< Oihana 21 >
1 A I ko makou kaawale ana aku, mai o lakou aku, ee aku la makou, a holo pololei mai la i Ko, a ia la ae, i Rode, a malaila mai i Patara.
Da muka rabu da su, muka shiga jirgin ruwa muka mike hanya zuwa birnin Kos, washegari sai birnin Rodusa, daga nan sai kuma zuwa birnin Batara.
2 A loaa ia makou kekahi moku e holo ana i Poinike, ee aku la makou, a holo aku la.
Da muka sami jirgi mai hayewa zuwa Fonisiya sai muka shiga.
3 A ike aku la makou ia Kupero, haalele aku la makou ia wahi ma ka lima hema, a holo aku la makou i Suria, a pae makou ma Turo; no ka mea, malaila e hooleiia'i ka ukana o ka moku.
Da muka hango tsibirin Kubrus muka bar shi a hagun mu muka nufi Suriya, muka sauka a birnin Taya domin a nan ne jirgin ruwan zai sauke kayansa.
4 Loaa ia makou kekahi mau haumana, noho iho la makou ilaila i na la ehiku; olelo mai la lakou ia Paulo, na ka Uhane, i pii ole oia i Ierusalema.
Bayan mun sami almajirai sai muka zauna can kwana bakwai. Al'majiran suka ce ma Bulus, ta wurin Ruhu, kada ma ya je Urushalima.
5 A i ka pau ana o keia mau la, haalele iho la makou ia wahi a hele aku la; ukali aloha mai la lakou a pau, a me na wahine, a me na keiki ia makou, a hiki mawaho o na kulanakauhale la; kukuli iho la makou ma kahakai, pule aku la.
Bayan 'yan kwanaki muka cigaba da tafiyarmu. Dukansu da matansu da 'ya'yansu suka raka mu har bayan birnin. Sa'annan muka durkusa a bakin gacci muka yi addu'a muka yi sallama da juna.
6 Honi ae la makou i kekahi i kekahi, ee aku la makou i ka moku; a hoi aku la lakou i ko lakou wahi.
Sai muka shiga jirgin ruwa, su kuma suka koma gida.
7 A pau ko makou holo ana ma ka moku, mai Turo mai, hiki makou i Petolemai, honi aku la i na hoahanau, a noho pu iho la me lakou, hookahi la.
Da muka gama tafiyarmu a Taya muka iso Talamayas. A nan ne muka gaisa da 'yan'uwa, muka zamna kwana daya da su.
8 A ia la ae, hele mai la makou ka poe me Paulo a hiki i Kaisareia; a komo aku la iloko o ka hale o Pilipo, o ke kahuna euanelio, oia kekahi o na hiku, a noho pu iho la makou me ia.
Washegari muka tashi muka tafi Kaisariya. Muka shiga gidan Filibus mai shaida bishara, daya daga cikin bakwai din, muka zauna da shi.
9 Eba ana mau kaikamahine puupaa i wanana mai la.
Wannan mutum yana da 'ya'ya hudu mata, budurwai masu yin annabci.
10 Noho iho la makou ilaila i na la he nui, a iho mai la kekahi kaula mai Iudea mai, o Agebo ka inoa.
Sa'anda muka zauna can 'yan kwanaki, wani annabi ya zo daga Yahudiya mai suna Agabus.
11 A hiki mai la ia io makou la, lawe iho la ia i ko Paulo kaei, nakinaki iho la i kona mau lima a me na wawae ona iho, i ae la, Ke i mai nei ka Uhane Hemolele, Penei e nakinaki ai na Iudaio ma Ierusalema i ke kanaka nona keia kaei, a e haawi aku ia ia i na lima o ko na aina e.
Ya zo wurinmu ya dauki damarar Bulus ya daure tasa kafar da hannayensa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki ya ce, 'Haka Yahudawa za su daure mai wannan damarar, zasu kuma bashe shi ga al'ummai.'”
12 A lohe makou i kela mau mea, noi ae la makou, a me kolaila poe ia ia, i pii ole ia i Ierusalema.
Da muka ji wannan sakon, sai dukanmu da mazaunan wurin muka roki Bulus kada ya tafi Urushalima.
13 I mai la o Paulo, Heaha ka oukou e hana'i pela, me ka uwe mai, a nahae ko'u naau? No ka mea, ua makaukau no wau, aole e nakinaki wale no, aka, e make no hoi kekahi ma Ierusalema, no ka inoa o ka Haku o Iesu.
Sai Bulus ya amsa ya ce, “Me kuke yi, kuna kuka kuna karya mani zuciya? Bama a shirye don dauri kadai nake ba har ma da mutuwa a Urushalima, sabili da sunan Ubangiji Yesu.”
14 Aole loa ia i ae mai, oki ae la makou, i iho la, E hookoia no ko ka Haku makemake.
Tun da Bulus bashi da niyyar a rinjaye shi, muka daina kuka muka ce, “Bari nufin Ubangiji ya tabbata.”
