< Hagai 2 >
1 I KA la iwakaluakumamakahi o ka malama ahiku, hiki mai la ka olelo a Iehova ma o Hagai la ke kaula, i ka i ana mai,
a ranar ashirin da ɗaya ga watan bakwai, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
2 E olelo aku oe ia Zerubabela ke keiki a Saletiela, ke kiaaina o Iuda, a ia Iosua ke keiki a Iosedeka, ke kahuna nui, a i ke koena o kanaka, i ka i ana aku,
“Ka yi magana da Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel wanda yake gwamna a Yahuda, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma dukan raguwar mutane. Ka tambaye su ka ce,
3 Owai o oukou e koe, nana i ike i kela luakini me kona nani mua? pehea oukou i ike ai i keia, ano, aole anei ia ma ko oukou maka me he mea ole la?
‘Wane ne a cikinku ya ragu da ya ga wannan gida a darajarsa ta dā? Yaya yake a gare ku a yanzu? Bai yi kamar a bakin kome ba, ko ba haka ba?
4 Aka, i nui hoi ka ikaika ou, e Zerubabela, wahi a Iehova; i nui hoi ka ikaika ou, e Iosua, e ke keiki a Iosedeka, ke kahuna nui; i nui hoi ka ikaika o oukou, e na kanaka a pau o ka aina nei, a e hana hoi, wahi a Iehova; no ka mea, me oukou pu hoi au, wahi a Iehova o na kaua.
Amma yanzu ka ƙarfafa, ya Zerubbabel,’ in ji Ubangiji. ‘Ka ƙarfafa, ya Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist. Ku ƙarfafa, dukanku mutanen ƙasar,’ in ji Ubangiji, ‘ku yi aiki. Gama ina tare da ku,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
5 E like me ka berita a'u i hoopaa aku ai me oukou, ia oukou i puka ai mai Aigupita mai, pela hoi e noho ai kuu Uhane iwaena o oukou; mai makau oukou.
‘Wannan shi ne alkawarin da na yi da ku a lokacin da kuka fito daga Masar. Ruhuna kuwa yana tare da ku. Kada ku ji tsoro.’
6 No ka mea, penei ka i ana mai a Iehova, ke Akua o na kaua; I kekahi manawa aku, he liuliu iki ia, a e hoonaue au i ka lani a me ka honua, i ke kai a me ka aina maloo;
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ba da jimawa ba zan sāke girgiza sammai da kuma ƙasa, teku da busasshiyar ƙasa.
7 A e hoonaue hoi au i na lahuikanaka a pau, a e hele mai auanei ka mea i makemakeia e na lahuikanaka a pau, a e hoopiha auanei au i keia hale i ka nani, wahi a Iehova o na kaua.
Zan girgiza dukan al’ummai, marmarin kowace al’umma kuma zai taso, sa’an nan zan cika gidan nan da ɗaukaka,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
8 No'u no ke kala, no'u hoi ke gula, wahi a Iehova o na kaua.
‘Da zinariya da azurfa duka nawa ne,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
9 E oi auanei ka nani o keia hale hope imua o ko ka mua, wahi a Iehova o na kaua; a ma keia wahi hoi e haawi aku no wau i ka maluhia, wahi a Iehova o na kaua.
‘Ɗaukakar gidan nan na yanzu za tă fi ɗaukakar gidan nan na dā,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki. ‘A wannan wuri kuma zan ba da salama,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
10 I ka la iwakaluakumamaha o ka iwa o ka malama, i ka lua o ka makahiki o Dariu, hiki mai la ka olelo a Iehova ma o Hagai la ke kaula, i ka i ana mai,
A ranar ashirin da huɗu ga watan tara, a shekara ta biyu ta mulkin Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Haggai cewa,
11 Penei ka Iehova o na kaua e olelo mai nei, E ninau aku oe i na kahuna no ke kanawai, penei,
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku tambayi firist abin da doka ta ce.
12 Ina e lawelawe kekahi i ka io laa ma ke kihi o kona aahu, a hoopa aku kona kihi i ka berena, i ka io hoolapalapa paha, a i ka waina, a i ka aila paha, a i kekahi mea ai e ae, e laa no anei ia? Hoole mai la na kahuna, i mai la, Aole.
Idan mutum yana riƙe da naman da aka keɓe a rigarsa, sa’an nan kuma wannan rigar ta taɓa burodi, ko dafaffen abinci, ko ruwan inabi, ko mai, ko kowane irin abinci, wannan zai sa abin yă zama tsarkake?’” Firistoci suka amsa, suka ce, “A’a.”
13 Alaila i aku la o Hagai, Ina i haumia kekahi i ke kupapau, a hoopa aku ia i kekahi o keia mau mea, e haumia anei ia mea? Pane mai la na kahuna, i mai la, E haumia no.
