< II Oihanaalii 20 >

1 A MAHOPE iho o keia mau mea, hiki mai la ka Moaba, a me ka Amona, a me lakou pu kekahi poe e ae, aole no ka Amona, e kaua mai ia Iehosapata.
Bayan wannan, Mowabawa da Ammonawa tare da waɗansu Meyunawa suka zo su yaƙi Yehoshafat.
2 Hele mai la kekahi poe a hai mai ia Iehosapata, i mai la, E hiki mai ana i ou la he poe nui, mai kela aoao mai o ke kai mai Suria mai; aia hoi lakou ma Hazezona-tamara, oia o Enegedi.
Sai waɗansu mutane suka zo suka faɗa wa Yehoshafat, “Ga babban runduna tana zuwa a kanka daga Edom, daga ƙetaren Teku, daga Aram. Ta ma kai Hazazon Tamar” (wato, En Gedi).
3 A makau iho la o Iehosapata, a halalo iho la kona maka e imi ia Iehova, a kukala aku la i la hookeai ma Iuda a pau loa.
A firgice, Yehoshafat ya yanke shawara yă nemi nufin Ubangiji, ya kuma yi shelar azumi a dukan Yahuda.
4 A hoakoakoa mai la ka Iuda e imi ia Iehova; noloko mai o na kulanakauhale a pau o Iuda i hele mai ai lakou e imi ia Iehova.
Mutanen Yahuda suka taru gaba ɗaya don su nemi taimako daga wurin Ubangiji, tabbatacce suka fito daga kowane garin Yahuda don su neme shi.
5 Alaila, ku iluna o Iehosapata iloko o ka ahakanaka o Iuda a me Ierusalema, iloko o ka hale o Iehova imua o ka pahale hou;
Sa’an nan Yehoshafat ya miƙe tsaye a taron Yahuda da Urushalima a haikalin Ubangiji a sabon filin
6 Olelo aku la, E Iehova ke Akua o ko makou poe kupuna, aole anei oe ke Akua o ka lani? aole anei oe e noho alii ana maluna o na aupuni a pau o na lahuikanaka, a iloko hoi o kou lima ka mana, a me ka ikaika, i hiki ole i kekahi ke ku e ia oe?
ya ce, “Ya Ubangiji Allah na kakanninmu, ba kai ne Allah wanda yake sama ba? Kana mulki a bisa dukan mulkokin ƙasashe. Iko da girma suna a hannunka, kuma ba wanda zai iya tsayayya da kai.
7 Aole anei oe ko makou Akua, ka mea nana i kipaku i ko keia aina imua o kou poe kanaka o ka Iseraela, a haawi ia mea i ka poe mamo a Aberahama kou mea i aloha ai, i mea mau loa.
Ya Allahnmu, ba kai ba ne ka kore mazaunan wannan ƙasa a gaban mutanenka Isra’ila ka kuma ba da ita har abada ga zuriyar Ibrahim abokinka?
8 A noho lakou malaila, a kukulu lakou no kou inoa i luakini, me ka i ana aku,
Sun yi zama a cikinta suka kuma yi gina wuri mai tsarki a cikinta domin Sunanka cewa,
9 I ka hiki ana mai o ka mea ino maluna o makou, o ka pahi kaua, o ka hoopaiia mai, o ke ahulau, a o ka wi, a ku makou imua o keia hale, a imua ou, (no ka mea, aia iloko o keia hale kou inoa, ) a kahea aku ia oe i ko makou wa pilikia, alaila e hoolohe mai oe, a e hoola.
‘In masifa ta zo mana, ko takobin hukunci, ko annoba ko yunwa, za mu tsaya a gabanka a gaban wannan haikalin da yake ɗauke da Sunanka, mu kuma yi kuka gare ka cikin azaba, za ka kuwa ji mu, ka cece mu.’
10 Ano, eia hoi ka Amona, a me ka Moaba, a me ko ka mauna o Seira, ka poe au i haawi ole ai i ka Iseraela e hele io lakou la, i ko lakou hele ana mai ka aina o Aigupita mai, no ia mea, huli lakou mai o lakou aku, aole i luku ia lakou.
