< II Samuela 17 >
1 OLELO aku la o Ahitopela ia Abesaloma, He pono na'u e wae aku ano i na kanaka he umikumamalua tausani, a e ku ae au a e hahai aku mahope o Davida i neia po.
Ahitofel ya ce wa Absalom, “Zan zaɓi mutum dubu goma sha biyu su fita a daren nan in fafari Dawuda.
2 A e loaa aku ia'u ia oi nawaliwali ia a me ke kanaka ole, a e hooweliweli aku au ia ia; a e holo aku na kanaka a pau me ia; a o ke alii wale no ka'u e pepehi aku ai.
Zan fāɗa masa sa’ad da yake cikin gajiya da karayar zuciya. Zan firgita shi, mutanen da suke tare da shi kuwa za su gudu. Sarki ne kaɗai zan kashe
3 A e hoihoi mai nei au i na kanaka a pau iou nei; o ke kanaka au e imi nei, na like ia me ka hoi hou ana mai o lakou a pau: pela e malu ai na kanaka a pau.
in dawo da dukan mutanen a gare ka. Mutuwar wanda kake nema zai zama dawowar duka; dukan mutanen ba za su cutu ba.”
4 He pono keia olelo i ka manao o Abesaloma a me na lunakahiko a pau o ka Iseraela.
Wannan shawara ta gamshi Absalom da dukan dattawan Isra’ila.
5 Alaila, i mai la o Abesaloma, E kahea aku hoi ia Husai no Areki; e lohe hoi kakou i kana olelo.
Amma Absalom ya ce, “A kira mini Hushai mutumin Arkitawan nan shi ma, mu ji abin da zai ce.”
6 A hiki mai o Husai io Abesaloma la, olelo mai la o Abesaloma ia ia, i mai la, Pela ka Ahitopela i olelo mai ai: e hana anei kakou e like me kana olelo? A i ole, e olelo mai hoi oe.
Da Hushai ya zo wurinsa, sai Absalom ya ce, “Ahitofel ya ba da wannan shawara. Mu yi abin da ya ce? In ba haka ba, sai ka ba mu ra’ayinka.”
7 I aku la o Husai ia Abesaloma, O ka oleloao a Ahitopela ana i olelo mai ai, aohe pono ia i neia manawa.
Hushai ya ce wa Absalom, “Shawarar da Ahitofel ya bayar a wannan lokaci kam, ba ta da kyau.
8 No ka mea, wahi a Husai, ua ike oe i kou makuakane a me na kanaka ona, he poe kanaka ikaika lakou, a ua ukiuki ko lakou naau me he bea la i kailiia aku kana ohana keiki ma ke kula; he kanaka kaua no hoi kou makuakane, aole ia e moe me na kanaka.
Ka san mahaifinka da mutanensa mayaƙa ne, suna cikin fushi kamar mugun beyar da aka ƙwace mata’ya’ya. Ban da haka ma, mahaifinka gogagge ne a yaƙi; ba zai kwana da rundunar ba.
9 Aia no ia ua pee ma kekahi lua, i kekahi wahi paha: a i ka haule mua ana o kekahi mau mea o lakou, e olelo auanei ka poe lohe, He lukuia iwaena o ka poe hahai ia Abesaloma;
Kai, ko yanzu ma, ya riga ya ɓuya cikin kogo ko kuma a wani wuri. In har ya fara kai wa rundunarka hari duk wanda ya ji, zai ce, ‘An yi kaca-kaca da rundunar da suka bi Absalom.’
10 A o ke koa, ka mea naau e like me ka naau o ka liona, e hehee loa ia: no ka mea, ua ike ka Iseraela a pau, he kanaka koa kou makuakane, a he poe kanaka ikaika hoi ka poe me ia.
Kai, ko jarumi mai zuciya kamar na zaki ma, zai narke don tsoro, gama dukan Isra’ila sun sani mahaifinka mayaƙi ne, sun kuma san cewa waɗanda suke tare da shi jarumawa ne.
11 Nolaila, eia kuu manao ke hai aku nei, I hoakoakoaia mai ka Iseraela a pau iou nei, mai Dana a hiki i Beeraseba, e like me ke one o ke kai ka nui loa; a e hele oe iho no i ke kaua.
“Saboda haka ina ba ka shawara, bari a tara maka dukan Isra’ila, daga Dan zuwa Beyersheba da yawansu ya yi kamar yashin bakin teku, kai kanka ka jagorance su zuwa fagen fama.
