< Pukaana 12 >

1 OLELO mai la o Iehova ia Mose laua o Aarona, ma ka aina o Aigupita, i mai la,
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna a Masar,
2 Eia ka malama makamua o ko oukou mau malama, eia ka malama mua o ko oukou makahiki.
“Wannan wata za tă zama a gare ku wata na farko, wata na fari na shekararku.
3 E olelo aku olua i ka poe kanaka o ka Iseraela a pau, e i aku, I ka la umi o keia malama, e lawe kela kanaka keia kanaka i hipakeiki ma ko ka hale o na makua, he hipakeiki no ka hale hookahi.
Ka faɗa wa dukan jama’ar Isra’ila cewa a rana ta goma ga wannan wata, kowane mutum zai ɗauki ɗan rago domin iyalinsa, ɗaya domin kowane gida.
4 Aka, ina he uuku ko ka hale, aole lawa no ka hipakeiki, e lawe pu ia me kona hoalauna e kokoke aua ma kona hale, e like me ka nui o lakou; e like me ka ai ana a kela kanaka keia kanaka, pela no oukou e helu ai i na hipakeiki.
In akwai wani gidan da ba za su iya cinye rago guda ɗungum ba, saboda iyalin kima ne, to, sai su haɗa kai da maƙwabtansu, su ɗauki rago guda gwargwadon yawansu, bisa ga abin da mutum guda zai ci.
5 I hipakeiki kina ole ka oukou, he kane o ka makahiki hookahi: noloko o ka poe hipa paha, noloko o ka poe kao paha ka oukou e lawe ai ia ia.
Dabbobin da za ku zaɓa, dole su zama bana ɗaya, namiji marar tabo, za ku kuma kamo su daga cikin tumaki ko awaki.
6 Na oukou ia e malama a hiki i ka la umikumamaha o ia malama; a na ke anaina kanaka a pau o ka Iseraela e pepehi iho ia i ke ahiahi.
Za ku turke dabbar har rana ta goma sha huɗu ga wata, wato, sa’ad da dukan taron jama’ar Isra’ila za su yanka ragunansu da yamma.
7 A e lawe lakou i ke koko, a e kau aku ma na lapauila a elua, a maluna ma ka hoaka o ka puka o na hale, kahi a lakou e ai ai ia mea.
Sa’an nan za su ɗauki jinin, su shafa a gefen da yake saman dogaran ƙofa na gidajen da suke cin naman dabbobin.
8 A ia po no, e ai lakou i ka io i ohinuia i ke ahi, e ai pu lakou ia mea me ka palaoa hu ole, a me na mea mulemule.
A wannan dare, za su gasa naman, su ci da ganyaye masu ɗaci, da kuma burodi marar yisti.
9 Mai ai maka oukou ia mea, aole hoi i hoolapalapaia i ka wai; aka, e ohinuia i ke ahi; o kona poo, me kona mau wawae, a me kona naau.
Kada ku ci nama ɗanye, ko kuma dafaffe, amma a gasa shi, da kan, da ƙafafun, da kuma kayan cikin.
10 Mai waiho oukou i kekahi a ao; a ina e koe kekahi mea a ao, e hoopau oukou ia mea i ke ahi.
Kada ku bar kome yă kai gobe, abin da ya kai gobe kuwa, sai ku ƙone shi.
11 Penei oukou e ai ai; e hoolikiia ko oukou puhaka, a me na kamaa e paa ana ma ko oukou mau wawae, a me ke kookoo ma ko oukou lima: e ai wikiwiki oukou, no ka mea, o ka moliaola ia na Iehova.
Ga yadda za ku ci shi, ku yi ɗamara, takalma kuwa a ƙafafunku, kuna riƙe da sandunan tafiya a hannunku. Ku ci shi da gaggawa; Bikin Ƙetarewa ne na Ubangiji.