“Yanzu kuma ga mutanen Ammon, da na Mowab, da na Dutsen Seyir, waɗanda ka hana Isra’ilawa su kai musu yaƙi sa’ad da suka fito daga ƙasar Masar, su ne mutanen da Isra’ila suka ƙyale, ba su hallaka su ba.
11 Eia hoi ko lakou uku ana mai ia makou, hele mai lakou e kipaku mai ia makou mai ko makou ainahooili aku, ka mea au i haawi mai ai ia makou.
Yau ga yadda suke so su biya mu. Su suke so su kore mu daga ƙasar da ka ba mu gādo.
12 E ko makou Akua e, aole anei oe e hoopai ia lakou? no ka mea, aole o makou mana imua o keia poe nui, ka poe i hele ku e mai ia makou; aole makou i ike i ka mea e pono ai makou ke hana, aka, ia oe ko makou mau maka.
Ya Allahnmu, ba za ka hukunta su ba? Gama ba mu da ƙarfin fuskantar wannan babbar rundunar da take so ta yaƙe mu. Ba mu san abin da za mu yi ba, mu dai mun zuba maka ido.”
13 A ku imua o Iehova ka Iuda a pau loa, me ko lakou poe uuku, a me ka lakou poe wahine, a me ka lakou poe kamalii.
Dukan mazan Yahuda, tare da matansu da yaransu da ƙananansu, suka tsaya a gaban Ubangiji.
14 Alaila, i ke ku ana o Iahaziela iwaena o ka ahakanaka, kau mai la ka Uhane o Iehova maluna ona, oia ke keiki a Zekaria, ke keiki a Benaia, ke keiki a Matanaia ka Levi, no ka poe mamo a Asapa.
Sa’an nan Ruhun Ubangiji ya sauko a kan Yahaziyel ɗan Zakariya, ɗan Benahiya, ɗan Yehiyel, ɗan Mattaniya, wani Balawe kuma zuriyar Asaf, yayinda yake tsaye a cikin taron.
15 Olelo mai la oia, E hoolohe oukou, e ka Iuda a pau, a me ko Ierusalema, a o oe kekahi, e ke alii, e Iehosapata, penei i olelo mai ai o Iehova, Mai makau oukou, aole hopohopo imua o keia poe nui; no ka mea, aole ia oukou ke kaua. i ke Akua no.
Ya ce, “Saurara, Sarki Yehoshafat da dukan waɗanda suke zama a Yahuda da Urushalima! Ga abin da Ubangiji ya ce muku, ‘Kada ku ji tsoro ko ku fid da zuciya saboda wannan babbar runduna. Gama yaƙin ba naku ba ne, amma na Allah.
16 I ka la apopo e iho ku e oukou io lakou la, aia hoi lakou e pii mai ana i ka pali o Ziza; a e loaa lakou ia oukou ma ke kapa o ke kahawai imua o ka waonahele o Ieruela.
Gobe ku fito ku gangara ku yaƙe su. Za su yi ta haurawa ta Mashigin Ziz, ku kuwa za ku same su a ƙarshen kwari a Hamadan Yeruwel.
17 Aole oukou e kaua i keia manawa, e hoomakaukau oukou, e ku malie, a e nana i ko Iehova hoola ana mai ia oukou, e ka Iuda, a me ko Ierusalema; mai makau oukou, mai hopohopo; i ka la apopo, e hele ku e aku oukou io lakou la. O Iehova pu kekahi me oukou.
Ba lalle ba ne ku yi wannan yaƙi. Ku dai, ku ja dāgā, ku tsaya kurum ku ga nasarar da Ubangiji zai ba ku, ya Yahuda da Urushalima. Kada ku ji tsoro; kada ku karai. Ku fito don ku fuskance su gobe, Ubangiji kuwa zai kasance tare ku.’”
18 Alaila, kulou iho la o Iehosapata ilalo kona maka i ka honua; a o ka Iuda a pau, a me ko Ierusalema, haule iho la lakou ilalo imua o Iehova, e hoomana aku ia Iehova.
Yehoshafat ya rusuna da fuskarsa har ƙasa, dukan mutanen Yahuda da Urushalima suka fāɗi rubda ciki suka yi sujada a gaban Ubangiji.