12 Pela kakou e hiki aku ai io na la i kahi e loaa aku ai ia ia, a e kau aku kakou maluna ona, e like me ka hau e kau mai maluna o ka honua: a oia, a o ka poe a pau me ia, aole loa e koe kekahi o lakou.
Sa’an nan za mu fāɗa masa duk inda yake, za mu fāɗa masa kamar yadda raɓa takan fāɗo a bisa ƙasa. Da shi da mutanensa babu ko ɗaya da za a bari da rai.
13 A ina paha ua komo aku ia iloko o kekahi kulanakauhale, alaila e lawe aku ka Iseraela a pau i na kaula i ua kulanakauhale la, a e kauo aku kakou ia wahi maloko o ka muliwai, a koe ole ma ia wahi kekahi pohaku liilii.
In ma ya janye zuwa cikin birni, sai dukan Isra’ila su kawo igiyoyi wa wannan birni, su ja shi zuwa kwari yă wargaje, yadda ba za a bar wani dutse a kan wani ba.”
14 I aku la o Abesaloma a me na kanaka a pau o ka Iseraela, ua oi aku ka pono o ka oleloao a Husai no Areki, mamua o ka oleloao a Ahitopela. No ka mea, ua manao mai o Iehova e hoolilo i ka oleloao akamai a Ahitopela i mea ole, i mea e hooili mai ai o Iehova i ka ino maluna o Abesaloma.
Absalom da dukan mutanen Isra’ila suka ce, “Shawarar Hushai mutumin Arkitawa ta fi ta Ahitofel kyau.” Gama Ubangiji ya ƙudura yă wofinta kyakkyawar shawarar Ahitofel, don yă jawo wa Absalom masifa.
15 Alaila, olelo aku la o Husai ia Zadoka laua o Abiatara na kahuna, Pela a penei i oleloao aku ai o Ahitopela ia Abesaloma a me na lunakahiko o ka Iseraela; pela a penei hoi au i oleloao aku ai.
Hushai ya ce wa Zadok da Abiyatar, firistoci, “Ahitofel ya ba wa Absalom da dattawan Isra’ila shawara su yi kaza da kaza, amma na ba su shawara su yi haka, su yi haka.
16 Nolaila, e hoouna koke aku olua e hai ia Davida, i ka i ana aku, Mai moe oe i neia po ma na papu o ka waonahele, e hele koke oe ma kela aoao, o pau loa ke alii a me na kanaka me ia i ke aleia.
Yanzu sai ku aika wa Dawuda saƙo nan da nan ku ce masa, ‘Kada ka kwana a mashigai cikin hamada; ka tabbata ka haye ba faci, in ba haka ba sarki da dukan mutanensa za su hallaka.’”
17 A ua noho o Ionatana laua o Ahimaaza ma Enerogela, no ka mea, aole pono e ikeia laua ke komo iloko o ke kulanakauhale, a hele aku la kekahi kauwawahine, a hai aku la ia laua: hele aku la hoi laua, a hai aku la i ke alii ia Davida.
Yonatan da Ahimawaz suna zaune a En Rogel. Wata baranya ce za tă je ta faɗa musu, su kuma su tafi su gaya wa Sarki Dawuda don suna tsoro kada a ga suna shiga birnin.
18 Aka, ua ike no kekahi keiki ia laua, a hai aku la ia Abesaloma: aka, hele koke aku la laua a hiki aku la i ka hale o kekahi kanaka i Bahurima, a he luawai maloko o ka pahale ona, ilaila laua i iho ai.
Amma wani saurayi ya gan su, ya gaya wa Absalom. Sai dukansu biyu suka tashi da sauri suka shiga gidan wani mutum a Bahurim. Yana da rijiya a cikin gida, sai suka shiga cikinta.
19 Lalau aku la ka wahine i ka mea uhi, hohola iho la maluna o ka waha o ka luawai, a halii iho la i ka palaoa maluna iho: a ua ike ole ia ua mea la.
Matarsa mutumin kuwa ta kawo tabarma ta shimfiɗa a bakin rijiyar, sai ta kawo hatsi ta baza a kanta. Ba kuwa wanda ya san abin da ta yi.
20 A hiki mai na kauwa a Abesaloma i ua wahine la ma ka hale, ninau mai la lakou, Auhea o Ahimaaza laua o Ionatana? I aku la ka wahine ia lakou, ua hala aku la laua ma kela aoao o ke kahawai. Imi aku la lakou, aole hoi i loaa, alaila hoi hou mai la lakou i Ierusalema.