12 No ka mea, e hele aku ana au ma ka aina a pau o Aigupita i keia po, a e pepehi no wau i na hiapo a pau ma ka aina o Aigupita, o ka ke kanaka a me ka ka holoholona: a e hoopai aku no wau i na akua a pau o Aigupita: owau no Iehova.
“A wannan dare, zan ratsa Masar, in bugi kowane ɗan fari, na mutum da na dabba, zan kuma hukunta dukan gumakan Masar. Ni ne Ubangiji.
13 A o ke koko, oia ka hoailona no oukou ma na hale o ko oukou wahi: aia ike aku au i ke koko, e waiho wau ia oukou, aole e kau mai ka mea ino maluna o oukou e make ai, ia'u e pepehi iho ai i ko ka aina o Aigupita.
Jinin zai zama alama a gare ku, a gidajen da kuke; sa’ad da kuwa na ga jinin, zan ƙetare ku. Ba wata annoba mai hallakarwa da za tă taɓa ku yayinda na bugi Masar.
14 A e lilo no keia la i mea e hoomanao ai no oukou: a e malama oukou ia la i ahaaina na Iehova, a hiki i ko oukou mau hanauna a pau: e malama oukou ia i ahaaina, ma ke kanawai mau loa.
“Wannan rana za tă zama muku abin tunawa dukan zamananku masu zuwa, za ku kiyaye ta kamar biki ga Ubangiji, dawwammamiyar farilla ce har abada.
15 Ehiku mau la ka oukou e ai ai i ka berena hu ole; i ka la mua e hoolei aku oukou i ka mea hu mawaho o ko oukou mau hale: o ka mea nana e ai i ka berena hu, mai ka la akahi a hiki i ka la hiku, e okiia'ku ia mai ka Iseraela aku.
Kwana bakwai za ku ci burodi marar yisti. A rana ta fari, za ku fid da yisti daga gidajenku gama duk wanda ya ci abu mai yisti daga rana ta fari har zuwa rana ta bakwai, za a fid da shi daga Isra’ila.
16 A i ka la makamua, hookahi halawai hemolele ana, a i ka hiku o ka la, hookahi halawai hemolele ana o oukou. Ia mau la la, aohe hana maoli, o ka mea wale no a kela kanaka a keia kanaka e ai ai, oia wale no ka mea a oukou e hana'i.
A rana ta fari, za ku yi taro mai tsarki, haka kuma za ku sāke yi a rana ta bakwai. Kada ku yi aiki a waɗannan ranaku, sai dai ku shirya abinci domin kowa, abin da za ku yi ke nan kawai.
17 E malama no oukou i ka ahaaina berena hu ole; no ka mea, ia la no ua lawe mai au i ko oukou poe koa, mai ka aina mai o Aigupita: no ia mea, e malama oukou i keia la i ka oukou mau hanauna aku, ma ke kanawai mau loa.
“Ku yi Bikin Burodi Marar Yisti domin a wannan rana ce na fitar da ku ɓangare-ɓangare daga Masar. Ku kiyaye wannan rana ta zama muku dawwammamiyar farilla wa tsara masu zuwa.
18 I ka malama makamua, i ka la umikumamaha o ka malama, i ke ahiahi, alaila e ai oukou i ka berena hu ole, a hiki i ke ahiahi o ka la iwakaluakumamakahi o ua malama la.
A wata na fari, za ku ci burodi marar yisti daga yammancin ranar goma sha huɗu har zuwa yammancin ranar ashirin da ɗaya.
19 Ehiku la e loaa ole ai ka mea hu maloko o ko oukou mau hale. O ka mea ai i ka palaoa hu, oia ke hookiia aku mai ke anaina kanaka o ka Iseraela aku: ina paha ho kanaka e oia, a ina paha o ka mea i hanau ma ka aina.
Kada a sami yisti a gidajenku har kwana bakwai. Kuma duk wanda ya ci wani abu mai yisti, za a fid da shi daga taron jama’ar Isra’ila, ko baƙo ne, ko haifaffen ɗan ƙasa.