19 Ku iluna na Levi, no na Kohata, a me na Kora, o hoolea aku ia Iehova ke Akua o ka Iseraela me ka leo kiekie.
Sa’an nan waɗansu Lawiyawa daga Kohatawa da Korayawa suka tashi tsaye suka yabe Ubangiji, Allah na Isra’ila, da babbar murya sosai.
20 Ala lakou i ke kakahiaka nui, a hele lakou i ka waonahele o Tekoa; a i ko lakou bele ana aku, ku iluna o Iehosapata, olelo aku la, E hoolohe mai ia'u e ka Iuda, a me ko Ierusalema; e manaoio ia Iehova i ko oukou Akua, i hookupaaia oukou; e manaoio i kana poe kaula, i lanakila oukou.
Da sassafe suka tashi suka nufi Hamadan Tekowa. Yayinda suka kama hanya, Yehoshafat ya tsaya ya ce, “Ku saurare ni, Yahuda da mutanen Urushalima! Ku amince da Ubangiji Allahnku za a kuwa kafa ku; ku amince da annabawansa za ku kuwa yi nasara.”
21 A kukakuka pu oia me na kanaka, a hoonoho oia i kekahi poe hoolea mele ia Iehova o hoomaikai aku i ka nani o kona hemolele, i ko lakou hele ana imua o ka poe kaua, i ka i ana aku, E hoolea aku ia Iehova; no ka mea, ua mau loa kona aloha.
Bayan suka yi shawara tare da shugabanni, sai ya zaɓi mutanen da za su ja gaban sojoji suna waƙa ga Ubangiji suna yabonsa saboda tsarkinsa suna cewa, “Ku yi godiya ga Ubangiji, gama ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.”
22 A i ka wa o ko lakou hoolea ana, a hoomaikai aku, hoonoho iho la o Iehova i poe hoohalua mahope o na mamo a Amona, a me Moaba, a me ko ka mauna o Seira, i ko lakou hele ku e ana ia Iuda; a ua lukuia lakou.
Da suka fara waƙa, suna kuma yabo, sai Ubangiji ya kai hari a kan mutanen Ammon da Mowab da Dutsen Seyir, waɗanda suka kawo hari a Yahuda, aka kuwa ci su da yaƙi.
23 O ka poe mamo a Amona a me ka Moaba, ku e lakou i ko ka mauna o Seira, a luku, a pepehi ia lakou a pau loa, a hoopau lakou i ko Seira; alaila, mokuahana iho la lakou, a pepehi lakou i kekahi i kekahi.
Mutanen Ammon da Mowab suka tasar wa mazaunan Dutsen Seyir, suka hallaka su ƙaƙaf. Sa’ad da suka karkashe mazaunan Seyir sai suka fāɗa wa juna, suka yi ta hallaka juna.
24 A hiki ka Iuda i ka halekiai ma ka waonahele, nana aku la i ka lehulehu, aia hoi, na heana o ka poe i haule i ka honua, aole wahi mea pakele.
Sa’ad da mutanen Yahuda suka zo wurin da yake fuskantar hamada, suka duba ta wajen babban rundunar, sai suka ga gawawwaki birjik a ƙasa; babu wani wanda ya kuɓuta.
25 A hiki o Iehosapata a me kona poe kanaka e lawe aku i ka waiwai pio, ua loaa ia lakou ka waiwai nui loa ma ka ili o na heana, a me na mea maikai loa, a ua hao iho la lakou ia mau mea no lakou iho, aole pau i ka haliia; a ekolu la o ko lakou hali ana i ka waiwai pio, no ka mea, ua nui loa ia.
Sa’ad da Yehoshafat da jama’arsa suka je kwasar ganima, sai suka sami shanu masu yawan gaske, da kayayyaki, da tufafi, da abubuwa masu daraja, waɗanda suka yi ta kwasa har suka gaji. Kwana uku suka yi suna kwasar ganimar saboda yawanta.
26 A i ka po aha, hoakoakoaia lakou ma ke awawa o Beraka; no ka mea, malaila lakou i hoomaikai aku ai ia Iehova; no ia mea, ua kapaia ka inoa o ia wahi, o ke awawa o I Beraka a hiki i keia la.
A rana ta huɗu sai suka taru a Kwarin Beraka, inda suka yabi Ubangiji. Wannan ne ya sa ake kiransa Kwarin Beraka har wa yau.
