< Pukaana 21 >
1 EIA na olelo kupaa au e kau ai imua o lakou.
“Waɗannan su ne dokokin da za ka sa a gabansu.
2 Ina kuai oe nau i kauwa Hebera, e hookauwa mai no oia i eono makahiki; a i ka hiku hoi, o kuu wale ia'ku no oia.
“In ka sayi mutumin Ibraniyawa a matsayin bawa, zai bauta maka shekara shida. Amma a shekara ta bakwai, za ka’yantar da shi, yă tafi’yantacce, ba tare da ya biya kome ba.
3 Ina i komo mai oia iloko, o kona kino wale no, alaila, e hele aku no oia iwaho, o kona kino wale no: aka, ina i mareia oia, alaila e hele pu aku no kana wahine me ia.
In ya zo shi kaɗai, zai tafi’yantacce shi kaɗai; amma in yana da mata a lokacin da ya zo, za tă tafi tare da shi.
4 Ina ua haawi mai kona haku i wahine nana, a ua hanau mai oia i mau keikikane nana, a i mau kaikamahine paha, alaila no ka haku ka wahine a me kana mau keiki. a e hele aku no ke kane, oia wale no.
In maigidansa ya yi masa aure, ta kuwa haifa masa’ya’ya maza ko mata, matan da’ya’yan, za su zama na maigidan, sai mutumin kaɗai zai tafi’yantacce.
5 Aka, ina olelo ikaika mai ke kauwa, Ua aloha au i kuu haku, a me kuu wahine, a me ka'u mau ken ki, aole au e hele kuu wale ia;
“Amma in bawan ya furta ya ce, ‘Ina ƙaunar maigidana, da matata, da’ya’yana, ba na so kuma in’yantu,’
6 Alaila, e lawe mai kona haku ia ia i na lunakanawai; a lawe mai no hoi ia ia i ka puka, a i ka lapauwila o ka puka paha; a e hou iho koua haku i kona pepeiao i ke kui, a e hookauwa mau loa mai oia nana.
dole maigidansa yă kai shi gaban alƙalai. Zai kai shi ƙofa ko madogarar ƙofa, yă huda kunnensa da basilla, sa’an nan zai zama bawansa duk tsawon kwanakinsa a duniya.
7 Ina e kuai lilo aku ke kanaka i kana kaikamahine i kauwawahine, aole ia e hookuuia aku e like me ke kuuia'na o na kauwakane.
“In mutum ya sayar da’yarsa a matsayin baiwa, ba za a’yantar da ita kamar bawa ba.
8 Ina i hewa oia i na maka o kona haku, ka mea i hoopalau mai ia ia nana, alaila, o hoolapanai oia ia ia. Aole ia e hiki ke kuai aku ia ia i ko ka aina e, no kana hana ino ana ia ia.
In ba tă gamshi maigida wanda ya zaɓe ta domin kansa ba, dole yă bari a fanshe ta. Ba shi da dama yă sayar da ita ga baƙi, tun da yake bai kyauta mata ba.
9 A ina ua hoopalau oia ia ia na kana keikikane, e hana aku no oia ia ia e like me ka hana ana i na kaikamahine.
In ya zaɓe ta domin ɗansa, dole yă ba ta duk damar da’ya ta mace take da shi.
10 A ina i lawe oia i wahine hou nana, mai hoemi ia i ka ai a me ka aahu, a me ka launa mare o kela wahine.
In ya auri wata mace, ba zai hana wa baiwar abinci da sutura ba, ba kuma zai ƙi kwana da ita ba.
11 A i ole ia e hana aku i keia mau mea ekolu ia ia, alaila, e hookuu wale ia aku oia, me ka uku ole ia mai i ke kala.
In bai tanada mata waɗannan abubuwa uku ba, sai tă tafi’yantacciya, babu biyan kome.
12 O ka mea pepehi i kanaka, a make ia, e oiaio no e pepehiia oia.
“Duk wanda ya bugi mutum har ya kashe shi, lalle a kashe shi.
