< Kinohi 7 >

1 I MAI ia o Iehova ia Noa, E komo ae oe me kau ohana a pau iloko o ka halelana; no ka mea, o oe no o keia hanauna ka'u i ike ai, he pono imua o'u.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Nuhu. “Shiga jirgin, kai da dukan iyalinka, gama na ga kai mai adalci ne a wannan zamani.
2 O na holoholona maemae a pau, e lawe pahiku aku oe ia lakou me oe, i ke Kane a me kana wahine; a o na holoholona maemae ole, e papalua he kane me kana wahine,
Ka ɗauki bakwai na kowace iri tsabtaccen dabba tare da kai, namiji da ta mace, da kuma biyu na kowace dabba marar tsabta, namiji da ta mace,
3 E pahikuia no hoi na manu o ka lewa, ke kane, ka wahine, e hoola i kumuhoolaha maluna o ka honua a pau.
da kuma bakwai na kowane iri tsuntsu, namiji da ta mace, domin a bar kowane irinsu da rai a dukan duniya.
4 No ka mea, ehiku la e koe, alaila e hooua iho ai au maluna o ka honua he kanaha la a me na po; a e luku ana au i na mea ola a pau a'u i hana'i, mai ke alo o ka honua aku.
Kwana bakwai daga yanzu zan aiko da ruwa a duniya yini arba’in da dare arba’in, zan kuma kawar da kowace halitta mai rai da na yi daga doron ƙasa.”
5 Hana iho la o Noa i na mea a pau a Iehova i kauoha mai ai ia ia.
Nuhu ya aikata duk abin da Ubangiji ya umarce shi.
6 Eono haneri na makahiki o Noa i ka wa i hiki mai ai ke kaiakahinalii maluna o ka honua.
Nuhu yana da shekaru 106 ne sa’ad da aka yi ambaliya ruwa a duniya.
7 Komo aku la e Noa me na keikikane ana, a me kana wahine, a me na wahine a kana mau keikikane iloko o ka halelana, no ke kaiakahinalii.
Nuhu da matarsa da’ya’yansa da matansu, suka shiga jirgi domin su tsira daga ruwa ambaliya.
8 O na holoholona maemae a me na holoholona maemae ole, a o na manu, a me na mea kolo a pau maluna o ka honua.
Biyu-biyu daga dabbobi masu tsabta da marasa tsabta, da tsuntsaye da kuma dukan halittu masu rarrafe a ƙasa,
9 Komo papalua aku la lakou iloko io Noa la, ke kane, ka wahine, me ka ke Akua i kauoha mai ai ia Noa.
namiji da ta mace, suka zo wurin Nuhu, suka shiga jirgi, kamar yadda Allah ya umarce Nuhu.
10 A hala ae la na la ehiku, hiki mai ke kaiakahinalii maluna o ka honua.
Bayan kwana bakwai kuwa ambaliya ruwa ta sauko a bisa duniya.
11 I ka makahiki eono haneri o ko Noa ola ana, i ka lua o ka malama, a ma ka la umikumamahiku o ua malama la, ia la no, huahuai mai la na panawai a pau o ka hohonu nui, a hamarna ae la na puka wai o ka lani.
A ranar sha bakwai ga wata na biyu, na shekara ta ɗari shida na rayuwar Nuhu, a ran nan sai dukan maɓuɓɓugai na manyan zurfafa suka fashe, tagogin sammai suka buɗe.
12 Hookahi kanaha la a me na po o ka ua ana maluna o ka honua.
Ruwa yana ta kwararowa bisa duniya, yini arba’in da dare arba’in.
13 Ia la hookahi no, komo ae la o Noa, a o Sema, a o Hama, a o Iapeta, na keikikane a Noa, a me ka wahine a Noa, a me na wahine ekolu a kana mau keikikane me lakou, iloko o ka halelana.
A wannan rana Nuhu tare da matarsa da’ya’yansa maza, Shem, Ham da Yafet da matansu uku suka shiga jirgi.
