< I Na Lii 4 >

1 PELA i alii ai o Solomona maluna o ka Iseraela a pau.
Sai Sarki Solomon ya yi mulki a bisa dukan Isra’ila.
2 Eia hoi kona mau luna, o Azaria ke keiki a Zadoka ke kahuna.
Waɗannan su ne manyan shugabanninsa. Azariya ɗan Zadok shi ne firist;
3 O Elihorepa a me Ahia na keiki a Sisa he mau kakauolelo; o Iehosapata ke keiki a Alihuda, ke kakauhana.
Elihoref da Ahiya,’ya’yan Shisha maza, su ne marubuta. Yehoshafat ɗan Ahilud, shi ne mai lura da takardu.
4 A o Benaia ke keiki a Iehoiada, maluna o ka poe koa; a Zadoka a me Abiatara he mau kahuna pule laua.
Benahiya ɗan Yehohiyada, shi ne shugaban mayaƙa. Zadok da Abiyatar, su ne firistoci.
5 A o Azaria ke keiki a Natana maluna o na luna; a o Zabuda ke keiki a Natana, kekahi luna punahele a ke alii.
Azariya ɗan Natan, shi ne mai lura da shugabannin yanki. Zabud ɗan Natan, shi ne firist da kuma mai wa sarki shawara.
6 A o Ahisara maluna o ka hale; o Adonirama ke keiki a Abeda maluna o ka waiwai hookupu.
Ahishar, shi ne sarkin fada. Adoniram ɗan Abda, shi ne mai lura da aikin gandu.
7 A ia Solomona na luna he umikumamalua maluna o ka Iseraela a pau, na mea hoomakaukau i ka ai na ke alii a na ko kona hale, kela kanaka keia kanaka i kona malama o ka makahiki i hoomakaukau ai.
Solomon yana da gwamnoni yankuna goma sha biyu a bisa dukan Isra’ila, waɗanda suke tanaji abinci domin sarki da kuma gidan sarauta. Kowanne yakan tanada abinci na wata ɗaya a shekara.
8 Eia ko lakou mau inoa, o Benehura ma ka mauna o Eperaima;
Ga sunayensu, Ben-Hur, shi ne a ƙasar tudun Efraim;
9 O Benedekera, ma Makaza, a me Salabima, a me Betesemeta, a me Elonabetehanana.
Ben-Deker, shi ne a Makaz, Sha’albim, Bet-Shemesh da Elon Bet-Hanan;
10 O Beneheseda ma Anibota, ia ia o Soko, a me ka aina a pau o Hepera.
Ben-Hesed, shi ne a Arubbot (Soko da dukan ƙasar Hefer);
11 O Benabinadaba ma ka aina a pau o Dora, ia ia o Tapata ke kaikamahine a Solomona i wahine.
Ben-Abinadab, shi ne a Nafot Dor (ya auri Tafat’yar Solomon);
12 A o Baana ke keiki a Ahiluda, ia ia Taanaka, a me Megido, a me Beteseana a pau, e pili ana i Zaretana, malalo o Iezereela, mai Beteseana aku a hiki i Abelamahola a ma o aku o Iokeneama.
Ba’ana ɗan Ahilud, shi ne a Ta’anak da Megiddo, da kuma dukan Bet-Sheyan biye da Zaretan ƙasa da Yezireyel, daga Bet-Sheyan zuwa Abel-Mehola a ƙetaren Yokmeyam;
13 A o Benegebera ma Ramota Gileada, ia ia na kauhale o Iaira ke keiki a Manase na wahi ma Gileada; ia ia hoi ka aina o Aregoba kahi ma Basana, he kanaono na kulanakauhale nui me na pa, a me na kaola keleawe:
Ben-Geber, shi ne a Ramot Gileyad (Mazaunan Yayir ɗan Manasse a Gileyad suna a ƙarƙashinsa, haka ma yankin Argob a Bashan tare da manyan biranen sittin masu katanga da suke da ƙyamare na tagulla);
14 A o Ahinadaba ke keiki a Ido, ia ia Mahanaima:
Ahinadab ɗan Iddo, shi ne a Mahanayim;
15 Ahimiaza ma Napetali; ua lawe hoi oia ia Basemata, ke kaikamahine a Solomona i wahine;
Ahimawaz, shi ne a Naftali (ya auri Basemat’yar Solomon);
16 A o Baana ke keiki a Husai ma Asera a me Alota;
Ba’ana ɗan Hushai, shi ne a Asher da Bayelot;
17 O Iehosapata ke keiki a Parua ma Isakara;
Yehoshafat ɗan Faruwa, shi ne a Issakar;
18 O Simei ke keiki a Ela ma Beniamina;
Shimeyi ɗan Ela, shi ne a Benyamin;
19 O Gebera ke keiki a Uri ma ka aina o Gileada, ka aina o Sihona ke alii o ka Amora, a me Oga ke alii o Basana; oia wale no ka luna ma kela aina.
Geber ɗan Uri, shi ne a Gileyad (ƙasar Sihon sarkin Amoriyawa da kuma Og sarkin Bashan). Shi ne kaɗai gwamna a bisa yankin.
20 He lehulehu ka Iuda, a me ka Iseraela, e like me ka one ma kahakai i ka nui, e ai ana, a e inu ana, a e hoolealea ana.
Mutanen Yahuda da na Isra’ila sun yi yawa sai ka ce yashi a bakin teku. Suka ci, suka sha, suka kuma yi farin ciki.