13 Ina hoohalua ole ke kanaka, a na ke Akua i haawi mai ia ia iloko o kona lima, alaila, na'u no e kuhikuhi aku ia oe i kahi nona e pee aku ai.
Amma in ba da nufin yă kashe shi ba, sai dai in Allah ne ya nufa haka, to, sai mutumin yă tsere zuwa inda zan nuna muku.
14 Aka, ina i hana hookiekie ke kanaka i kona hoalauna, e pepehi maalea ia ia, e lawe no oe ia ia mai ko'u kuahu aku, i make ia.
Amma in mutumin ya yi dabara har ya kashe wani mutum da gangan, sai a ɗauke shi daga bagadena a kashe shi.
15 O ka mea hahau i kona makuakane, a i kona makuwahine, e oiaio no, e make ia.
“Duk wanda ya bugi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, dole a kashe shi.
16 O ka mea aihne i ke kanaka, a kuai lilo aku ia ia, a ina i loaa oia ma kona lima, e oiaio no, e make ia.
“Duk wanda ya saci mutum ya sayar da shi, ko kuwa aka iske shi a hannunsa, lalle kashe shi za a yi.
17 A o ka mea hailiili i kona makuakane, a me kona makuwahine, he oiaio no, e make ia.
“Duk wanda ya la’anta mahaifinsa ko mahaifiyarsa, dole a kashe shi.
18 A ina hakaka na kanaka, a pehi aku kekahi i kona hoa i ka pohaku, a kui aku i ka lima, aole hoi ia i make, na moe nae ma kahi moe;
“Idan mutane suka yi faɗa, ɗayan ya jefa ɗayan da dutse, ko ya naushe shi amma bai mutu ba, sai dai ya yi ta jiyya,
19 Ina ala hou oia a hele iwaho ma kona kookoo, alaila, e pakele no ka mea nana ia i pepehi; aka, e uku no oia, no kona booki ana i kana hana, a nana no hoi e hoola loa aku ia ia.
idan mutumin ya sāke tashi ya yi tafiya ko da yana dogarawa da sanda ne, wanda ya buge shi zai kuɓuta, sai dai zai biya diyyar lokacin da ya ɓata masa, yă kuma lura da shi, har yă warke sarai.
20 A ina e hahau ke kanaka i kana kauwakane, a i kana kauwawahine, i ka laau, a make ia malalo iho o kona lima, e oiaio no, e hoopaiia oia.
“In mutum ya dūke bawansa ko baiwarsa da sanda, sai bawan ko baiwar ta mutu saboda dūkan, dole a hukunta shi,
21 Aka, ina e ola oia i hookahi la paha, a i elua paha, alaila, aole ia e hooukuia: no ka mea, oia kana kala.
amma ba za a hukunta shi ba, in bawan ko baiwar ta tashi, bayan kwana ɗaya ko biyu, tun da bawan ko baiwar mallakarsa ne.
22 Ina hakaka na kanaka, a hooeha i ka wahine hapai keiki, a hemo aku la kana keiki, aole hoi he hewa mahope; e oiaio no e hooukuia oia e like me ka mea e kauia maluna ona e ke kane a ka wahine; a e haawi no oia imua o na lunakanawai.
“Idan mutum biyu suna faɗa, har suka yi wa mace mai ciki rauni, har ya sa ta yi ɓari, amma wani lahani bai same ta ba, za a ci wa wanda ya yi mata raunin tara bisa ga yadda mijinta ya yanka za a biya, in dai abin da ya yanka ya yi daidai da abin da alƙalai suka tsara.
23 Aka, ina he hewa mahope, alaila, e haawi no oe i ke ola no ke ola,
Amma in akwai rauni mai tsanani, sai a ɗauki rai a maimakon rai,
24 I ka maka no ka maka, i ka lima no ka lima, i ka wawae no ka wawae.
ido don ido, haƙori don haƙori, hannu don hannu, ƙafa don ƙafa,
25 I ke kuni ana no ke kuni ana, i ka palapu no ka palapu, i ka paopao ana no ka paopao ana.
ƙuna don ƙuna, rauni don rauni, ƙujewa don ƙujewa.