14 O lakou me na holoholona hihiu a pau ma ko lakou ano iho, a me na holoholona laka a pau ma ko lakou ano iho, a me kela mea kolo keia mea kolo, e kolo ana maluna o ka honua ma kona ano iho, a me na manu a pau ma ko lakou ano iho, o na mea eheu a pau, o kela ano keia ano.
Tare da su kuwa, akwai kowane naman jeji bisa ga irinsa, da dukan dabbobin gida bisa ga irinsu, da kowace halitta mai rarrafe a ƙasa bisa ga irinta, da kowane tsuntsun gida da na jeji bisa ga irinsa, da dukan abu mai fiffike.
15 Komo papalua ae la lakou io Noa la iloko o ka halelana, o na mea io a pau e ha ana i ka hanu ola.
Biyu-biyu na dukan halittu masu numfashi suka zo wurin Nuhu, suka shiga jirgi.
16 He kane he wahine o na mea io a pau ka poe i komo aku iloko, mo ka ke Akua i kauoha mai ai ia ia: a papani ae la o Iehova i ka puka mahope ona.
Dabbobi da kowane abu mai rai da suka shiga ciki, namiji ne da ta mace, yadda Allah ya umarci Nuhu. Sa’an nan Ubangiji ya kulle jirgin daga baya.
17 Hookahi kanaha la o ke kaiakahinalii maluna o ka honua; mahuahua ae la ka wai, a hoolana ae la i ka halelana, a ua kaikaiia ae la ia maluna o ka honua.
Kwana arba’in ambaliya ta yi ta saukowa a duniya, sa’ad da ruwa ya yi ta ƙaruwa sai ya yi ta ɗaga jirgin sama, ya kuwa tashi can bisa duniya.
18 Lanakila ae la ka wai a mahuahua loa ae la maluna o ka honua; a holo aku la ka halelana maluna o ka wai.
Ruwa ya taso, ya ƙaru ƙwarai a duniya, jirgin kuma ya yi ta yawo a bisa ruwa.
19 Lanakila loa ae la ka wai maluna o ka honua; a uhiia ae la na kuahiwi kiekie a pau loa malalo o ka lani.
Ruwa ya ƙaru ƙwarai a duniya, ya kuma rufe dukan duwatsu masu tsawo a ƙarƙashin sammai.
20 He umikumamalima na kubita o ke kiekie o ka wai maluna; a uhiia ae la na kuahiwi.
Ruwan ya taso ya rufe duwatsu, zurfin ruwa daga duwatsun zuwa inda jirgin yake ya fi ƙafa ashirin.
21 A make iho la na mea ola a pau i holo maluna o ka honua, o na manu, o na holoholona laka, o na holoholona hihiu, a o na mea kolo a pau e kolo ana maluna o ka honua, a me na kanaka a pau;
Kowane abu mai rai da yake tafiya a duniya ya hallaka, tsuntsaye, dabbobin gida, namun jeji, da dukan masu rarrafe waɗanda suke rarrafe a duniya, da kuma dukan mutane.
22 O ka poe a pau nona ka hanu ola iloko o na puka ihu, o na mea a pau ma ka aina maloo, make iho la lakou.
Kome a busasshiyar ƙasa da yake numfashi a hancinsa ya mutu.
23 A pau loa iho la na mea ola maluna o ka honua i ka make, o na kanaka, me na holoholona, a me na mea kolo, a me na manu o ka lewa; a ua hoopauia lakou mai ka honua aku: o Noa wale no ka i koe, a me ka poe me ia iloko o ka halelana.
Aka kawar da kowane abu mai rai, mutane da dabbobi da halittu masu rarrafe a ƙasa, da tsuntsayen sama a doron ƙasa, duka aka kawar da su daga duniya. Nuhu kaɗai aka bari da waɗanda suke tare da shi a cikin jirgi.
24 A lanakila ae la ka wai maluna o ka honua, hookahi haneri na la a me kanalima.
Ruwa ya mamaye duniya har kwana ɗari da hamsin.

< Kinohi 7 >

The Great Flood
The Great Flood