< Kanawailua 2 >

1 A LAILA huli ae la kakou, a hele aku la i ka waonahele ma ke ala o ke Kaiula, e like me ka Iehova i kauoha mai ai ia'u; a hoopuni ae la kakou i ka mauna o Seira i na la he nui.
Sai muka juya muka kama hanya, muka nufi hamada, ta hanyar Jan Teku yadda Ubangiji ya umarce ni. Da daɗewa muka yi ta yawo kewaye da ƙasar tudun Seyir.
2 Olelo mai la o Iehova ia'u, i mai la,
Sai Ubangiji ya ce mini,
3 Ua loihi ko oukou hoopuni ana i keia mauna: e huli ae oukou ma ke kukuluakau.
“Kun yi ta yawo kewaye da ƙasar tudun nan da daɗewa; yanzu ku juya, ku nufi arewa.
4 A e kauoha aku oe i na kanaka, penei, E hele ana oukou ma ka mokuna o ko oukou poe hoahanau, o na mamo a Esau e noho ana ma Seira; a e makau mai auanei lakou ia oukou: nolaila e malama nui oukou ia oukou iho:
Ka ba wa mutane waɗannan umarnai, ka ce, ‘Kuna gab da wucewa cikin yankin’yan’uwanku, zuriyar Isuwa, wanda yake zama a Seyir. Za su ji tsoronku, amma ku yi hankali
5 Mai hakaka oukou me lakou; no ka mea, aole au e haawi aku i kekahi o ko lakou aina no oukou, aole i kekahi kapuwai; no ka mea, ua haawi aku au i ka mauna o Seira i wahi e noho ai no Esau.
kada ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku wata ƙasa daga cikinsu ba, ba ma wadda za tă iya isa ku sa ƙafarku a kai. Na ba wa Isuwa ƙasar tudu ta Seyir, ta zama tasa.
6 E kuai oukou i ka lakou ai i ke kala, i ai ai oukou; a e kuai hoi oukou i ko lakou wai i ke kala, i inu ai oukou.
Duk abincin za ku ci, da ruwan da za ku sha, za ku biya su.’”
7 No ka mea, ua hoopomaikai mai o Iehova kou Akua ia oe ma na hana a pau a kou lima; ua ike no ia i kou hele ana ma keia waonahele nui; me oe no o Iehova kou Akua i neia mau makahiki he kanaha; aole oe i nele i kekahi mea.
Ubangiji Allahnku ya albarkace ku cikin dukan aikin hannuwanku. Ya kiyaye ku cikin tafiyarku a duk fāɗin hamada. Waɗannan shekaru arba’in Ubangiji Allahnku ya kasance tare da ku, ba kuwa kun rasa wani abu ba.
8 A ia kakou i maalo ae mai ko kakou poe hoahanau aku, na mamo a Esau, e noho ana ma Seira, ma ke ala o ka papu mai Elata aku, a mai Ezionagabera, huli ae kakou a hele i ke ala ma ka waonahele o Moaba.
Saboda haka muka ci gaba, muka wuce’yan’uwanmu, zuriyar Isuwa, wanda yake zama a Seyir. Muka bar hanyar Araba, wadda ta haura daga Elat da Eziyon Geber, muka nufi wajen hamadar Mowab.
9 Olelo mai la o Iehova ia'u, Mai hana ino aku i ko Moaba, aole e ku e ia lakou i ke kaua ana; aole au e haawi i ko lakou aina i wahi e noho ai no oukou; no ka mea, ua haawi aku au ia Ara i wahi e noho ai no na mamo a Lota.
Sai Ubangiji ya ce mini, “Kada ku dami Mowabawa, ko ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku wani sashe na ƙasarsu ba. Na ba da Ar ga zuriyar Lot, ta zama mallakarsu.”
10 I ka manawa mamua i noho ai ka poe Emima malaila, he poe nunui a lehulehu, he poe loihi e like me ka poe Anakima;
(Emawa, mutane ne masu ƙarfi da kuma yawa, suna kuma da tsayi kamar Anakawa, dā sun zauna a can.
11 Ua manaoia lakou, he poe kanaka nunui e like me ka poe Anakima; aka, ua kapaia lakou e ko Moaba, he poe Emima.
Kamar Anakawa, su ma an ɗauka su Refahiyawa ne, amma Mowab suna kiransu Emawa.
12 I ka manawa mamua i noho ai ka poe Horima ma Seira: aka, na na mamo a Esau i hookuke aku lakou, a luku i ua poe la imua o lakou, a noho iho la ma ko lakou la wahi; e like me ka Iseraela i hana aku ai i ka aina o ko lakou wahi i noho ai a Iehova i haawi mai ai no lakou.
Haka ma Horiyawa, a dā sun zauna a Seyir, amma zuriya Isuwa suka kore su. Suka hallaka Horiyawa da suke kafinsu, suka kuma zauna a wurinsu, kamar dai yadda Isra’ila ta yi a ƙasar da Ubangiji ya ba su a matsayin mallaka.)