Sa’an nan Haggai ya ce, “In mutumin da ya ƙazantar da kansa ta wurin taɓa gawa, ya taɓa wani daga cikin waɗannan abubuwa, za su ƙazantu?” Firistoci suka amsa, suka ce, “I, zai ƙazantu.”
14 Olelo aku la o Hagai, i aku la, Pela no keia poe kanaka, a pela keia lahuikanaka imua o'u, wahi a Iehova: a pela hoi ka hana a pau a ko lakou lima; a o ka mea a lakou e mohai mai ai ilaila, he haumia ia.
Sai annabi Haggai ya ce, “‘Haka yake da wannan mutane da kuma wannan al’umma a gabana,’ in ji Ubangiji. ‘Duk abin da suke yi da kuma dukan abin da suke miƙawa ƙazantattu ne.
15 Nolaila hoi, e noonoo pono oukou mai keia la e noho nei a hiki i ka wa mamua, i ka wa i kau ole ia'i ka pohaku maluna o kekahi pohaku ma ka luakini o Iehova.
“‘Yanzu kuwa sai ku yi la’akari da wannan daga wannan rana zuwa gaba, ku tuna yadda al’amura suke kafin a ɗora wani dutse bisa wani a haikalin Ubangiji.
16 Mai ia manawa, ina hele aku kekahi i ka puu hua ai he iwakalua na ana ona, a loaa he umi; a i hele aku hoi kekahi i kahi kaomi waina e hookahe ai i na ana he kanalima mailoko mai o ke kaomi waina, a loaa iho he iwakalua wale no.
A lokacin, idan wani ya tafi wurin tsibin da zai auna mudu ashirin, sai yă iske mudu goma kawai. Idan kuma wani ya tafi wurin matse ruwan inabi don yă ɗebo lita hamsin, sai yă tarar da lita ashirin kawai.
17 Hahau aku la au ia oukou i ka maloo a me ka popo, a me ka huahekili ma na hana a pau a ko oukou mau lima; aka, aole o oukou i huli mai i o'u nei, wahi a Iehova.
Na mai da aikin da kuka sha wahala kuka yi ya zama banza ta wurin saukar da burtuntuna, da fumfuna, da ƙanƙara, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,’ in ji Ubangiji.
18 E noonoo oukou mai keia la e noho nei a mamua aku, mai ka la iwakaluakumamaha o ka malama aiwa, a hiki i kela la i hookumuia'i ka luakini o Iehova; e noonoo oukou.
‘Daga wannan rana zuwa gaba, wato, rana ta ashirin da huɗu ga watan tara, ku lura da ranar da aka kafa harsashin haikalin Ubangiji. Ku lura da kyau.
19 Ua koe anei ka hua ai iloko ka halepapaa? Eia hoi, aole ka waina, a me ka fiku, a me ka pomegerane, a me ka laau oliva i hua mai i ka hua: mai keia la aku nae, e hoomaikai aku no wau ia oukou.
Akwai sauran irin da ya rage a rumbu? Har yanzu, kuringar inabi da itacen ɓaure, rumman da itacen zaitun ba su ba da’ya’ya ba tukuna. “‘Amma daga wannan rana zuwa gaba zan sa muku albarka.’”
20 Hiki hou mai la ka olelo a Iehova ia Hagai i ka la iwakaluakumamaha o ua malama la, i ka i ana mai,
Maganar Ubangiji ta zo wa annabi Haggai sau na biyu a rana ta ashirin da huɗu ga wata cewa,
21 E i aku oe ia Zerubabela ke kiaaina o Iuda, penei, E hoonaue ana au i ka lani a me ka honua;
“Ka faɗa wa Zerubbabel gwamnan Yahuda cewa zan girgiza sammai da ƙasa.
22 A e hookahuli au i ka nohoalii o na aupuni, a e hoolilo au i ka ikaika o na aupuni kanaka e i mea ole; e hookahuli hoi au i na halekaa a me ka poe holo maloko; a e haule iho auanei na lio a me na hoohololio, o kela mea keia mea o lakou, i ka pahikaua a kona hoahanau.
Zan hamɓarar da gadajen mulki in kuma ragargaza ƙarfin ƙasashen al’ummai. Zan tumɓuke kekunan yaƙi da mahayansu; dawakai da mahayansu za su mutu, kowane ta wurin takobin ɗan’uwansu.
23 Ia la hoi, wahi a Iehova o na kaua, e lawe au ia oe, e Zerubabela ke keiki a Saletiela, o ka'u kauwa, wahi a Iehova, a e hoolike au ia oe me ke komolima hoopili wepa; no ka mea, ua koho au ia oe, wahi a Iehova o na kaua.
“‘A wannan rana,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘Zan ɗauke ka, bawana Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel,’ in ji Ubangiji, ‘in kuma maishe ka kamar zoben hatimi, gama na zaɓe ka,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”