< II Oihanaalii 8 >
1 A PAU na makahiki he iwakalua, ka wa a Solomona i ku kulu ai ka hale o Iehova, a me kona hale iho,
A ƙarshen shekaru ashirin, a lokacin da Solomon ya gina haikalin Ubangiji da nasa fadan,
2 Alaila, o na kulanakauhale a Hurama i haawi mai ai ia Solomona, kukulu iho la o Solomona ia lakou, a hoonoho malaila i ka Iseraela.
Solomon ya sāke gina ƙauyukan da Hiram ya ba shi, ya kuma zaunar da Isra’ilawa a cikinsu.
3 Hele aku la o Solomona i Hamata-zoba, a lanakila maluna ona.
Sa’an nan Solomon ya tafi Hamat-Zoba ya ci ta da yaƙi.
4 Kukulu iho la oia ia Tademora ma ka waonahele, a me na kulanakauhale papaa ana i kukulu ai ma Hamata.
Ya kuma gina Tadmor a hamada da kuma dukan biranen ajiyar da ya gina a Hamat.
5 Kukulu hoi oia ia Betehorana luna, a me Betehorana lalo, na kulanakauhale paa i ka pa, a me na puka a me na kaola;
Ya sāke gina Bet-Horon na Bisa da kuma Bet-Horon na Ƙasa a matsayin birane masu katanga, da bangaye da ƙofofi da kuma ƙyamare,
6 A me Baalata a me na kulanakauhale papaa o Solomona, a me na kulanakauhalo no na kaa, a me na kulanakauhale no ka poe holoholo lio, a me na mea a pau a Solomona i makemake ai e kukulu ma Ierusalema, a ma Lebanona, a ma ka aina a pau o kona aupuni.
haka kuma Ba’alat da dukan biranen ajiyarsa, da kuma dukan birane domin keken yaƙinsa da dawakansa, duk abin da ya so yă gina a Urushalima, a Lebanon da kuma dukan yankin da ya yi mulki, ya gina shi.
7 A o na kanaka i koe no ka Heta, a me ka Amora, a me ka Periza, a me ka Hiva, a me ka Iebusa, aole no ka poe mamo a Iseraela,
Dukan mutanen da suka rage daga Hittiyawa, Amoriyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa (waɗannan mutane ba Isra’ilawa ba ne),
8 O na mamo o ka poe i koe ma ka aina, ka poe i pau ole i ka Iseraela, hoolilo o Solomona ia lakou i poe hookupu nana, a hiki i keia la.
wato, zuriyarsu da suka ragu a ƙasar, wadda Isra’ilawa ba su hallaka ba, waɗannan ne Solomon ya mai da su bayinsa na aikin dole, kamar yadda yake har wa yau.
9 Aka, o ka poe mamo a Iseraela, aole i hoolilo o Solomona i kekahi poe o lakou i poe kauwa no kana hana; no ka mea, he poe kanaka kaua lakou, ho poe luna koa, a he poe luna o na hale kaa a me na holoholo lio.
Amma Solomon bai mai da Isra’ilawa bayi don aikinsa ba; su ne mayaƙansa, shugabannin hafsoshinsa, da shugabannin keken yaƙinsa da kuma mahayan keken yaƙinsa.
10 Eia ka poe koikoi o na luna a ke alii a Solomona; elua haneri a me kanalima, ka poe i hoonohoia maluna o na kanaka.
Su ne kuma manyan ma’aikatan Sarki Solomon, manyan mutane ɗari biyu da hamsin masu lura da mutane.
11 A alakai o Solomona i ke kaikamahine a Parao mai ke kulanakauhale o Davida mai a i ka hale ana i kukulu ai nona; no ka mea, olelo iho la oia, Aole e noho ka'u wahine ma ka hale o Davida, ke alii o ka Iseraela, no ka mea, ua laa ia mau wahi, kahi i komo ai ka pahu o Iehova.
Solomon ya kawo’yar Fir’auna daga Birnin Dawuda zuwa fadan da ya gina mata, gama ya ce, “Matata ba za tă zauna a fadan Dawuda sarkin Isra’ila ba, domin wuraren da akwatin alkawarin Ubangiji ya shiga masu tsarki ne.”
12 Alaila, mohai aku la o Solomona i na mohai ia Iehova maluna o ke kuahu o Iehova, ka mea ana i kukulu ai imua o ka lanai;
A kan bagaden Ubangiji da ya gina a gaban shirayi, Solomon ya miƙa hadayun ƙonawa ga Ubangiji,
13 E mohai aku ana i kela la i keia la i ka mea i hoomaopopola'i, a e like hoi me ke kanawai o Mose no na Sabati, a me na mahina hou, a no na ahaaina maikai, ekolu manawa i kela makahiki i keia maka hiki, i ka ahaaina berena hu ole, ka ahaaina hebedoma, a me ka ahaaina kauhalelewa.
bisa ga bukace-bukace na kullum don hadayun da Musa ya umarta don Asabbatai, Sabon Wata da kuma bukukkuwa uku na shekara, Bikin Burodi Marar Yisti, Bikin Makoni da Bikin Tabanakul.
14 Mamuli o ka manao o Davi da kona makua, hoonoho papa iho la oia i ka poe kahuna e like me ka lakou hana ana, a i na Levi hoi ia a ka lakou oihana e hoolea aku, a e lawelawe imua o ka poe kahuna, e like me ka hana o kela la keia la, a hoonoho papa no hoi i ka poe kiai puka ma kela ipuka keia ipuka, no ka mea, pela ke kauoha a Davida ke kanaka o ke Akua.
Bisa ga farillar mahaifinsa Dawuda, ya naɗa ɓangarori na firistoci don ayyukansu da Lawiyawa don su jagoranci yabo su kuma taimaki firistoci bisa ga bukace-bukacen kowace rana. Ya kuma naɗa matsara ƙofofi ɓangarori, ɓangarori don ƙofofi dabam-dabam domin abin da Dawuda mutumin Allah ya umarta ke nan.
15 Aole i paleia'e ke kanawai o ke alii i ka poe kahuna, a me na Levi ma kekahi mea, aole hoi ma na waihonawaiwai.
Ba a kuwa yi rashin biyayya ba game da abin da sarki ya umarta game da firistoci ko Lawiyawa a kan kayan haikalin ba.
16 A ua hoomakaukauia ka hana a pau a Solomona, a hiki i ka la o ka hookumu ana i ka hale o Iehova, a i kona paa ana no hoi; pela i paa ai ka hale o Iehova.
An yi dukan ayyukan Solomon, daga ranar kafa tushen haikalin Ubangiji har gamawarsa. Ta haka aka gama haikalin Ubangiji.
17 Alaila, hele o Solomona i Eziona-gebera, a i Elota ma kahakai i ka aina o Edoma.
Sa’an nan Solomon ya tafi Eziyon Geber da Elot a bakin tekun Edom.
18 A haawi mai la o Hurama ia Solomona ma na lima o kana poe kauwa, i na moku a me na kauwa ike i ke kai; a hele pu lakou me na kauwa a Solomona i Opira, a lawe mailaila mai i eha haneri a me kanalima talena gula, a hali mai la io Solomona la i ke alii.
Sai Hiram ya aika masa jiragen ruwan da masu tuƙinsu waɗanda suka san teku sosai. Ma’aikatan Hiram suka tafi da na Solomon zuwa Ofir suka dawo da talentin zinariya ɗari huɗu da hamsin wa Sarki Solomon.