15 A mahope iho o keia mau la, hoomakaukau iho la makou, a pii aku la i Ierusalema.
Bayan wadannan kwanaki, muka dauki jakkunanmu muka haura Urushalima.
16 Hele pu aku la no me makou kekahi poe o na haumana, no Kaisareia, e alakai pu ana ia Menasona, no Kupero, he haumana kahiko ia, a hookipaia makou e ia.
Wadansu almjirai daga Kaisariya suka bi mu. Sun zo ne tare da wani ana ce da shi Manason, mutumin Kuburus mai bi na farko, wanda za mu zauna da shi.
17 A hiki makou i Ierusalema, apo mai la na haumana ia makou me ka olioli.
Da muka isa Urushalima, 'yan'uwa suka marabce mu da farin ciki.
18 A ia la ae, hele pu aku la o Paulo me makou io Iakobo la; malaila no na lunakahiko a pau.
Washegari Bulus ya tafi tare da mu zuwa wurin Bitrus, dukan dattawa kuma suna nan.
19 Honi aku la oia ia lakou, hai pakahi aku la ia i na mea a pau a ke Akua i hana'i i ko na aina e, ma kana oihana.
Bayan ya gaishe su, sai ya shaida masu daya bayan daya abubuwan da Allah ya yi cikin al'ummai ta wurin hidimarsa.
20 A i ko lakou lohe ana, hoomaikai aku lakou i ke Akua, i mai la ia ia, E ke kaikaina, ke ike nei oe i ka nui o na umi tausani o na Indaio i manaoio; ua ikaika loa lakou a pau ma ke kanawai.
Da suka ji haka, suka yabi Ubangiji suka ce masa, “Ka gani, dan'uwa, dubban Yahudawa sun bada gaskiya suna kuma da niyyar kiyaye shari'a.
21 Ua lohe lakou nou, ua ao aku oe i na Iudaio a pau ma na aina e, e haalele i ke kanawai o Mose, a ua papa aku i ke okipoepoe ana i na keiki, aole hoi e hele ma ia aoao.
An kuma gaya masu a kanka cewa, kana koya wa Yahudawan da suke zaune cikin al'ummai su yi watsi da Musa. Kana koya masu kada su yi wa 'ya'yansu kaciya, kada kuma su bi tsofaffin al'adu.
22 Heaha la hoi? E akoakoa io mai no ka ahakanaka; no ka mea, e lohe auanei lakou i kou hiki ana mai.
Me ya kamata mu yi? Hakika za su ji ka zo.
23 Nolaila, e hana oe i keia a makou e olelo aku ai ia oe. Eia no ia makou na kanaka eha, ua hoohiki lakou.
Sabo da haka ka yi abin da muka fada maka yanzu. Muna da maza hudu da suka dauki wa'adi.
24 E lawe ae ia lakou, a e huikala ia oe iho me lakou, a e hui pu me lakou ma ka waiwai makana, i amu lakou i na poo; i ike na mea a pau, he mea ole keia mau mea a lakou i lohe ai nou; aka, ua hele pololei oe, ua malama hoi i ke kanawai.
Tafi da wadannan ka tsarkake kanka tare da su, ka dauki dukan dawainiyar su dana askin kai. Ta haka kowanne mutum zai sani abubuwan da ake fadi a kanka karya ne. Za su sani cewa kai mai kiyaye shari'a ne.
25 I ka poe manaoio no na aina e, ua palapala makou i ka mea a kakou i manao ai, aole lakou e malama i keia mau mea, eia wale no, e hookaaokoa lakou i ko na akua e, a me ke koko, a me na mea i umi wale ia, a me ka moe kolohe.
Game da al'umman da suka bada gaskiya mun yi masu wasika, mun bada umarni su kaurace kansu daga sadakokin da aka mika wa gumaku, da jini, da abin da aka makare da kuma fasikanci.
26 Alaila lawe ae la o Paulo i ua mau kanaka la, a ia la ae, huikala pu ae la kela ia ia iho me lakou, a komo aku la i ka luakini, e hoike aku i ka malama ana o na la huikala, a hiki i ka wa e haawiia'ku ai ka mohai, no kela mea keia mea o lakou.
Sai Bulus ya dauki mazannan, washegari ya tsarkake kansa tare da su, suka shiga haikali, domin ya sanar da cikar ranakun tsarkakewarsu, wato ranar ba da sadaka domin kowanne dayansu.
27 A kokoke e pau kela mau la ehiku, ike ae la ka poe Iudaio no Asia ia ia, maloko o ka luakini, hoohaunaele ae la lakou i ka lehulehu, a hopu iho la ko lakou lima ia ia,
Da kwanakin nan bakwai suka yi gab da cika, wadansu Yahudawa daga Asiya suka ga Bulus a haikali, sai suka zuga taro, suka danke shi.