20 Mai ai oukou i kekahi mea hu: ma na hale o oukou a pau, e ai oukou i ka berena hu ole.
Kada ku ci wani abincin da aka yi da yisti. Ko’ina kuka zauna, dole ku ci burodi marar yisti.”
21 Alaila, kii aku la o Mose i na lunakahiko a pau o ka Iseraela, i aku la ia lakou, E wae oukou, a e lawe i ka oukou hipakeiki, ma ka oukou mau ohana, a e pepehi i ka moliaola.
Sa’an nan Musa ya kira dukan dattawan Isra’ila ya ce musu, “Ku je da sauri ku zaɓi dabbobin iyalanku, ku yanka ragon Bikin Ƙetarewa.
22 A e lawe oukou i pupu husopa, a e kupenu iho iloko o ke koko ma ko kiaha, a e hamo i ka hoaka a me na lapauila elua o ka puka, i ke koko oloko o ke kiaha, a mai puka aku kekahi o oukou mawaho o ka puka o kona hale, a kakahiaka.
Ku ɗauki ƙunshin itacen hizzob, ku tsoma cikin jinin da yake a kwano, ku yayyafa wa dogaran ƙofa duka biyu, da bisa kan ƙofar. Kada wani daga cikinku yă fita daga ƙofar gidansa sai da safe.
23 No ka mea, e hele ae ana o Iehova e pepehi i ko Aigupita, a ike mai ia i ke koko ma ka hoaka a ma na lapauila, e waiho no o Iehova ia puka, aole ia e ae mai i ka mea luku e komo i ko oukou mau hale e pepehi mai.
Sa’ad da Ubangiji yake ratsa ƙasar don yă bugi Masarawa, zai ga jinin a bisa da kuma gefen madogaran ƙofa, zai ƙetare ƙofar, ba zai bar mai hallakawa yă shiga gidajenku, yă buge ku ba.
24 E malama oukou i keia mea i kanawai mau loa no oukou, a no ka oukou poe keiki.
“Ku kiyaye waɗannan dokokin a matsayin dawwammamiyar farilla, da ku da’ya’yanku har abada.
25 A hiki aku oukou i ka aina a Iehova e haawi mai ai no oukou, e like me kana i olelo mai ai, alaila e malama oukou i keia oihana.
Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji zai ba ku yadda ya alkawarta, ku kiyaye wannan biki.
26 A i ka wa e olelo mai ai ka oukou poe keiki ia oukou, Heaha ke ano o keia oihana ia oukou?
Sa’ad da kuma’ya’yanku suka tambaye ku, ‘Mece ce manufar wannan biki?’
27 E olelo aku oukou, O ka mohai moliaola keia na Iehova, nana no i waiho i na hale o na mamo a Iseraela ma Aigupita, i ka wa ana i pepehi aku ai i ko Aigupita, a hoopakele mai i ko na hale o makou. Kulou iho la ke poo o kanaka a hoomana aku la.
Sai ku faɗa musu, ‘Hadaya ce ta Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji, domin ya tsallake gidajen Isra’ilawa a Masar, lokacin da ya kashe Masarawa, amma bai taɓa gidajenmu ba.’” Sai mutane suka rusuna, suka yi sujada.
28 Hele aku la na mamo a Iseraela, hana iho la e like me ka mea a Iehova i kauoha mai ai ia Mose laua o Aarona, pela lakou i hana'i.
Isra’ilawa suka tafi suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa da Haruna.
29 A hiki i ke aumoe, pepehi iho la o Iehova i na hiapo a pau, ma ka aina o Aigupita, mai ka hiapo a Parao, a ka mea noho maluna o kona nohoalii, a hiki i ka hiapo a ka mea pio iloko o ka hale luapaahao, a me na hiapo a pau a na holoholona.
Da tsakar dare, sai Ubangiji ya karkashe dukan’ya’yan fari a ƙasar Masar, tun daga ɗan farin Fir’auna, wato, magājinsa, har zuwa ɗan fari na ɗan sarƙa da yake kurkuku, har da’ya’yan fari na dabbobi.
