< Petero II 1 >

1 O SIMON A Petero, he kauwa a he lunaolelo na Iesu Kristo, na ka poe i loaa pu ka manao oiaio i maikai like, ma ka pono o ko kakou Akua, a me Iesu Kristo ko kakou Hoola;
Siman Bitrus, bawa da kuma manzon Yesu Kiristi, Zuwa ga waɗanda ta wurin adalcin Allahnmu da Mai Cetonmu Yesu Kiristi sun sami bangaskiya mai daraja irin tamu.
2 E nui ko oukou alohaia mai, a me ka maluhia hoi, no ka ike pono ana i ke Akua, a me Iesu, ko kakou Haku;
Alheri da salama su zama naku a yalwace ta wurin sanin Allah da Yesu Ubangijinmu.
3 E like me ka haawi ana mai o kona mana Akua i na mea a pau no kakou, e ola'i, a e haipule ai, ma ka ike ana aku i ka mea nana kakou i wae mai ma ka nani a me ka pono.
Ikonsa na Allahntaka ya ba mu kome da muke bukata don rayuwa da kuma tsoron Allah ta wurin sanin wanda ya kira mu ta wurin ɗaukakarsa da nagartarsa.
4 Malaila no ua haiia mai na mea nui loa, e pomaikai nui ai; i mea e loaa ai ia oukou kekahi ano e like me ko ke Akua, no ka mea, ua haalele oukou i ka hewa iloko o ke ao nei, ma ke kuko.
Ta wurin waɗannan ya ba mu alkawaransa masu girma da kuma masu daraja, domin ta wurinsu ku iya yin tarayya cikin Allahntakarsa, ku kuma kuɓuta daga lalatar da take cikin duniya wadda mugayen sha’awace-sha’awace suke jawowa.
5 Eia hoi kekahi, e hooikaika loa oukou, me ko oukou manaoio e kui aku ai i ka hana pono; a me ka hana pono, i ka naauao;
Saboda haka, ku yi iyakar ƙoƙari ku ƙara wa bangaskiyarku nagarta; ga nagarta kuwa, ku ƙara mata sani;
6 A me ka naauao, i ka pakiko; a me ka pakiko, i ke ahonui; a me ke ahonui, i ka haipule;
ga sani kuma ku ƙara masa kamunkai; ga kamunkai kuma ku ƙara da daurewa; ga daurewa kuwa ku ƙara da tsoron Allah;
7 A me ka haipule, i ka launa hoahanau; a me ka launa hoahanau, i ke aloha.
ga tsoron Allah kuma ku ƙara da nuna alheri ga’yan’uwa; ga nuna alheri ga’yan’uwa kuma ku ƙara da ƙauna.
8 Ina iloko o oukou keia mau mea, a i mahuahua hoi, aole oukou e lilo i poe hoopalaleha, a i poe hua ole, ma ka ike aku i ko kakou Haku ia Iesu Kristo.
Domin in kuna ƙaruwa a waɗannan halaye, za su kāre ku daga rashin tasiri da rayuwa na rashin amfani cikin saninku na Ubangijinmu Yesu Kiristi.
9 Aka, o ka mea i nele i keia mau mea, ua makapo ia, ua powehiwehi ka ike ana, a ua poina ia ia kona huikalaia ana i na hewa kahiko.
Amma in wani ba shi da su, ba shi da hangen nesa ke nan kuma makaho ne, ya kuma manta cewa an tsarkake shi daga zunubansa na dā.
10 Nolaila, ea, e na hoahanau, e hooikaika loa oukou, i hooiaioia ko oukou heaia mai, a me ko oukou kohoia ana; no ka mea, ina e hana oukou i keia mau mea, aole loa oukou e haule.
Saboda haka’yan’uwana, ku ƙara aniya wajen tabbatar da kiranku da zaɓenku da aka yi. Gama in kuka yi waɗannan abubuwa, ba za ku taɓa fāɗuwa ba,
11 Pela e hookomo lokomaikai ia'ku ai oukou iloko o ke aupuni mau loa o ko kakou Haku a Hoola hoi o Iesu Kristo. (aiōnios g166)
za ku sami kyakkyawar marabta cikin madawwamin mulkin Ubangijinmu da Mai Cetonmu Yesu Kiristi. (aiōnios g166)
12 Nolaila, aole loa au hoomolowa i ka hoeueu i ko oukou manao i keia mau mea, ua ike no nae oukou, a ua ku paa ma keia mea oiaio.