21 A ua alii ae la o Solomona maluna o na aupuni a pau mai ka muliwai a hiki i ka aina o ko Pilisetia, a i ka mokuna o Aigupita; a lawe mai la i na makana, a malama lakou ia Solomona i na la a pau o kona ola ana.
Solomon kuwa ya yi mulki a bisa dukan masarautai daga Kogi zuwa ƙasar Filistiyawa, har zuwa iyakar Masar. Waɗannan ƙasashe sun yi ta kawo haraji, suka kuma zama bayin Solomon dukan kwanakin ransa.
22 A o ka ai na Solomona i ka la hookahi, he kanakolu kora palaoa maikai, a me na kora huita wali he kanaono:
Tanajin Solomon na kowace rana su ne, garwa talatin na garin abinci,
23 O na bipikauo kupaluia he umi, a me na bipikauo mai ke kula mai he iwakalua, a me na hipa hookahi haneri, a okoa hoi na dia, a me na anetelopa, a me na bufalo, a me na manu momona.
shanun da aka yi kiwo a gida guda goma, shanu ashirin da suka ƙoshi daga kiwo, tumaki da awaki ɗari; ban da ƙishimai, bareyi, batsiyoyi, da kaji masu ƙiba.
24 No ka mea, ia ia ke aupuni ma keia aoao a pau o ka muliwai, mai Tipesa a hiki i Aza, maluna oia o nalii a pau ma keia aoao o ka muliwai: a he malu kona ma na aoao a puni ia.
Gama ya yi mulki a bisa dukan masarautai yamma da Kogi, daga Tifsa zuwa Gaza, aka kuwa sami zaman lafiya a kowane gefe.
25 Noho maluhia ae la o ka Iuda a me ka Iseraela, kela kanaka keia kanaka, malalo o kona kumuwaina iho a malalo o kona laaufiku iho, mai Dana a Bereseba, i na la a pau o Solomona.
A kwanakin da Solomon yake raye, Yahuda da Isra’ila, daga Dan zuwa Beyersheba, sun zauna lafiya, kowane mutum ya zauna a ƙarƙashin itacen inabi da na ɓaurensa.
26 Ia Solomona na wahi e ku ai na lio, he kanaha tausani, no kona mau kaa, a me na kanaka hololio he umikumamalua haneri.
Solomon yana da rumfunan dawakai masu jan kekunan yaƙi, dubu huɗu, da kuma dawakai dubu goma sha biyu
27 A ua hoomakaukau kela mau luna i ai na Solomona ke alii, a na ka poe a pau i hele mai i ka papaaina o Solomona ke alii, kela kanaka keia kanaka i kona malama, aole nele iki lakou.
Shugabannin yankuna, kowanne a watansa yakan yi tanajin abinci domin Sarki Solomon da kuma duk wanda ya zo teburin sarki. Sun tabbatar ba a rasa kome ba.
28 Ka hua bale hoi a me ka mauu na na lio, me na lio holo, ka lakou i lawe mai ai i kahi o lakou, kela kanaka keia kanaka e like me kana kauoha.
Kowa a cikinsu, bisa ga lokacin da aka ba shi, yakan kai hatsin sha’ir da ciyawa domin dawakan-kekunan yaƙi, da sauran dawakai a inda aka ajiye su.
29 A haawi mai la ke Akua i ke akamai ia Solomona, a me ka naauao he nui loa, a me ka nui ana o ka naau, e like me ka one ma kahakai.
Allah ya ba Solomon hikima da hangen nesa mai girma, da kuma fāɗin fahimta marar iyaka, kamar yashi a bakin teku.
30 A o ko Solomona akamai, ua oi aku ia mamua o ke akamai o na kamaaina a pau o ka hikina, a me ke akamai a pau o Aigupita.
Hikimar Solomon ta fi hikimar mutanen Gabas, ta kuma fi dukan hikimar Masar girma.
31 No ka mea, ua oi aku kona akamai mamua o ko na kanaka a pau, mamua o ko Etana o ka Ezera, a me ko Hemana, a me ko Kalekola, a me ko Dareda na keiki a Mahola: a ua kaulana oia ma na lahuikanaka a puni.
Ya fi kowane mutum hikima, har da Etan dangin Ezra ma. Yana da hikima fiye da Heman, Kalkol da Darda,’ya’yan Mahol maza. Sunansa ya bazu ko’ina a ƙasashen da suke kewaye.
32 A ua olelo mai la oia i na olelo akamai ekolu tausani, a o kana mau mele, hookahi tausani ia a me kumamalima.
Ya yi karin magana dubu uku. Waƙoƙinsa kuwa sun kai dubu ɗaya da biyar.
33 A ua olelo mai oia i na laau, mai ka laau Kedera ma Lebanona a hiki i ka husopa, e kupu ana mailoko ae o ka pa: a olelo mai la hoi oia no na holoholona, a me na manu, a me na mea kolo, a me na ia.
Ya yi magana a kan rayuwar itatuwa, daga al’ul na Lebanon zuwa hizzob da yake girma a bangaye. Ya kuma yi koyarwa game da dabbobi, da tsuntsaye, da abubuwa masu rarrafe, da kuma kifi.
34 Hele mai la hoi ko na lahuikanaka a pau e hoolohe i ke akamai o Solomona, mai na lii a pau o ka honua, i lohe i kona akamai.
Mutane suka yi ta zuwa daga ƙasashe dabam-dabam don su ji hikimar Solomon. Sarakuna daga ko’ina a duniya, sun ji labarin hikimarsa, suka kuma aika da mutane don su ji shi.

< I Na Lii 4 >