30 Ala ae la o Parao i ka po, oia a me kana poe kauwa a pau, a me ko Aigupita a pau: a he nui loa ke kupinai ana ma Aigupita, no ka mea, aohe hale i make ole ai kekahi.
Fir’auna da dukan fadawansa da kuma dukan Masarawa, suka tashi a cikin daren da kuka mai zafi, aka kuma ji kukan a ko’ina a cikin ƙasar Masar, gama ba gidan da ba a yi mutuwa ba.
31 Hea mai la oia ia Mose laua o Aarona i ka po, i mai la, E ku ae olua e hele aku maiwaena aku o ko'u poe kanaka, o olua a me na mamo a Iseraela: e hele, e hookauwa aku na Iehova, e like me ka olua i olelo mai ai.
A cikin daren, Fir’auna ya aika a kira Musa da Haruna ya ce, “Ku tashi, ku da jama’arku, ku fita daga cikin jama’ata. Ku tafi, ku bauta wa Ubangiji yadda kuka ce.
32 E lawe pu aku no i ka oukou poe hipa, a me ka oukou poe bipi, e like me ka olua i olelo ai, a e hele: a e hoomaikai hoi olua ia'u.
Ku kwashi garkunanku na tumaki da na awaki, da na shanu, ku yi tafiyarku kamar yadda kuka ce, amma ku sa mini albarka.”
33 Ikaika iho la ka manao o ko Aigupita, e kipaku koke ia lakou mai ka aina aku: no ka mea, Ua pau makou i ka make, wahi a lakou.
Masarawa suka matsa wa Isra’ilawa su fita daga ƙasarsu da sauri. Gama mutanen Masar sun ce, “Ai, za mu mutu duka, in ba su tafi ba!”
34 Lawe mai la na kanaka i ka lakou berena maka, hu ole, a me ko lakou mau papawiliai, ua ope pu ia me ko lakou lole maluna o ko lakou mau hokua.
Sai mutanen suka ɗauki garin da sun kwaɓa ba yisti a ciki, tare da ƙwaryansu na aikin kwaɓan, suka nannaɗe su a mayafansu, suka rataye a kafaɗunsu.
35 Hana iho la na mamo a Iseraela, e like me ka olelo ana a Mose, a nonoi aku la i ko Aigupita i na mea kala, a me na mea gula, a me na mea aahu.
Isra’ilawa kuwa suka yi yadda Musa ya umarce su, suka roƙi Masarawa kayan adonsu na azurfa da na zinariya, da kuma tufafi.
36 A haawi mai la o Iehova i ka lokomaikaiia i na kanaka imua o ka maka o ko Aigupita, a haawi mai la lakou: pela lakou i hao ai i ko Aigupita.
Ubangiji kuwa ya sa Isra’ilawa suka yi farin jini a wurin Masarawa, Masarawa kuma suka saki hannu wa mutanen, suka ba su duk abin da suka roƙa; ta haka Isra’ilawa suka washe Masarawa.
37 Hele mai la na mamo a Iseraela mai Ramese a hiki i Sukota, eono paha haneri tausani kane i hele wawae, a he okoa na kamalii.
Isra’ilawa suka kama tafiya daga Rameses zuwa Sukkot. Akwai maza dubu ɗari shida da suke tafiya da ƙafa, ban da mata da yara.
38 Hele pu mai la ka poe e he nui loa, i hui pu ia mai, a me na hipa, a me na bipi, he nui loa na holoholona.
Waɗansu mutane da yawa da ba Isra’ilawa ba, suka haura tare da su, da garkunan shanu, da na tumaki da awaki.
39 Pulehu iho la lakou i berena hu ole o ka berena maka a lakou i lawe mai ai mai Aigupita mai, aole ia i hu, no ka mea, ua kipakuia lakou mailoko mai o Aigupita, aole i hiki ia lakou ke kali, aole hoi lakou i hoomakaukau i o na lakou iho.
