< I Oihanaalii 18 >
1 MAHOPE mai o keia mea, pepehi aku la o Davida i na Pilisetia, a hoopau ia lakou; a lawe ae la oia ia Gata, a me na kulanahale ona mailoko ae o ka lima o na Pilisetia.
Ana nan sai Dawuda ya ci Filistiyawa ya kuma rinjaye su, ya ƙwace Gat da ƙauyukan kewayenta daga mulkin Filistiyawa.
2 Pepehi aku hoi oia i ka Moaba: a lilo mai la na Moaba i poe kauwa na Davida, a lawe mai la hoi lakou i ka waiwai hookupu.
Dawuda ya kuma ci Mowabawa, suka zama bayinsa suka kuma biya haraji.
3 Pepehi aku la hoi o Davida ia Hadarezera ke alii o Zoba, a hiki i Hamata, ia ia i hele aku ai e hoopaa i kona aupuni ma ka muliwai o Euperate.
Ban da haka, Dawuda ya yaƙi Hadadezer sarkin Zoba, har can Hamat, sa’ad da ya je don yă kafa mulkinsa a wajen Kogin Yuferites.
4 Lawe ae la o Davida mai ona aku i na halekaa he tausani, me na hoohololio ehiku tausani, a me na tausani kanaka kani wawae he iwakalua: oki iho la hoi o Davida i ke olona wawae o na lio a pau o na halekaa; aka, hookoe iho la ia i hookahi haneri o na lio halekaa.
Dawuda ya kame keken yaƙinsa dubu ɗaya, da mahayan kekunan yaƙi dubu bakwai da sojojin kafa guda dubu ashirin. Ya yayyanke dukan agaran dawakansa, amma ya bar dawakai da suka isa jan kekunan yaƙi ɗari.
5 A i ka hele ana mai o ko Suria no Damaseko e kokua mamuli o Hadarezera, ke alii o Zoba, pepehi aku la o Davida i ko Suria he iwakaluakumamalua na tausani kanaka.
Da Arameyawan Damaskus suka zo su taimaki Hadadezer sarkin Zoba, sai Dawuda ya bugi dubu ashirin da biyunsu.
6 A hana iho la o Davida i na pakaua ma Suria no Damaseko, a lilo ae la ko Suria i poe kauwa na Davida, a lawe mai la i ka waiwai hookupu. Pela o Iehova i malama mai ai ia Davida i na wahi a pau ana i hele ai.
Ya sa ƙungiyoyin sojoji a masarautar Arameyawan Damaskus. Arameyawan kuwa suka zama bayinsa, suka kuma kawo haraji. Ubangiji ya ba Dawuda nasara a ko’ina da ya tafi.
7 Lawe ae la hoi o Davida i na palekaua gula maluna o na kauwa a Hadarezera ke alii o Zoba, a lawe mai la ia mau mea i Ierusalema.
Dawuda ya kwashe garkuwoyin zinariyan da shugabannin sojojin Hadadezer suke riƙe, ya kawo su Urushalima.
8 Lawe mai la hoi o Davida i ke keleawe he nui loa, mai Tibehata mai. a mai Kuna hoi, o na kulanakaubale ia o Hadarezera; ka mea keia i hanaia'i e Solomona ke kai keleawe, me na pau a me na ipu keleawe.
Daga Teba da Kun, garuruwan da suke ƙarƙashin Hadadezer, Dawuda ya kwashe tagulla da yawa sosai, wanda Solomon ya yi amfani don yă yi Tekun tagulla, ginshiƙai da kuma kayayyakin tagulla dabam-dabam.
9 A lohe ae la o Tou ke alii o Hamata, ua pepehi o Davida i ka poe kaua a pau o Hadarezera, o ke alii no Zoba;
Sa’ad da Towu sarkin Hamat ya ji cewa Dawuda ya ci mayaƙan Hadadezer sarkin Zoba gaba ɗaya,
10 Hoouna mai la oia i kana keiki ia Hadorama io Davida la, e hooaloha ia ia, a e hoomaikai ia ia, no kona kaua ana ia Hadarezera, a ua pepehi ia ia; (no ka mea, he kanaka o Hadarezera i kaua aku me Tou; ) a me ia no na ipu gula, na ipu kala a me na ipu keleawe he nui loa.
sai ya aiki ɗansa Hadoram zuwa wurin Sarki Dawuda yă gaishe shi yă kuma yi masa barka da nasara a yaƙi a kan Hadadezer, wanda yake yaƙi da Towu. Hadoram ya kawo kowane irin kayayyakin zinariya da na azurfa da na tagulla.
11 Hoolaa aku la o Davida ke alii ia mau mea no Iehova, me ke kala a me ke gula ana i lawe mai ai no na lahuikanaka a pau; mai ka Edoma mai, mai ka Moaba mai, a mai ka poe mamo mai a Amona, a mai ko Pilisetia, a mai ka Amaleka mai.
Sarki Dawuda ya miƙa waɗannan kayayyakin ga Ubangiji, kamar yadda ya yi da azurfa da kuma zinariyan da ya kwaso daga dukan waɗannan al’ummai. Edom da Mowab, Ammonawa da Filistiyawa, da kuma Amalek.
12 A pepehi aku la o Abisai ke keiki a Zeruia i na kanaka o Edoma he umikumamawalu tausani, ma ke awawa paakai.
Abishai ɗan Zeruhiya ya bugi mutanen Edom dubu goma sha takwas a Kwarin Gishiri.
13 Hana iho la hoi oia i na pakaua ma Edoma: a lilo ae la ka Edoma a pau i poe kauwa na Davida. Pela o Iehova i malama mai ai ia Davida i na wahi a pau ana i hele aku ai.
Ya sa ƙungiyoyin sojoji a Edom, dukan mutanen Edom kuwa suka zama bayin Dawuda. Ubangiji ya ba Dawuda nasara a ko’ina da ya tafi.
14 A nohoalii iho la o Davida maluna o ka Iseraela a pau, a hooko aku la i ke kanawai me ka hoopono aku iwaena o kona poe kanaka a pau.
Dawuda ya yi mulki a bisa dukan Isra’ila, yana yin abin da yake daidai da kuma gaskiya saboda dukan mutanensa.
15 A o Ioaba ke keiki a Zeruia, oia ka lunakaua; a o Iehosapata ke keiki a Ahiluda ke kakaolelo.
Yowab ɗan Zeruhiya shi ne shugaban mayaƙa; Yehoshafat ɗan Ahilud shi ne marubuci;
16 A o Zadoka ke keiki a Ahituba, a me Abimeleka ke keiki a Abiatara na kahuna; a o Savasa ke kakauolelo;
Zadok ɗan Ahitub da Abimelek ɗan Abiyatar su ne firistoci; Shafsha shi ne magatakarda;
17 A o Benaia ke keiki a Iehoiada, maluna ia o ka poe Kereti a me ka poe Peleti: a o na keikikane a Davida, he mau luna lakou me ke alii.
Benahiya ɗan Yehohiyada shi ne shugaban Keretawa da Feletiyawa;’ya’yan Dawuda maza su ne manyan ma’aikata a gefen sarki.