13 Ano hoi, e ku iluna, a e hele aku ma kela aoao o ke kahawai o Zareda: a hele aku kakou ma kela aoao o ke kahawai o Zareda.
Ubangiji kuwa ya ce, “Yanzu ku tashi ku ƙetare Kwarin Zered.” Sai muka ƙetare kwarin.
14 A o na makahiki o ko kakou hele ana mai Kadesabanea mai, a hiki kakou ma ke kahawai o Zareda, he kanakolu ia a me kumamawalu; a pau ka hanauna a pau o na kanaka koa i ka nalowale iwaena o ka poe kaua, e like me ka Iehova i hoohiki ai ia lakou.
Dukan shekarun da muka yi a tafiyarmu daga Kadesh Barneya zuwa lokacin da muka ƙetare Kwarin Zered, sun kai shekaru talatin da takwas. A lokacin, wannan tsara gaba ɗaya ta mutanen da suka isa yaƙi sun mutu daga sansani, yadda Ubangiji ya rantse musu.
15 No ka mea, ku e mai la ka lima o Iehova ia lakou e luku ia lakou mailoko aku o ka poe kaua, a pau lakou i ka make.
Hannun Ubangiji ya yi gāba da su sai da ya hallaka su ƙaƙaf daga sansani.
16 A i ka manawa i pau ai na kanaka koa i ka lukuia, a i ka make iwaena o na kanaka,
To, sa’ad da na ƙarshe cikin waɗannan mayaƙa a cikin mutanen ya rasu,
17 Olelo mai la o Iehova ia'u, i mai la,
sai Ubangiji ya ce mini,
18 E hele ana oe i ka mokuna o Moaba i Ara i keia la:
“Yau za ku wuce ta yankin Mowab a Ar.
19 A hiki aku oe a kokoke i na mamo a Amona, mai hana ino aku ia lakou, aole hoi e hakaka aku me lakou: aole au e haawi i wahi e noho ai nou ma ka aina o na mamo a Amona; no ka mea, ua haawi aku au ia i wahi e noho ai no na mamo a Lota.
Sa’ad da kuka iso kusa da Ammonawa, kada ku dame su, ko ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku mallakar wata ƙasar da take ta Ammonawa ba. Na riga na ba da ita mallaka ga zuriyar Lot.”
20 (Ua manaoia hoi ia he aina kanaka nunui: o na kanaka nunui i noho ai malaila i ka manawa kahiko, a ua kapaia lakou e ka Amona, he Zamezumima;
(Wannan ita ma a ɗauka ta a matsayin ƙasar Refahiyawa waɗanda dā sun zauna a can ne; amma Ammonawa suna ce da su Zamzummawa.
21 He poe kanaka nunui, a lehulehu, a loihi, e like me na Anakima; aka, na Iehova lakou i luku aku imua o lakou, a hookuke aku lakou ia poe, a noho iho la ma ko lakou wahi:
Mutane ne masu ƙarfi da kuma yawa, suna kuma da tsayi kamar Anakawa. Ubangiji ya hallaka su daga gaban Ammonawa, waɗanda suka kore su, suka kuma zauna a wurinsu.
22 E like me kana i hana aku ai no na mamo a Esau e noho ana ma Seira, ia ia i luku ai i ka poe Horima imua o lakou; hookuke aku la lakou ia poe, a noho iho la ma ko lakou wahi, a hiki i keia la:
Ubangiji ya yi daidai yadda ya yi wa zuriyar Isuwa waɗanda suka zauna a ƙasar Seyir, sa’ad da ya hallaka Horiyawa a gabansu. Su kuma suka kore su, suka zauna a wurinsu. Har wa yau, zuriyar Isuwa ne suke zama a can.
23 A o ko Ava e noho ana ma Hazerima a hiki i Aza, na ko Kapetora, mai Kapetora mai, i luku aku lakou, a noho iho la ma ko lakou la wahi.)
Kusan abu ɗaya ya faru, sa’ad da Kaftorawa daga ƙasar Kaftor suka hallaka Awwiyawa, waɗanda dā suke zaune a yankin ƙauyukan da suke kewaye da Gaza. Suka zauna a wurinsu.)
24 E ku oukou iluna, e hele aku, a hiki ma keia kapa o ke kahawai o Arenona: aia hoi, ua haawi aku au ia Sihona no ka Amora, ke alii o Hesebona, a me kona aina iloko o kou lima; e hoomaka oe e komo, a e ku e aku ia ia i ke kaua.
“Ku fito yanzu ku ƙetare Kwarin Arnon. Duba, na ba da Sihon mutumin Amoriyawa a hannunku, na kuma ba da sarkin Heshbon da ƙasarsa. Ku fara mallake ta, ku kuma yi yaƙi da shi.
25 I keia la e hoomaka ai au e kau i ka makau ia oe, a me ka weliweli ia oe, maluna o na lahuikanaka malalo ae o ka lani a pau, ka poe i lohe i kou kaulana ana, a e haalulu lakou, a e pilihua auanei nou.