Suka toya burodi marar yisti da garin da aka kwaɓa wanda suka kawo daga Masar. Garin da aka kwaɓan ba shi da yisti, domin an kore su daga Masar, ba su kuwa sami damar shirya wa kansu abinci ba.
40 O ka noho ana o na mamo a Iseraela, i noho ai lakou ma Aigupita, eha haneri makahiki a me ke kanakolu.
Zaman da Isra’ilawa suka yi a Masar, ya kai shekara 430.
41 A pau aku la ia mau makahiki eha haneri a me ke kanakolu, ia la no, hele mai la ka poe koa a pau o Iehova, mai ka aina mai o Aigupita.
A ranar da shekara 430 ɗin nan suka cika, a ran nan ne dukan ɓangare-ɓangare na mutanen Ubangiji suka bar Masar.
42 He po ia e hoomanao nui ia'i no Iehova, no kona lawe ana mai ia lakou mai ka aina mai o Aigupita: eia no ka po o Iehova e hoomanaoia'i e na mamo a pau a Iseraela, ma na hanauna o lakou.
Gama Ubangiji ya yi tsaro a wannan dare, domin yă fitar da su daga Masar, a wannan dare, dole dukan Isra’ilawa su yi tsaro, don su girmama Ubangiji, cikin dukan tsararraki masu zuwa.
43 I mai la o Iehova ia Mose laua o Aarona, Eia no ke kanawai o ka moliaola; aole e ai ke kanaka e i a mea.
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna, “Waɗannan ne ƙa’idodin Bikin Ƙetarewa. “Ba baƙon da zai ci shi.
44 Aka, o ke kauwa a kela kanaka keia kanaka i kuaiia i ke kala, aia okipoepoe iho oe ia ia, alaila ia e ai iho ai ia mea.
Duk bawan da kuka sayo, yana iya ci, in dai an yi masa kaciya,
45 O ke kanaka e, a me ke kauwa i hoolimalimaia, aole laua e ai ia mea.
amma wanda ba ya zama tare da ku na ɗinɗinɗin, da kuma wanda aka ɗauki hayansa, ba zai ci ba.
46 I ka hale hookahi no e aiia'i ia mea; mai lawe oukou i kekahi io ma kahi e aku mawaho o ka hale; mai uhai hoi oukou i kekahi iwi o ia mea.
“Dole a ci shi a cikin gida ɗaya; kada a kai naman waje. Kada a karya wani daga ƙasusuwansa.
47 E hana no ke anaina kanaka o Iseraela a pau ia mea.
Dole dukan taron jama’ar Isra’ila su yi bikin.
48 A i noho pu kekahi kanaka e me oe, a manao no ia e malama i ka moliaola no Iehova, e okipoepoeia kona poe kane a pau; alaila e hookokoke mai ia e malama ia mea; a e lilo ia i mea like me ka mea i hanauia ma ka aina: no ka mea, aole loa e ai kekahi ia mea, ke okipoepoe ole ia oia.
“Baƙon da yake zama tare da ku da yake so yă yi Bikin Ƙetarewar Ubangiji, dole yă yi wa dukan mazan da suke cikin gidansa kaciya; sa’an nan ne zai iya yin abubuwa kamar haifaffen ɗan ƙasa.
49 Hookahi no kanawai no ke kanaka i hanauia ma ko oukou wahi, a me ke kanaka e, e noho pu ana me oukou.
Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ta shafi ɗan ƙasa da kuma baƙon da yake zama a tsakaninku.”
50 Pela no i hana'i na mamo a Iseraela a pau; e like me ka mea a Iehova i kauoha mai ai ia Mose a ia Aarona, pela lakou i hana'i.
Dukan Isra’ilawa suka yi na’am da shi, suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa da Haruna.
51 Ia la no, lawe mai la no o Iehova i na mamo a Iseraela mai ka aina o Aigupita mai, ma ko lakou poe koa.
A wannan rana, Ubangiji ya fito da Isra’ilawa ɓangare-ɓangare daga Masar.

< Pukaana 12 >