Da mutanen Absalom suka zo wurin matan a gidan, suka ce, “Ina Yonatan da Ahimawaz?” Matar ta ce, “Tuni, sun haye rafi.” Sai mutanen suka yi ta nemansu amma ba su ga kowa, sai suka koma Urushalima.
21 A hala aku la lakou, pii mai la laua mailoko mai o ka luawai, hele aku la, a hai aku la i ke alii ia Davida. I aku la ia Davida, Eku ae, e holo koke ma kela aoao o ka wai; no ka mea, penei ka Ahitopela i olelo ku e ai ia oukou.
Bayan mutanen suka tafi, sai su biyun suka fito daga rijiyar suka je suka gaya wa Sarki Dawuda. Suka ce masa, “Maza ka ƙetare kogi; Ahitofel ya ba wa Absalom shawara a yi maka kaza da kaza.”
22 Alaila ku ae la o Davida a me na kanaka a pau me ia, a hele aku la ma kela aoao o Ioredane: a i ka wanaao, aole i koe kekahi o lakou i ka hele ole ma kela aoao o Ioredane.
Saboda haka Dawuda da dukan mutanen da suke tare da shi suka tashi suka ƙetare Urdun. Kafin wayewar gari, babu wanda ya rage da bai haye ba.
23 A ike aku la o Ahitopela, aole i hanaia e like me kana oleloao, hoee aku la ia i ka noho maluna o kona hoki, ku ae la ia, hoi hou aku la ia i kona wahi, i kona hale iho, i kona kulanakauhale, a kauoha aku la no ko ka hale ona, a kaawe iho la ia ia iho, a make; a ua kanuia oia ma ka halekupapau o kona makuakane.
Da Ahitofel ya ga ba a bi shawararsa ba, sai ya hau jakinsa ya koma gidansa a garinsu. Ya kintsa gidansa sa’an nan ya rataye kansa. Ta haka ya mutu, aka kuma binne shi a kabarin mahaifinsa.
24 Alaila hele aku la o Davida i Mahanaima: a hele aku la hoi o Abesaloma ma kela aoao o Ioredane, oia a me na kanaka a pau o ka Iseraela me ia.
Dawuda kuwa ya tafi Mahanayim. Absalom kuma ya ƙetare Urdun tare da dukan mutanen Isra’ila.
25 Hoonoho aku la o Abesaloma ia Amasa ma ko Ioaba wahi maluna o ka poe kaua: a o ua Amasa la, he keiki ia na kekahi kanaka no ka Iseraela, o Itera ka inoa, ka mea i komo aku iloko io Abigala la ke kaikamahine a Nahasa, a o ke kaikaina o Zeruia o ka makuwahine o Ioaba.
Absalom ya riga ya naɗa Amasa a kan sojoji a maimakon Yowab. Amasa kuwa ɗan wani mutum mai suna Itra ne, mutumin Ishmayel wanda ya auri Abigiyel,’yar Nahash,’yar’uwar Zeruhiya mahaifiyar Yowab.
26 Hoomoana iho la ka Iseraela me Abesaloma ma ka aina o Gileada.
Isra’ilawa da Absalom suka kafa sansani a ƙasar Gileyad.
27 A hiki aku la o Davida i Mahanaima, ilaila o Sobi ke keiki a Nahasa no Raba o na mamo a Amona, a o Makira ke keiki a Amiela no Lodebara, a o Barezilai no Rogelima ma Gileada,
Sa’ad da Dawuda ya zo Mahanayim, sai Shobi ɗan Nahash daga Rabba ta Ammonawa, da Makir ɗan Ammiyel daga Lo Debar, da Barzillai mutumin Gileyad daga Rogelim
28 Lawe mai la lakou i na moe a me na kiaha a me na ipu lepo a me na hua palaoa a me ka bale a me ka palaoa, a me ka palaoa papaa, a me ka papapa maka, a me ka pi, a me ka papapa papaa;
suka kawo wa Dawuda da mutanensa tabarmai, da kwanoni, da kayayyakin da aka yi da yumɓu. Suka kuma kawo alkama da sha’ir, da gari, da soyayyen hatsi, da wake, da waken barewa,
29 A me ka meli, a me ka bata, a mo na hipa, a me ka waiubipipaa, na Davida a na ka poe kanaka me ia e ai ai: no ka mea, olelo ae la lakou, Ua pololi na kanaka, ua luhi a me ka makewai ma ka waonahele.
da zuma, da kindirmo, da tumaki, da cukun madarar shanu wa Dawuda da mutanensa su ci. Gama sun ce, “Mutanen suna jin yunwa, sun kuma gaji, ga ƙishirwa a hamada.”