< Kinohi 25 >

1 LAWE hou ae la o Aberahama i wahine nana, o Ketura kona inoa.
Ibrahim ya auro wata mace, mai suna Ketura.
2 O na keiki ana i hanau ai nana, o Zimerama, o Iokesana, o Medana, o Midiana, o Isebaka a o Sua.
Ta haifa masa Zimran, Yokshan, Medan, Midiyan, Ishbak da Shuwa.
3 Na Iokesana o Seba, a o Dedana. Eia ka poe mamo a Dedana, o ka Asurima, Ka Letusima, a me ka Leumima.
Yokshan shi ne mahaifin Sheba da Dedan. Zuriyar Dedan su ne mutanen Ashur, da mutanen Letush, da kuma mutanen Lewummin.
4 O na keiki a Midiana; o Epa, o Epera, o Hanoka, o Abida, a o Eledaa. O keia poe a pau na Ketura mai.
’Ya’yan Midiyan maza su ne, Efa, Efer, Hanok, Abida, da kuma Elda’a. Dukan waɗannan zuriyar Ketura ce.
5 Kauoha mai la o Aberahama i kona waiwai a pau ia Isaaka.
Ibrahim ya bar wa Ishaku kome da ya mallaka.
6 Aka, haawi aku la o Aberahama i na makana na na keikikane a na haiawahine a Aberahama, a hookuu aku la ia lakou, i kona wa e ola ana, mai kana keiki o Isaaka aku, e hele i ka aina o ka hikina.
Amma yayinda Ibrahim yake da rai, ya ba wa’ya’yan ƙwarƙwaransa maza kyautai, ya kuma sallame su daga ɗansa Ishaku zuwa ƙasashen gabas.
7 Eia na la o na makahiki o ko Aberahama ola ana, hookahi haneri a me kanahikukumamalima.
Duka-duka, Ibrahim ya yi shekara ɗari da saba’in da biyar.
8 Alaila kaliia'ku ke ea o Aberahama, a make iho la ia i ka wa elemakule maikai; he kanaka kahiko loa ia, a ua nui na la ona, a ua huiia'ku ia me kona poe kanaka.
Sa’an nan Ibrahim ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuma mutu da kyakkyawar tsufa, tsoho da kuma shekaru masu yawa; aka kuma tara shi ga mutanensa.
9 Na kana mau keiki na Isaaka laua o Isemaela i kanu aku ia ia maloko o ke ana o Makepela, ma ka mahinaai a Eperona ke keiki a Zohara no ka Heta, ma ke alo o Mamere,
’Ya’yansa maza kuwa Ishaku da Ishmayel suka binne shi cikin kogon Makfela, kusa da Mamre, a cikin filin Efron ɗan Zohar mutumin Hitti,
10 Ma ka mahinaai a Aberahama i kuai ai me na mamo a Heta: ilaila i kanuia'i o Aberahama, a me Sara o kana wahine.
filin da Ibrahim ya saya daga Hittiyawa. A nan aka binne Ibrahim tare da matarsa Saratu.
11 Mahope mai o ka make ana o Aberahama, hoopomaikai mai la ke Akua ia Isaaka; a noho iho la o Isaaka ma ka luawai o Lahairoi.
Bayan rasuwar Ibrahim, Allah ya albarkaci ɗansa Ishaku wanda a lokacin yana zama kusa da Beyer-Lahai-Royi.
12 Eia ka mooolelo no Isemaela, no ke keikikane a Aberahama, o ka mea a Hagara no Aigupita ke kauwawahine a Sara i hanau ai na Aberahama:
Waɗannan su ne zuriyar Ishmayel ɗan Ibrahim, wanda Hagar mutuniyar Masar, baranyar Saratu, ta haifa wa Ibrahim.
13 Eia hoi na inoa o na keikikane a Isemaela, ma ko lakou mau inoa, e like me ko lakou hanau ana: o Nebaiota kana hiapo; o Kedara, o Adebeela, o Mibesama,
Ga jerin sunayen’ya’yan Ishmayel maza bisa ga haihuwarsu, Nebayiwot ɗan farin Ishmayel, Kedar, Adbeyel, Mibsam,
14 O Misama, o Duma, o Masa.
Mishma, Duma, Massa,
15 Hadara, o Tema, o Ietura, o Napisa, a o Kedema.
Hadad, Tema, Yetur, Nafish da Kedema.
16 Oia na keikikane a Isemaela, oia hoi ko lakou mau inoa; ma ko lakou mau kauhale, a ma ko lakou mau kulanahale; he umikumamalua mau alii e like me ko lakou mau lahuikanaka.
Waɗannan su ne’ya’yan Ishmayel maza, waɗanda kuma suke sunayen kabilu goma sha biyu masu mulki bisa ga wuraren zamansu da sansaninsu.
17 Eia na makahiki o ke ola ana o Isemaela, hookahi haneri na makahiki me kanakolukumamahiku: ua kailiia'ku kona ea, a make iho la ia; a ua huiia aku ia me kona poe kanaka.
Duka-duka Ishmayel ya yi shekara ɗari da talatin da bakwai; sai ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuma mutu, aka kuma tara shi ga mutanensa.
18 Noho iho la lakou mai Havila a hiki i Sura, ma ke alo o Aigupita, i kou hele ana i Asuria; pela oia I noho ai ma ke alo o kona poe hoahanau a pau.
Zuriyarsa sun zauna tsakanin Hawila ne da Shur, wanda yake kusa da gabashin iyakar Masar wajen Asshur. Sun yi zaman rikici da dukan sauran’yan’uwansu.
