< Kekahuna 12 >
1 E HOOMANAO oe i kou Mea nana i hana, I na la o kou noho opiopio ana; Oi hiki ole mai na la ino, A hookokoke ole ia mai na makahiki, Au e olelo ai, Aole o'u oluolu i keia mau mea:
Ka tuna da Mahaliccinka a kwanakin ƙuruciyarka, kafin lokacin wahala ta zo shekaru kuma su ƙarato sa’ad da za ka ce, “Ba na jin daɗinsu,”
2 I ka wa i pouli ole ai ka la, a me ka malamalama, O ka mahina hoi a me na hoku; A hoi ole mai na ao mahope o ka ua:
kafin rana da haske wata da taurari su daina haske, gizagizai kuma su tattaru bayan da suka sheƙa ruwa;
3 I ka la i haalulu ai na kiai hale, A kulou ilalo na kanaka ikaika; A oki ka poe wili no ka hapa, A i pouli ai na mea nana ma na puka makani;
sa’ad da masu tsaron gida suke rawar jiki, majiya ƙarfi kuma suka rasa ƙarfi, sa’ad da masu niƙa suka daina don ba su da yawa, idanun da suke duba ta taga suka duhunta;
4 A paniia na puka ma ke alanui, I ka wa i uuku mai ai ka leo o ka wili ana; A e ala ae oia i ka leo o ka manu, A e hoohaahaaia na kaikamahine lea i ke oli a pau.
sa’ad da aka rufe ƙofofin shiga tituna ƙarar niƙa kuma ya tsagaita; sa’ad da kukan tsuntsaye ta farkar da mutane, ba a kuwa jin waƙoƙinsu,
5 A makau lakou i na mea kiekie; Aia hoi ma ke alanui na mea e weliweli ai, Ua hoopailua hoi ka laau alemona, A o ka uhini, he mea ia e kaumaha ai, A lilo no hoi ka hua kepa i mea mikomiko ole; No ka mea, hele ke kanaka i kona hale mau, A hele ka poe kanikau ma na alanui:
sa’ad da mutane suke jin tsoron tudu da kuma hatsarori a tituna; sa’ad da itacen almon ya toho, fāra kuma ya yi ta jan jikinsa da ƙyar, sha’awace-sha’awace sun kafe. Daga nan mutum ya tafi madawwamiyar gidansa ya bar masu makoki suna ta yi.
6 Oi moku ole ia ke kaula kala, Aole hoi i naha ke kiaha gula; Aole naha ka bakeke ma ka punawai, Aole hoi i naha ke kaa ma ka luawai.
Ka tuna da shi, kafin igiyar azurfa ta katse, ko tasar zinariya ta fashe; kafin tulu yă ragargaje a maɓulɓula, ko guga ta tsinke a rijiya,
7 Alaila, e hoi ka lepo i ka honua e like me ia mamua, A o ka uhane, e hoi ia i ke Akua nana ia i haawi mai.
turɓaya ta koma ƙasar da ta fito, rai kuma yă koma ga Allah wanda ya ba da shi.
8 Lapuwale o na lapuwale, wahi a ke kahuna, pau na mea i ka lapuwale.
“Ba amfani! Ba amfani!” In ji Malami, “Gaba ɗaya ba amfani!”
9 Eia hoi kekahi: I ko ke kahuna naauao ana, ua ao mau aku oia i na kanaka; ua noonoo oia, a imi, a hooponopono hoi i na olelo akamai he nui hoa.
Ba kawai Malami ya kasance mai hikima ba, amma kuma ya koyar da mutane. Ya yi tunani ya kuma yi binciken da ya tsara karin magana masu yawa.
10 Ua imi iho la ke kahuna e loaa mai na olelo oluolu, a o na mea i kakauia, he olelo pololei ia a me ka oiaio hoi.
Malami ya yi bincike don yă sami kalmomin da suka dace, kuma abin da ya rubuta daidai ne da kuma gaskiya.
11 O na olelo a ka poe naauao, ua like ia me na mea oi, a me na kui i makiaia a paa e ka poe luna o ka ahakanaka, na mea i haawiia'ku ai e ke kahu hookahi.
Kalmomin masu hikima kamar tsinken tsokanar dabba ne, tarin maganganunsu kuma kamar ƙusoshi ne da aka kafa daram, da aka ba wa Makiyayi guda.
12 Eia hoi kekahi: E aoia mai oe, e ka'u keiki, e keia mau mea; o ka hana ana i na buke he nui loa, he mea hope ole ia, a o ka imi nui i ka palapala, he mea ia e luhi ai ke kino.
Ka yi hankali ɗana, game da duk wani ƙari a kan waɗannan. Wallafa littattafai ba shi da iyaka, kuma yawan karatu yakan gajiyar da jiki.
13 E hoolohe oe i ka hope o keia mau mea a pau. E makau i ke Akua, a e malama i kona mau kanawai, no ka mea. oia ka ke kanaka [pono] a pau.
Yanzu an ji kome; ga ƙarshen magana. Ka ji tsoron Allah ka kuma kiyaye umarnansa, gama wannan shi ne dukan hakkin mutum.
14 No ka mea, e hookomo ana ke Akua i na hana a pau, a me na mea a pau i hunaia iloko o ka hookolokoloia, ina paha he pono, ina paha he hewa.
Gama Allah zai shari’anta kowane irin aiki, har da waɗanda aka yi a ɓoye, ko nagari ne, ko mugu.