, da reshen dabino da iwa a rana guda;
15 O ka lunakahiko a me ka mea koikoi, oia ke poo, O ke kaula i ao mai i ka wahahee, oia ka huelo.
dattawa da manyan mutane su ne kai, annabawa waɗanda suke koyar da ƙarairayi su ne wutsiya.
16 O na alakai o keia poe kanaka, he poe alakai hewa lakou; A o ka poe i alakai hewa ia, e lukuia no lakou.
Waɗanda suke jagorar wannan mutane suna ɓad da su, su ne waɗanda ake jagora aka sa suka kauce.
17 Nolaila, aole olioli ka Haku maluna o ko lakou poe ui. Aole hoi ia e aloha i na keiki makua ole o lakou, A me ko lakou wahinekanemake; No ka mea, ua haumia lakou a pau, a ua hewa, Olelo no na waha a pau ma ka lapawale. Aole nae i hali aku kona huhu no keia maa mea a pau, Aka, ke o mai nei no kona lima i keia manawa.
Saboda haka Ubangiji ba zai ji daɗin matasa ba, ba kuwa zai ji tausayin marayu da gwauraye ba, gama kowa marar sanin Allah ne da kuma mugu, kowane baki yana faɗin mugayen maganganu. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
18 No ka mea, e a ana ka hewa e like me ke ahi, E hoopaa no ia i ka nahele ooi, a me ka laau kalakala, A e a no hoi ia maloko o ka ululaau paapu; A e punohn iluna, he punohu u wahi.
Tabbatacce mugunta tana ƙuna kamar wuta; tana cin ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya, ta sa wuta a jeji mai itatuwa masu yawa, don yă yi murtuke hayaƙi har zuwa sama.
19 Ua hoaia ka aina, no ka ukiuki o Iehova o na kaua, A ua lilo hoi na kanaka i wahie no ke ahi; Aohe kanaka i aloha i kona hoa.
Ta wurin fushin Ubangiji Maɗaukaki ƙasar za tă ci wuta mutane kuma za su zama abin hura wutar, babu wanda zai ji tausayin ɗan’uwansa.
20 E ai no ia ma ka lima akau, a e pololi nae, E ai no hoi ia ma ka lima hema, aole nae e maona; E ai no ke kanaka i ka io o kona lima iho.
A dama za su ci, amma su ci gaba da jin yunwa; a hagu za su ci, amma ba za su ƙoshi ba. Kowa zai mai da naman’ya’yansa abinci.
21 O Manase ia Eperaima, a o Eperaima hoi ia Manase, A e hui no hoi laua e ku e ia Iuda; Aole nae i huli aku kona huhu no keia mau mea a pau, Aka, ke o mai nei no kona lima i keia manawa.
Manasse zai mai da Efraim abinci, Efraim kuma yă cinye Manasse; tare za su yi gāba da Yahuda. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.