26 A ina e hahau ke kanaka i ka maka o kana kauwakane, a i ka maka o kana kauwawahine, a oki loa ia, alaila, e hookuu wale iho oia ia ia, no kona maka.
“In mutum ya bugi bawa ko baiwa a ido, har idon ya lalace, dole yă’yantar da shi ko ita, maimakon ido.
27 A ina kui oia i ka niho o kana kauwakane, a i ka niho o kana kauwawahine, alaila, e hookuu wale iho oia ia ia, no kona niho.
In kuma ya fangare haƙorin bawa ko baiwa, dole yă’yantar da bawan ko baiwar, a maimakon haƙorin.
28 Ina e o iho ka bipi i ke kanaka, a i ka wahine, a make laua; alaila, e oiaio no e hailukuia ua bipi la, aole hoi e aiia kona io, a e hala ole ke kahu o ka bipi.
“In bijimi ya kashe namiji ko ta mace, dole a jajjefe bijimin har yă mutu, ba za a kuma ci namansa ba. Amma mai bijimin ba shi da laifi.
29 Aka, ina i o oia mamua, a na haiia i kona kahu, aole nae ia i hoopaa ia ia, a ua pepehi oia i ke kanaka, a i ka wahine paha, alaila, e hailukuia ua bipi la, a e make no hoi kona kahu.
In, har an san bijimin da wannan hali, an kuma yi wa mai shi gargaɗi, amma bai ɗaura shi ba, har ya kashe namiji ko ta mace, za a jajjefe bijimin tare da mai shi, har su mutu.
30 Aka, ina o hooukuia oia i ke kala, alaila, e haawi no oia i ka uku no kona ola, e like me ka mea i kauia maluna ona.
Amma fa, in an bukace shi yă biya, zai biya don yă fanshi ransa ta wurin biyan abin da aka aza masa.
31 Ina i o oia i ke keikikane, a ina i o oia i ke kaikamahine paha, e hanaia aku no oia e like me keia kanawai.
Wannan doka ta shafi batun bijimin da ya kashe ɗa ko’ya.
32 Ina e o iho ka bipi i ke kauwakane, a i ke kauwawahine paha, alaila, e uku aku oia i kanakolu sekela kala na ko laua haku, a e hailukuia ua bipi la.
In bijimin ya kashe bawa ko baiwa, mai shi zai biya shekel talatin na azurfa wa maigidan bawan, a kuma a jajjefe bijimin.
33 A ina wehe ke kanaka i lua, a ina eli ke kanaka i lua, aole hoi e uhi, a i haule ka bipi maloko, a he hoki paha;
“In mutum ya bar rami a buɗe, ko ya haƙa rami bai kuma rufe ba, sai saniya ko jaki ya fāɗi a ciki,
34 Alaila, e uku ka mea nana ka lua, a e haawi hoi i kala na ke kahu o laua; a e lilo ka mea make nana.
Mai ramin zai biya rashin da aka yi wa mai shi, matacciyar saniyan ko jakin, zai zama na mai ramin.
35 A ina hooeha ka bipi a ke kahi kanaka i ka kekahi, a make ia, alaila, e kuai lilo aku laua i ka bipi ola, a e puunaue i ke kala, a e puunaue no hoi laua i ka bipi i make.
“In bijimin mutum ya raunana bijimin wani, har ya mutu, sai mutanen biyu su sayar da mai ran, su raba kuɗin daidai, haka ma su yi da mai ran.
36 Aka, ina i ikeia ua o no ia bipi mamua, aole nae i hoopaa kona kahu ia ia, alaila, e oiaio no e uku aku no ia i bipi no ka bipi, a e lilo no ka bipi make nana.
Amma fa, in tun can, an san bijimin yana da wannan halin faɗa, duk da haka mai shi bai ɗaura shi ba, dole mai shi yă biya, dabba domin dabba, matacciyar dabbar kuwa tă zama nasa.