< Ezekiela 38 >
1 HIKI mai la ka olelo a Iehova ia'u, i mai la,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 E ke keiki a ke kanaka, e hooku e oe i kou maka ia Goga, i ka aina o Magoga, i ka moi nui o Meseka a me Tubala, a e wanana ku e ia ia.
“Ɗan mutum, ka fuskanci Gog, na ƙasar Magog, babban sarkin Meshek da Tubal; ka yi annabci a kansa
3 A e olelo aku, Ke i mai nei Iehova ka Haku, penei; Ke ku e nei au ia oe, e Goga, ka moi nui o Meseka a me Tubala:
ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
4 A e hoohuli au ia oe ihope a hookomo au i na kilou iloko o kou mau a, a e lawe mai au ia oe mawaho, a me kou poe kaua a pau, na lio, na hoohololio, e aahu ana i kela mea keia mea, he lehulehu nui hoi me na paleumauma, a me na palekaua, e lawelawe ana lakou a pau i ka pahikaua:
Zan juyar da kai, in sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka in fitar da kai tare da dukan sojojinka, dawakanka, mahayan dawakanka saye da makamai, da kuma jama’a mai girma masu riƙe da garkuwoyi manya da ƙanana, dukansu da takuba a zāre.
5 Na Peresia, na Aitiopa, a me na Libua me lakou, ia lakou a pau ka palekaua a me ka mahiole:
Farisa, Kush da Fut za su kasance tare da su, duka riƙe da garkuwoyi da hulunan kwano,
6 O Gomera a me kona mau poe a pau; ka ohana a Togarema, a no na wahi kukulu akau, a me kona mau poe a pau; a me na kanaka he nui no me oe.
haka ma Gomer da dukan sojojinsa, da Bet Togarma daga can arewa tare da dukan sojojinsa, al’ummai masu yawa tare da kai.
7 E makaukau oe, a e hoomakaukau iho ia oe iho, o oe, a me kou poe a pau i akoakoa iou la, a e lilo oe i mea kiai no lakou.
“‘Ka shirya; ka kintsa, kai da dukan jama’arka da suka taru kewaye da kai, ka kuma zama mai ba su umarni.
8 A hala na la he nui no, e hoonohoia oe iluna: a i na makahiki hope, e komo oe i ka aina i hoihoiia mai mai ka pahikaua mai, i houluuluia mai waena mai o na lahuikanaka i ku e i na mauna o ka Iseraela i neoneo mau; aka, ua laweia mai mai ko na aina mai, a e noho maluhia lakou a pau.
Bayan kwanaki masu yawa za a kira ka. A shekaru masu zuwa za ka kai hari a ƙasar da ta farfaɗo daga yaƙi, wadda aka tattara mutanenta daga al’ummai masu yawa zuwa duwatsun Isra’ila, dā kango ne sosai. An fitar da su daga al’ummai, yanzu kuwa dukansu suna zama lafiya.
9 E pii ae no oe a e hele mai e like me ka ino, a e like auanei oe me ke ao e uhi mai i ka aina, o oe, a me kou mau poe a pau, a me na kanaka he nui no me oe.
Kai da dukan sojojinka da kuma al’ummai masu yawa da suke tare da kai za ku haura, kuna cin gaba kamar hadari; za ku zama kamar girgijen da yake rufewa ƙasa.
10 Ke i mai nei Iehova ka Haku, penei; Ia la no e hiki no, a e kupu kekahi mau mea maloko o kou naau, a e noonoo no oe i ka manao ino.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar, tunani zai shiga cikin zuciyarka za ka kuma ƙirƙiro muguwar dabara.
11 A e olelo oe, E pii aku au i ka aina kauhale paa ole i ka paia, e hele au i ka poe e noho maluhia ana, e noho ana lakou a pau me na pa ole, aole o lakou kaola pa, aole o lakou pukapa;
Za ka ce, “Zan kai hari wa ƙasar da ƙauyukanta ba su da katanga; zan fāɗa wa mutanen da suke zamansu kurum cikin salama, dukansu suna zama babu katanga babu ƙofofi ko ƙyamare.
12 E lalau i ka waiwai pio, a e lawe hoi i ka waiwai kaili, a e hoohuli i kou lima ma na wahi neoneo, i noho hou ia, a maluna o na kanaka i houluuluia mai mai loko mai o na lahuikanaka, ua loaa ia lakou na holoholona a me na ukana, a e noho ana no mawaenakonu o ka aina.
Zan washe in kwashe ganima in kuma juye hannuna gāba da kufai da aka sāke zaunar da mutanen da aka tattara daga al’ummai, masu yawan shanu da kayayyaki, masu zama a tsakiyar ƙasa.”
13 O Seba a me Dedana, a me ka poe kalepa o Taresisa, a me kolaila poe liona opiopio a pau, ke olelo aku ia oe, Ua hele mai anei oe e lalau i ka waiwai pio? Ua houluulu anei oe i kou anaina e lawe i ka waiwai kaili? E lawe aku hoi i ke kala a me ke gula, e lawe aku hoi i na holoholona a me na ukana, a e lawe aku hoi i ka waiwai pio nui?
