< Hosea 12 >
1 KE ai nei ka Eperaima i ka makani, A ke hahai nei hoi ia i ka makani hikina: Hoomahuahua no ia i na la a pau i ka hoopunipuni a me ka luku ana; A hana lakou i ka berita me ko Asuria, A ua laweia'ku ka aila i Aigupita.
Efraim yana kiwo a kan iska; yana fafarar iskar gabas dukan yini yana riɓaɓɓanya ƙarairayi da rikici. Ya yi yarjejjeniya da Assuriya ya kuma aika wa Masar man zaitun.
2 He paio hoi ko Iehova me ka Iuda, A e hoopai aku oia ia Iakoba e like me kona mau aoao; E hoouku aku kela ia ia e like me kana hana.
Ubangiji yana da ƙarar da zai kawo a kan Yahuda; zai hukunta Yaƙub bisa ga hanyoyinsa zai sāka masa bisa ga ayyukansa.
3 Iloko o ka opu hoopaa aku oia i ke kuekuewawae o kona kaikuaana, A ma kona ikaika hakaka pu ia me ke Akua.
A cikin mahaifa ya cafke ɗiɗɗigen ɗan’uwansa; a matsayin mutum ya yi kokawa da Allah.
4 A hakaka pu ia me ka anela, a lanakila: Uwe iho la ia, a nonoi aku la ia ia: Loaa oia ia ia ma Betela, a olelo pu oia me kakou;
Ya yi kokawa da mala’ika ya kuma rinjaye shi; ya yi kuka ya kuma yi roƙo don tagomashi. Ya same shi a Betel ya kuma yi magana da shi a can,
5 Oia hoi, o Iehova ke Akua o na kaua; O Iehova, oia kona inoa ponoi.
Ubangiji Allah Maɗaukaki, Ubangiji ne sunansa sananne!
6 Nolaila, e huli oe i kou Akua: E malama i ke aloha, a me ka olelo hoopono, A e hilinai mau maluna o kou Akua.
Amma dole ku koma ga Allahnku; ku ci gaba da ƙauna da yin gaskiya, ku kuma saurari Allahnku kullum.
7 He kalepa no ia, ma kona lima ka mea kaupaona hoopunipuni: A makemake no ia i ka alunu.
Ɗan kasuwa yana amfani da mudu marar gaskiya; yana jin daɗin cuta.
8 A i iho la o Eperaima, Ua lako no nae wau, Ua loaa ia'u ka waiwai; Ma ka'u mau hana a pau aole i loaa kuu hewa, ka mea i hewa'i au.
Efraim yana fariya yana cewa, “Ni mai arziki ne ƙwarai; na azurta. Da dukan wadatata ba za a sami wani laifi ko zunubi a gare ni ba.”
9 A owau, o Iehova kou Akua, mai ka aina o Aigupita mai, E hoonoho hou aku au ia oe i na halelewa, e like me na la o ka ahaaina.
“Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar; zan sa ku sāke zauna a tentuna, kamar a kwanakin ƙayyadaddun bukukkuwanku.
10 A ua olelo aku au ma na kaula, A ua hoomahuahua i na hihio, A ua olelo aku au i na olelo nane ma ka lima o na kaula.
Na yi magana da annabawa, na ba su wahayi da yawa na kuma ba da misalai ta wurinsu.”
11 Ua hewa anei ko Gileada? Oia, ua hewa lakou; Ke kaumaha nei lakou i na bipi ma Gilegala; A o ko lakou mau kuahu, ua like me na ahu ma na auwaha o ka mahinaai.
Gileyad mugu ne? Mutanensa mutanen banza ne! Suna miƙa bijimai a Gilgal? Bagadansu za su zama tsibin duwatsu. A gonar da aka nome.
12 A holo aku la o Iakoba i ka aina o Suria; A hooluhi aku la o Iseraela no ka wahine, A no ka wahine malama aku la ia i na holoholona.
Yaƙub ya gudu zuwa ƙasar Aram; Isra’ila ya yi bauta don yă sami mata, domin kuma yă biya, sai da ya yi kiwon tumaki.
13 A ma ke kaula i lawe mai ai o Iehova i ka Iseraela mai Aigupita mai, A ma ke kaula i malama mai ai oia ia ia.
Ubangiji ya yi amfani da annabi don yă fitar da Isra’ila daga Masar ta wurin annabi ya lura da shi.
14 Hoonaukiuki loa aku la o Eperaima ia ia; Nolaila e waiho aku ai ia i kona koko maluna ona, A e hoihoi aku kona Haku i kona hoowahawaha maluna ona.
Amma Efraim ya yi muguwar tsokana da ta sa ya yi fushi; shugabansa zai ɗora musu hakkin jini a kansa kuma zai sāka masa saboda wulaƙancinsa.