< Korineto II 7 >

1 NO ia hoi, e ka poe i alohaia, no ka loaa ana mai ia kakou o neia mau olelo hoopomaikai, e hoomaemae kakou ia kakou iho i na mea paumaele a pau o ke kino a me ka uhane, a hoopaa ana hoi i ka maikai ma ka makau i ke Akua.
Da yake muna da waɗannan alkawura, ya ku ƙaunatattu, sai mu tsarkake kanmu daga kowane abu da yake ƙazantar da jiki, da ruhu, mu zama da cikakken tsarki, saboda bangirma ga Allah.
2 E ike mai oukou ia makou; aole makou i hana ino aku i kekahi, aole hoi makou i hookolohe aku i kekahi, aole no hoi makou i alunu aku i ka kekahi.
Ku saki zuciya da mu. Ba mu yi wa kowa laifi ba, ba mu ɓata kowa ba, ba mu cuci kowa ba.
3 Aole au e olelo aku ia mea no ka hoohewa aku; no ka mea, ua i aku la au mamna, eia oukou iloko o ko makou naau, e make pa a e ola pu hoi.
Ba na faɗin wannan don in sa muku laifi. Na riga na gaya muku yadda muke ƙaunarku ƙwarai cikin zukatanmu, har babu abin da zai iya raba ku da ƙaunarmu, ko a mutuwa ko a rayuwa.
4 He nui ka wiwo ole o kuu olelo ana aku ia oukou, he nui hoi kuu kaena ana no oukou: na piha au i ka oluolu, na nui loa kuu olioli iloko o ko makou popilikia a pau.
Na amince da ku gaya, ina kuma taƙama da ku ƙwarai. Na ƙarfafa sosai. Duk da wahalce wahalcenmu dai ina farin ciki ƙwarai da gaske.
5 No ka mea, ia makou i hele mai ai i Makedonia, aole i loaa i ko makou kino ka maha iki, ua pilikia makou ma na aoao a pau; mawaho he hakaka, maloko he makau.
Gama sa’ad da muka zo Makidoniya, jikin nan namu bai sami hutu ba, sai ma aka matsa mana a ta kowane gefe, a waje ga rikici, a zukatanmu kuma ga tsoro.
6 Aka, o ke Akua nana e hooluolu mai i ka poe haahaa, oia ka i hooluolu mai ia makou i ka hele ana mai o Tito;
Amma Allah, wanda yakan yi wa masu ɓacin rai ta’aziyya ya yi mana ta’aziyya da zuwan Titus,
7 Aole wale no i kona hele ana mai; aka, i ka oluolu ana i hooluoluia'i e oukou, i ka hai ana mai ia makou i ko oukou iini ana, i ko oukou uwe ana, a me ko oukou manao ikaika ia'u; nolaila, na nui kuu olioli.
ba ma don zuwansa kaɗai ba, har ma a game da ƙarfafa zuciyan nan da ya samu a wurinku. Ya gaya mana yadda kuke so ku gan ni sosai, da kuma yadda kuka yi baƙin ciki game da abin da ya faru, da niyyar da kuka yi na goyon bayana. Wannan ne ya sa na ji daɗi ƙwarai.
8 Nolaila, aole au e mihi nei i kuu hana eha ana ia oukou i ka palapala; ua mihi no nae au mamua; no ka mea, ke ike nei au, he pokole wale no ko oukou eha i na palapala la.
Ko da na ɓata muku rai ta wurin wasiƙata, ba na baƙin ciki da haka. Ko da yake dā kam na yi baƙin ciki, don na lura wasiƙata ta ɓata muku rai, amma na ɗan lokaci ne kawai.
9 Ano, ke olioli nei au, aole i ko oukou hana eha ia, aka, i hana eha ia oukou e mihi ai; no ka mea, ua hana eha ia oukou ma ka ke Akua, i loaa ole ia oukou ka hewa e makou.
Duk da haka, yanzu ina farin ciki, ba don na sa ku baƙin ciki ba, sai dai domin baƙin cikinku ya kai ku ga tuba. Gama kun yi baƙin ciki kamar yadda Allah ya so, saboda haka, ba ku yi hasarar kome a sanadinmu ba.
10 No ka mea, o ka eha ana mai i ke Akua, nolaila mai ka mihi ola e mihi ole ia'i: aka, o ka eha ana o ko ke ao nei, oia ka mea e make ai.
Baƙin ciki irin na tsoron Allah yana kai ga tuban da yake kawo ceto, ba ya kuma kawo baƙin ciki, amma baƙin ciki irin na duniya yakan kawo mutuwa.
11 Aia hoi, o na mea la a oukou i hana eha ia'i ma ka ke Akua, he nui ka ikaika i hanaia e ia iloko o oukou, oia, he hoakaka, oia, he huhu, oia, he makau, oia, he iini nui, oia, he manao ikaika, oia, he hoopai! ma na mea a pau, ua hoike mai oukou ia oukou iho, he hala ole i keia mea.
Ku dubi abin da wannan baƙin ciki irin na tsoron Allah ya kawo muku mana, ya sa ku marmarin aikatawa, da nuna cewa kun yi kuskure, ya sa kuka yi fushi, kuka kuma ji tsoro, ya sa kuka sa zuciya, kuka kuma sa aniya, ya sa kuna a shirye ku ga an yi horon da ya dace. Game da wannan sha’ani kam, lalle ta kowace hanya kun nuna cewa ba ku da laifi.
12 No ia hoi, aole au i palapala aku ia oukou no ka mea nana ka hana hewa ana'ku, aole hoi no ka mea i hana hewa ia'ku, aka, i akaka ia oukou ko makou malama ana ku ia oukou imua o ke Akua.
To, ko da yake na rubuta muku, ba musamman a kan wanda ya yi laifin ba ne, ba kuwa a kan wanda aka cutar ba, sai dai domin a bayyana muku a gaban Allah tsananin kula da kuke yi mana.
13 No ia mea, ua hooluoluia mai makou i ko oukou oluolu ana: a ua oi aku ko makou olioli no ka olioli ana o Tito, no ka mea, ua hoomahaia kona naau e oukou a pau.
Ta wurin wannan duka, muka sami ƙarfafawa. Ban da ƙarfafawar da muka samu, mun ji daɗi ƙwarai saboda yadda muka ga farin cikin Titus, domin ruhunsa ya sami wartsakewa daga gare ku duka.
14 No ia mea, ina au i kaena aku ia ia i kekahi mea no oukou, aole o'u hilahila; aka, me makou i olelo aku ai i na mea a pau ia oukou ma ka oiaio, pela hoi ko makou kaena ana imua o Tito, ua ikeia he oiaio.
Na yi taƙama da ku a wurinsa, ba ku kuwa ba ni kunya ba. Kamar dai yadda dukan abin da muka gaya muku gaskiya ne, haka ma taƙamarmu a kanku a gaban Titus ya zama gaskiya.
15 A ua mahuahua aku konaaloha ia oukou i kona hoomanao ana i ka hoolohe o oukou a pau, i ko oukou hookipa ana ia ia me ka makau a me ka haalulu.
Ƙaunar da yake yi muku ya ƙaru ƙwarai, duk sa’ad da yake tunawa da biyayyarku duka, da kuma irin yawan bangirman da kuka nuna masa lokacin da kuka karɓe shi.
16 He hauoli ko'u, no ka mea, ke manao pono nei au ia oukou ma na mea a pau.
Ina farin ciki ne don na amince da ku ƙwarai da gaske.

< Korineto II 7 >