A wannan rana zan fara sa tsoro da fargabanku a kan dukan al’ummai, a ƙarƙashin sama. Za su ji labarinku, za su yi rawan jiki, su kuma damu saboda ku.”
26 A hoouna aku la au i na elele mai ka waonahele o Kedemota aku io Sihona la, ke alii o Hesebona, me ka olelo aloha, i aku la,
Daga hamadar Kedemot, na aiki’yan saƙo zuwa wurin Sihon sarkin Heshbon, a kan ina neman zaman lafiya, ina cewa,
27 E ae mai oe ia'u e hele au ma kou aina: e hele au ma ke ala loa, aole au e kapae ma ka akau, aole hoi ma ka hema.
“Bari mu wuce cikin ƙasarka. Za mu bi ta kan hanya ne kaɗai; ba za mu ratse dama ko hagu ba.
28 E kuai mai oe i ai na'u no ke kala, i ai iho ai au; a e haawi mai i wai no'u no ke kala, i inu ai hoi au; e hele wawae wale no au;
Ka sayar mana da abincin da za mu ci, da kuma ruwan da za mu sha a farashinsu na azurfa. Ka dai bar mu mu wuce ta ƙasarka kawai,
29 (E like me na mamo a Esau, e noho ana ma Seira, a me ko Moaba e noho ana ma Ara i hana mai ai ia'u; ) a hiki aku au ma keia kapa o Ioredane, ma ka aina a Iehova ko makou Akua i haawi mai ai ia makou.
kamar yadda zuriyar Isuwa, waɗanda suke zaune a Seyir, da Mowabawa, waɗanda suke zaune a Ar, suka yardar mana, gama muna so mu ƙetare Urdun zuwa ƙasa wadda Ubangiji, Allahnmu yake ba mu.”
30 Aka, aole i ae mai o Sihona, ke alii o Hesebona, e hele kakou ma o na la; no ka mea, hoopaakiki mai la o Iehova kou Akua i kona naau, a hooku e oia i kona manao, i hoolilo ai oia ia ia iloko o kou lima, e like me ia i keia la.
Amma Sihon sarkin Heshbon ya ƙi yă bar mu mu wuce a ciki. Gama Ubangiji Allahnku ya sa ruhunsa ya taurare don yă ba da shi a hannuwanku kamar yadda ya yi yanzu.
31 A olelo mai o Iehova ia'u, aia hoi, ua hoomaka iho nei au e hoolilo ia Sihona, a me kona aina ia oe: e komo oe, i lilo ai kona aina ia oe.
Ubangiji ya ce mini, “Duba, na fara ba da Sihon da ƙasarsa gare ku. Yanzu ku fara cinta, ku kuma mallake ƙasarsa.”
32 Alaila hele ku e mai la o Sihona ia kakou, oia a me kona poe kanaka a pau, i ke kana ma Iahaza.
Sa’ad da Sihon da dukan sojojinsa suka fito don su sadu da mu, a yaƙi, a Yahaz,
33 A hoolilo mai o Iehova ko kakou Akua ia ia imua o kakou, a luku aku la kakou ia ia, a me kana mau keiki, a me kona poe kanaka a pau.
sai Ubangiji Allahnmu ya ba da shi gare mu, muka kuwa buga shi tare da’ya’yansa maza da kuma dukan sojojinsa.
34 A hoopio aku la kakou i kona mau kulauakauhale a pau, a luku aku i na kanaka o na kulanakauhale a pau, a me na wahine a me na kamalii, aole kakou i hookoe i kekahi.
A wannan lokaci mun ci dukan biranensa, muka kuma hallaka su, maza, mata da kuma yara. Ba mu bar wani da rai ba.
35 O na holoholona wale no ka kakou i la we pio ai na kakou, a me ka waiwai o na kulanakauhale, oia ka kakou i lawe.
Amma muka washe, muka kuma kwasa shanu da kuma ganima daga biranen wa kanmu.
36 Mai Aroera ma kapa o ke kahawai o Arenona, a me ke kulanakauhale ma ke kahawai a hiki i Gileada, aole kekahi kulanakauhale i lanakila maluna o kakou; na Iehova ko kakou Akua i hoolilo mai na mea a pau ia kakou.
Ubangiji Allahnmu ya taimake mu muka ci Arower wadda take a gefen Kwarin Arnon, da garin da yake a cikin kwarin, har zuwa Gileyad. Babu garin da ya gaggare mu.
37 Aole nae oe i hele ma ka aina o na mamo a Amona, aole hoi ma na wahi o ke kahawai o Iaboka, aole hoi ma na kulanakauhale o na mauna, aole hoi ma kekahi wahi a Iehova ko kakou Akua i papa mai ai ia kakou.
Amma bisa ga umarnin Ubangiji Allahnmu, ba ku yi kusa da wata ƙasar Ammonawa, ko ƙasar da take gefen kwarin kogin Yabbok, ko kuwa wadda take kewaye da birane cikin tuddai ba.

< Kanawailua 2 >