19 Eia ka mooolelo no Isaaka no ke keiki a Aberahama: Na Aberahama o Isaaka:
Waɗannan su ne zuriyar Ishaku ɗan Ibrahim. Ibrahim ya haifi Ishaku,
20 He kanaha na makahiki o Isaaka i kona wa i lawe ai ia Rebeka ke kaikamahine a Betuela no Suria, a ke kaikuwahine o Labana no Suria, i wahine nana.
Ishaku yana da shekara arba’in sa’ad da ya auri Rebeka’yar Betuwel, mutumin Aram, daga Faddan Aram,’yar’uwar Laban mutumin Aram.
21 Nonoi aku la o Isaaka ia Iehova no kana wahine, no ka mea, ua pa oia: a hoolohe mai la ke Akua ia ia, a hapai ae la kana wahine o Rebeka.
Ishaku ya yi addu’a ga Ubangiji a madadin matarsa, saboda ba ta haihuwa. Ubangiji ya amsa addu’arsa, matarsa Rebeka kuwa ta yi ciki.
22 Oni pu ae la na keiki iloko ona; i iho la ia, A i pela ia, i aha keia mea a'u? A hele aku la ia e ninau ia Iehova.
Jariran suka kama kokawa da juna a cikinta, sai ta ce, “Me ya sa wannan yake faruwa da ni?” Saboda haka ta tafi don ta nemi nufin Ubangiji.
23 I mai la o Iehova ia ia, Elua no lahuikanaka iloko o kou opu, elua hoi poe kanaka e puka mai ana noloko mai o kou opu, a e oi aku ka ikaika o kekahi poe i ko kekahi poe; a e hookauwa aku ka hanau mua i ka hanau hope.
Ubangiji ya ce mata, “Al’ummai biyu suna a cikin mahaifarki mutum biyu da za ki haifa, za su rabu da juna, ɗayan zai fi ɗayan ƙarfi, babban kuma zai bauta wa ƙaramin.”
24 A hiki mai kona manawa e hanau ai, aia hoi, he mau mahoe iloko o kona opu.
Da lokaci ya yi da za tă haihu, sai ga’yan biyu maza a mahaifarta.
25 A puka mai la ka mua, ua huluhulu, a ulaula, e like me ka aahu huluhulu, a kapa iho la lakou i kona inoa, o Esau.
Wanda ya fara fita ja ne, dukan jikinsa kuwa kamar riga mai gashi. Don haka aka sa masa suna Isuwa.
26 Mahope iho, puka mai la kona kaikaina, a paa aku la kona lima i ke kuekue wawae o Esau; a kapaia kona inoa, o Iakoba. He kanaono na makahiki o Isaaka i ko Rebeka manawa i hanau ai laua.
Bayan wannan, ɗan’uwansa ya fito, da hannunsa yana riƙe da ɗiɗɗigen Isuwa; don haka aka sa masa suna Yaƙub. Ishaku yana da shekara sittin, lokacin da Rebeka ta haife su.
27 Nui ae la ua mau keiki la: he kanaka akamai o Esau i ka hahai holoholona hihiu, he kanaka no ka nahelehele: aka, he kanaka noho malie o Iakoba, e noho ana ma na halelewa.
Yaran suka yi girma, Isuwa kuwa ya zama riƙaƙƙen maharbi, mutumin jeji, yayinda Yaƙub, shiru-shiru ne mai son zama a tentuna.
28 Aloha aku la o Isaaka ia Esau, no ka mea, ai iho la ia i ka io o ua mea hihiu: a o Rebeka ka i aloha ia Iakoba.
Ishaku, mai son ci naman jeji, ya ƙaunaci Isuwa, amma Rebeka ta ƙaunaci Yaƙub.
29 Hoolapalapa iho la o Iakoba i ka mea ai: a hoi mai la o Esau mai ka nahelehele mai, a ua nawaliwali ia.
Wata rana sa’ad da Yaƙub yana dafa fate. Isuwa ya shigo daga jeji, da yunwa sosai.
30 I mai la o Esau ia Iakoba, Ke noi aku nei au ia oe, e ho mai na'u e ai ia mea ulaula; no ka mea, ua nawaliwali au: nolaila ua kapaia kona inoa o Edoma.
Ya ce wa Yaƙub, “Ina roƙonka, ka ɗan ɗiba mini faten nan! Ina fama da yunwa!” (Shi ya sa aka kira shi Edom.)
31 I aku la o Iakoba, E kuai kaua i keia la, i lilo mai ia'u kau pono o ka hanau mua.
Yaƙub ya amsa ya ce, “Ka fara sayar mini da matsayinka na ɗan fari tukuna.”
32 I iho la o Esau, Eia wau ua kokoke e make, a heaha auanei ko'u pomaikai i keia pono o ka hanau mua?
Isuwa ya ce, “Duba, ina gab da mutuwa, me matsayina na ɗan fari zai yi mini?”
33 I aku la o Iakoba E hoohiki oe na'u i keia la; a hoohiki aku la ia nana: a kuai lilo mai la ia i kana pono o ka hanau mua, na Iakoba.
Amma Yaƙub ya ce, “Ka rantse mini tukuna.” Don haka ya rantse masa, ya sayar da matsayinsa na ɗan fari ga Yaƙub.
34 Alaila, haawi aku la o Iakoba na Esau i ka berena a me na papapa i hoolapalapaia; ai iho la ia a inu hoi, ku ae la ia a hele aku la i kona wahi i hele ai: pela o Esau i hoowahawaha'i i kana pono o ka hanau mua.
Sa’an nan Yaƙub ya ba wa Isuwa burodi da ɗan miyan lansir. Ya ci, ya sha, sa’an nan ya tashi ya tafi. Ta haka Isuwa ya yi banza da matsayinsa na ɗan fari.

< Kinohi 25 >