28 Kahea aku la lakou, E na kanaka o ka Iseraela, e alu. Eia ke kanaka nana i ao aku i kanaka a pau mai o a o i ka mea ku e i kanaka, a me ke kanawai, a me keia wahi; a lawe mai no hoi ia i mau Helene maloko o ka luakini, a ua hoohaumia i keia wahi hemolele.
Suna ta kururuwa, “Mutanen Isra'ila ku taimaka mana. Wannan shine mutumin da ke koya wa dukan mutane ko'ina abubuwa gaba da mutane, da shari'a da kuma wannan wurin. Banda haka ya kawo Helenawa cikin haikalin nan ya kazantar da wannan wuri tsatsarka.”
29 (No ka mea, ua ike mua lakou me ia maloko o ke kulanakauhale, ia Teropima, no Epeso, kuhi iho la lakou ua kai mai o Paulo ia ia maloko o ka luakini.)
Domin dama sun ga Tarofimas mutumin Afisa tare da Bulus cikin birni, suka yi zaton ya kawo shi cikin haikali.
30 Ua pioloke ke kulanakauhale a pau, holo kiki mai la na kanaka a pau; hopu mai la lakou ia Paulo, kauo aku la lakou ia ia mawaho o ka luakini; papani koke iho la i na puka.
Sai duk gari ya rude, mutane suka runtuma suka danke Bulus. Suka ja shi waje daga cikin haikalin, nan da nan aka rufe kofofin.
31 I ko lakou imi ana e pepehi ia ia, lohe aku la ka lunatausani koa, ua haunaele o Ierusalema a pau;
Suna kokarin kashe shi kenan, sai labari ya kai wurin hafsan sojoji cewa Urushalima duk ta yamutse da tarzoma.
32 A lawe koke ae la ia i na koa, a me na lunahaneri, a holo kiki aku la io lakou la: a ike mai lakou i ua lunatausani la, a me na koa, oki ae la ko lakou pepehi ana ia Paulo.
Nan take ya dauki mayaka da jarumawa, suka sheka da gudu wurin taron. Da mutane suka ga hafsan sojoji da rundunansa sai suka daina dukan Bulus.
33 A hiki mai ua lunatausani la, hopu mai la ia ia, a kauoha aku la e paa ia i na kaulahao elua; ninau mai la, Owai keia? Heaha ka mea ana i hana'i?
Sai hafsan ya tafi ya danke Bulus ya sa aka daure shi da sarkoki biyu. Ya tambaya ko shi wanene da kuma laifinsa.
34 Uwauwa aku la kekahi i kekahi mea, a o kekahi i kekahi mea, iwaena o ka ahakanaka. Aole i hiki ia ia ke ike i ka oiaio, no ka haunaele, kauoha aku la ia, e alakai ia ia maloko o ka pakaua.
Wadansu cikin taron suna ta kururuwa wadansu su ce wannan, wadansu su ce, wancan. Tunda hafsan bai fahimci abin da suke fadi ba, sabo da ihunsu, ya dokaci a shigar da Bulus farfajiyar sojoji.
35 Aia ia iluna o na anuu, kaikaiia'ka la ia e na koa, no ka anehenehe o ua ahakanaka la.
Da suka kai matakala, sojoji suka dauki Bulus sabo da tsananin husatar taron jama'a.
36 No ka mea, hahai aku la ka ahakanaka, uwauwa aku la, E, e kai aku ia ia.
Domin taron suka biyo baya suna ihu suna cewa, “A kashe shi.”
37 A kokoke kaiia iloko o ka pakaua, i aku la o Paulo i ka lunatausani, E pono anei ia'u ke olelo aku ia oe? I mai la kela, Ua ike anei oe i ka ololo Helene?
An kusa shigar da shi farfajiyan kenan sai Bulus ya ce wa babban hafsan, “Ko ka yarda inyi magana da kai?” Hafsan ya ce, “Ka iya Helenanci?
38 Aole anei oe ka Aigupita, i ku iluna i na la mamua aku nei, a alakai ai i na kanaka eha tausani ma ka waonahele, he poe powa?
Ashe ba kai ne Bamasaren nan da kwanakin baya ka haddasa tawaye, ka dauki 'yan ta'adda dubu hudu ka kai su jeji ba?”
39 I mai la o Paulo, He kanaka Iudaio no wau, no Tareso i Kilikia, he kamaaina wau no kekahi kulanakauhale kaulana; ke nonoi aku nei au ia oe e ae mai ia'u e olelo aku i kanaka.
Bulus ya ce, “Ni Ba'ibrane ne daga birnin Tarsus a Kilikiya. Ni dan kasar babban birni ne. Ka amince mani in yi magana da mutanen.”
40 Ae mai la no kela; alaila, ku mai la o Paulo ma na anuu, peahi mai la ka lima i kanaka; hooneoneo nui iho la, olelo mai la ia ma ka olelo Hebera, i mai la,
Da hafsan ya bashi izni, Bulus ya mike a kan matakala ya daga hannayensa sama ya yi nuni su yi shuru. Da wuri ya yi tsit, Bulus ya yi masu magana da Ibraniyanci. Ya ce,