27 Alaila, hoi ka Iuda a pau a me ko Ierusalema, a o Iehosapata ka mea mamua, i ka hoi ana i Ierusalema, me ka olioli; no ka mea, ua hoohauoli o Iehova ia lakou maluna o ko lakou poe enemi.
Sa’an nan Yehoshafat ya jagoranci dukan mutanen Yahuda da Urushalima suka dawo da farin ciki zuwa Urushalima, gama Ubangiji ya ba su dalilin farin ciki a kan abokan gābansu.
28 A hoi mai lakou i Ierusalema me na mea kani, a me na mea ukeke, a me na pu, i ka hale o Iehova.
Suka shiga Urushalima suka shiga haikalin Ubangiji da kiɗin molaye da sarewa da kuma garayu.
29 A kau mai ka weliweli i ke Akua maluna o na aupuni o ka honua, i ko lakou lohe ana, ua kaua aku o Iehova i ka poe enemi o ka Iseraela.
Tsoron Allah ya kama dukan mulkokin ƙasashe sa’ad da suka ji yadda Ubangiji ya yi yaƙi a kan abokan gāban Isra’ila.
30 A ua maluhia ke aupuni o Iehosapata, a ua hoomalu mai kona Akua ia ia a puni.
Mulkin Yehoshafat kuwa ya zauna lafiya, gama Allahnsa ya ba shi hutu a kowane gefe.
31 A noho alii o Iehosapata maluna o ka Iuda. He kanakolukumamalima makahiki kona i kona hoomaka ana e noho alii, a noho alii ia i na makahiki he iwakaluakumamalima, a o ka inoa o kona makuwahine, o Azuba, ke kaikamahine a Silehi.
Ta haka Yehoshafat ya yi mulki a bisa Yahuda. Yana da shekara talatin da biyar sa’ad da ya zama sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da biyar. Sunan mahaifiyarsa Azuba ce,’yar Shilhi.
32 A hele ia ma ka aoao o kona makuakane o Asa, aole i huli mai ia aoao aku; ua hana oia i na mea pololei i na maka o Iehova.
Ya yi tafiya a hanyoyin mahaifinsa Asa bai kuwa kauce daga gare su ba; ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji.
33 Aka, aole i hoohioloia na wahi kiekie: aole hoomakaukau na kanaka i ko lakou mau naau no ke Akua o ko lakou poe kupuna.
Duk da haka ba a kawar da masujadai kan tudu ba, domin har yanzu mutanen ba su tsayar da zukatansu ga Allahn kakanninsu ba.
34 A o ke koena o na hana a Iehosapata, na mea mua, a me na mea hope, aia hoi, ua kakauia iloko o ka buke a Iehu ko keiki a Henani, ka mea i oleloia'i iloko o ka buke o na'lii o ka Iseraela.
Sauran ayyukan mulkin Yehoshafat, daga farko zuwa ƙarshe, an rubuta su a tarihin Yehu ɗan Hanani, waɗanda aka rubuta a littafin sarakunan Isra’ila.
35 A mahope aku, hui pu o Iehosapata ke alii o Iuda me Ahazia, ko alii o ka Iseraela, ka mea i hana hewa.
Daga baya, Yehoshafat sarkin Yahuda ya haɗa kai da Ahaziya sarkin Isra’ila, wanda yake da laifin mugunta.
36 Huipu oia me ia e hana i mau moku e holo i Taresa. A hana no laua i mau moku ma Eziona-gebera.
Ya yarda da shi su gina jiragen ruwan kasuwanci. Bayan aka gina waɗannan a Eziyon Geber,
37 Alaila, wanana mai la o Eliezera ke keiki a Dodava no Maresa, ia Iehosapata, i mai la, I kou huipu ana me Ahazia, e wawahi auanei o Iehova i ka mea au i hana'i. A naha iho la na moku, aole i hiki ia lakou ke holo i Taresa.
Eliyezer ɗan Dodabahu na Maresha ya yi annabci a kan Yehoshafat cewa, “Domin ka haɗa kai da Ahaziya, Ubangiji zai hallaka abin da ka yi.” Jiragen ruwan kuwa suka farfashe, ba a kuwa iya sa su je kasuwanci ba.

< II Oihanaalii 20 >