Sheba da Dedan da’yan kasuwar Tarshish da dukan ƙauyukanta za su ce maka, “Ka zo ka kwashe ganima ne? Ka tattara jama’arka don ka yi waso, ka kuma kwashe azurfa da zinariya, ka kwashe shanu da kayayyaki ka kuma ƙwace ganima mai yawa?”’
14 Nolaila, e wanana oe, e ke keiki a ke kanaka, a e olelo aku ia Goga, Ke i mai nei Iehova ka Haku. penei; Aole anei i ka la e noho maluhia ai kuu poe kanaka o ka Iseraela, e ike oe ia?
“Saboda haka ɗan mutum, ka yi annabci ka ce wa Gog, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar, sa’ad da mutanena Isra’ila suna zaman lafiya, ba za ka sani ba?
15 A e hele mai oe mai kou wahi mai, mai loko mai o na wahi kukulu akau, o oe a me na kanaka he nui me oe, e holo ana lakou a pau maluna o na lio, he lehulehu loa, he poe koa ikaika.
Za ka zo daga wurinka a can arewa, kai da al’ummai masu yawa tare da kai, dukansu suna hawan dawakai, jama’a mai yawa, babbar runduna.
16 A e pii ku e mai oe i kuu poe kanaka Iseraela, e like me ke ao e uhi mai ka aina; a e hiki no ia i na la mahope, a e lawe mai au ia oe e ku e i kuu aina, i ike mai na lahuikanaka ia'u i ko'u wa e hoanoia'i ma ou la, e Goga, imua o ko lakou mau maka.
Za ka ci gaba a kan mutanena Isra’ila kamar yadda girgijen yakan rufe ƙasa. A kwanaki masu zuwa, ya Gog, zan kawo ka, ka yi yaƙi da ƙasata, domin al’ummai su san ni sa’ad da na nuna kaina mai tsarki ta wurinka a gabansu.
17 Ke i mai nei Iehova ka Haku, penei; O oe anei ka mea nona wau i olelo ai i ka wa kahiko, ma kuu mau kauwa na kaula o ka Iseraela, na mea i wanana i na makahiki ia manawa e lawe au ia oe e ku e ia lakou?
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ba kai ba ne na yi magana da kai a kwanakin dā ta wurin bayina annabawan Isra’ila? A lokacin sun yi annabci shekaru masu yawa cewa zan kawo ka, ka yaƙe su.
18 A e hiki no keia ia mau la, i ka wa e hele mai ai o Goga e ku e i ka aina o ka Iseraela, wahi a Iehova ka Haku, e pii mai no kuu ukiuki i kuu maka.
Ga abin da zai faru a ranar. Sa’ad da Gog ya fāɗa wa ƙasar Isra’ila, fushina mai zafi zai ƙuna, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
19 No ka mea, i ko'u lili ana a me ke ahi o kuu huhu i olelo aku ai au, Oiaio, ia la e nui auanei ka haalulu ana ma ka aina o ka Iseraela:
Cikin kishina da hasalata mai zafi zan furta cewa a wannan lokaci za a yi babbar girgizar ƙasa a ƙasar Isra’ila.
20 E haalulu hoi ma kou alo na ia o ke kai, na manu hoi o ka lewa, na holoholona hoi o ke kula, a me na mea kolo a pau e kolo ana ma ka lepo, a me na kanaka a pau e noho ana maluna o ka honua, a e hoohioloia na mauna ilalo, a e hiolo no na alapii, a e hiolo no na pa a pau ilalo i ka lepo.
Kifin teku, tsuntsayen sarari, namun jeji, kowace halitta mai rarrafe da kuma dukan mutane a duniya za su yi rawar jiki a gabana. Za a tumɓuke duwatsu, a ragargaza tsaunuka, kuma kowane bango zai fāɗi ƙasa.
21 A e kahea au i pahikaua ku e ia ia maluna o kuu mau mauna a pau, wahi a Iehova ka Haku; e ku e ka pahikaua a kela kanaka keia kanaka i kona hoahanau iho,
Zan kira takobi a kan Gog a dukan duwatsuna, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Kowane takobin mutum zai yi gāba da ɗan’uwansa.
22 A e hakaka au me ia me ka mai ahulau, a me ke koko; a e hooua au i ka ua kahe nui, a me na huahekili nui, a me ke ahi, a me ka luaipele maluna ona, a me kona mau poe a pau, a me na kanaka he nui, ka poe me ia.
Zan yi hukunci a kansa da annoba da kuma zub da jini; zan yi ruwa mai yawa da ƙanƙara da kibiritu mai cin wuta a kansa da a kan sojojinsa da kuma a kan al’ummai masu yawa da suke tare da shi.
23 Pela e hoonui ai au ia'u iho, a e hoano iho ai ia'u iho; a e ikeia mai au e na lahuikanaka he nui; a e ike lakou owau no Iehova.
Ta haka zan nuna girmana da kuma tsarkina, zan sanar da kaina a gaban al’ummai masu yawa. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.’