Saboda haka kullum zan tuna muku da waɗannan, ko da yake kun sansu kun kuma kahu ƙwarai cikin gaskiyar da kuke da ita yanzu.
13 Ke manao nei au, he mea pono i ko'u noho ana i keia halelewa, e hoala ia oukou me ka hoeueu aku i ka manao.
A ganina ya dace in tunashe ku muddin ina raye cikin tentin wannan jiki,
14 No ka mea, ua ike au, ua kokoke no e hemo ia'u keia halelewa o'u, e like me ka ko kakou Haku o Iesu Kristo i hoike mai ai ia'u.
domin na sani na kusa in ajiye shi a gefe, yadda Ubangijinmu Yesu Kiristi ya nuna mini a sarari.
15 Aka hoi, e hooikaika mau wau, i hiki ia oukou, ke manao mau i keia mau mea mahope o kuu make ana.
Zan kuwa yi iyakacin ƙoƙari in ga cewa bayan rabuwata kullum za ku iya tuna da waɗannan abubuwa.
16 No ka mea, aole makou i hahai mamuli o na olelo wahahee i imi akamai ia, i ko makou hoike ana aku ia oukou i ka mana, a me ka hiki ana mai o ko kakou Haku o Iesu Kristo, aka, he poe ike maka makou i kona nani.
Ba mu bi tatsuniyoyin da aka ƙaga da wayo sa’ad da muka gaya muku game da ikon Ubangijinmu Yesu Kiristi da zuwansa ba, sai dai mu shaidu ne na ɗaukakarsa mai girma da muka gani da ido.
17 No ka mea, mai ke Akua ka Makua mai, i loaa mai ai ia ia ka hoomaikai, a me ka hoonani, i ka wa i hiki mai ai ka leo io na la, mai ka nani kupanaha loa mai; Eia kuu keiki hiwahiwa, ua olioli loa au ia ia.
Gama ya sami girma da ɗaukaka daga Allah Uba sa’ad da murya ta zo masa daga Mafificiyar Ɗaukaka cewa, “Wannan Ɗana ne, wanda nake ƙauna; da shi nake jin daɗi ƙwarai.”
18 O keia leo, mai ka lani mai, oia ka makou i lohe ai, i ka wa a makou i noho pu ai me ia, ma ka mauna hoano.
Mu kanmu mun ji wannan muryar da ta zo daga sama sa’ad da muke tare da shi a kan dutse mai tsarki.
19 Eia hoi ia kakou ka na kaula olelo, i hooiaio loa ia; ua hana pono no hoi oukou i ko oukou malama ana ia mea, me he kukui la, e hoomalamalama ana i kahi pouli, a wehe mai ke alaula, a puka mai ka hokuao iloko o ko oukou mau naau;
Muna kuwa da maganar annabawa da aka ƙara tabbatar mana, zai fi kyau in kuka lura da ita, kamar hasken da yake haskakawa a wuri mai duhu, har yă zuwa wayewar gari da kuma haskakawar tauraron asubahi a zukatanku.
20 Me ka ike mua i keia, o kela wanana keia wanana o ka palapala hemolele, aole na na kaula ponoi iho ka hoike ana.
Gaba da kome dai, dole ku gane cewa babu annabcin Nassin da ya fito daga fassarar annabi da kansa.
21 No ka mea, i ka wa kahiko, aole no ka mauao o kanaka, ka na kaula; aka, ua olelo mai na kanaka hemolele o ke Akua i ka uluhia mai e ka Uhane Hemolele.
Gama annabci bai taɓa samo tushensa daga nufin mutum ba, sai dai mutane sun yi magana daga Allah yayinda Ruhu Mai Tsarki ya bishe su.

< Petero II 1 >