< Titus 1 >
1 Bulus, bawan Allah, kuma manzon Yesu Almasihu, ta wurin bangaskiyar zababbun mutanen Allah da sanin gaskiya da ta yadda da allahntaka.
Pavel, služebník Boží, apoštol pak Ježíše Krista, podle víry vyvolených Božích a známosti pravdy, kteráž jest podle zbožnosti,
2 Wadannan na cikin begen rai marar matuka wanda Allah, wanda babu karya a cikinsa, ya alkawarta kafin dukkan lokatan zamanai. (aiōnios )
K naději života věčného, kterýž zaslíbil před časy věků ten, jenž nikdy neklamá, Bůh, zjevil pak časy svými, (aiōnios )
3 A daidai lokaci, ya bayyana maganarsa ta wurin sakonsa da ya damka mani in shelar. Zan yi wannan ta wurin umarnin Allah mai ceton mu.
Totiž to slovo své, skrze kázání mně svěřené, podle zřízení Spasitele našeho Boha, Titovi, vlastnímu synu u víře obecné:
4 Zuwa ga Titus, da' na gaske a cikin bangaskiyarmu. Alheri, jinkai da salama daga wurin Allah Uba da Almasihu Yesu mai ceton mu.
Milost, milosrdenství a pokoj od Boha Otce a Pána Jezukrista Spasitele našeho.
5 Sabili da wannan ne na bar ka a Karita domin ka daidaita abubuwan da basu cika ba, ka kuma nada dattibai a dukan birane kamar yadda na umarceka.
Z té příčiny zanechal jsem tebe v Krétě, abys to, čehož tam ještě potřebí, spravil a ustanovil po městech starší, jakož i já při tobě jsem zřídil:
6 Dole ne dattijo ya zama marar abin zargi, mijin mace daya, da amintattun 'ya'ya wadanda babu wani zargi na mugunta ko rashin kamun kai a kansu.
Jest-li kdo bez úhony, jedné manželky muž, dítky maje věřící, na kteréž by nemohlo touženo býti, že by byli bujní, anebo nepoddaní.
7 Wajibi ne shugaban Ikklisiya, a matsayin sa na mai kulla da haikalin Allah, ya zama marar aibi. Kada ya zama mai surutu ko rashin hakuri. Kada ya zama mai saurin fushi, ko mashayi, ko mai hayaniya, ko mai handama.
Neboť biskup má býti bez úhony, jako Boží šafář, ne svémyslný, ne hněvivý, ne pijan vína, ne bijce, ne žádostivý mrzkého zisku,
8 Maimakon haka, ya zama mai karbar baki, abokin abinda ke mai kyau. Dole ne ya zama mai hankali, adali, cike da allahntaka, da kuma kamun kai.
Ale přívětivý k hostem, dobrotivý, opatrný, spravedlivý, svatý, zdrželivý,
9 Ya zama mai rike amintaccen sakon da aka koyar da karfi, yadda zai iya karfafa wasu da koyarwa mai kyau ya kuma yi wa wadanda suke hamayya da shi gyara.
Pilně se přídržící věrné řeči v učení Božím, aby mohl i napomínati učením zdravým, i ty, kteříž odpírají, přemáhati.
10 Domin akwai kangararrun mutane dayawa, musamman masu kaciya. Maganganunsu na banza ne. Suna yaudara kuma suna badda mutane.
Neboť jsou mnozí nepoddaní, marnomluvní, i svůdcové myslí lidských, zvláště ti, jenž jsou z obřízky.
11 Wajibi ne mu hana su. Suna koyar da abinda bai kamata su koyar ba saboda makunyaciyar riba suna kuma rusar da iyalai dungum.
Jimž musejí ústa zacpána býti; kteříž celé domy převracejí, učíce neslušným věcem, pro mrzký zisk.
12 Daya daga cikinsu, kuma mai hikima ne daga cikinsu, yace, “Kirawa manyan makaryata ne, lalatattu kuma miyagun dabbobi, masu kyiuya da zarin cin abinci.”
Řekl jeden z nich, vlastní jejich prorok, že Kretenští jsou vždycky lháři, zlá hovada, břicha lenivá.
13 Wannan magana gaskiya ne, ka yi masu gyara da tsanani yadda zasu kafu a cikin bangaskiya.
Svědectví to pravé jest. A protož tresciž je přísně, ať jsou zdraví u víře,
14 Kada ka mai da hankalin ka ga tatsunniyoyi na Yahudawa ko dokokin mutane wadanda sun sauya gaskiya.
Nešetříce Židovských básní, a přikázání lidí těch, jenž se odvracují od pravdy.
15 Ga wadanda suke da tsarki, komai mai tsarki ne. Amma wadanda suke marasa tsarki da rashin bangaskiya, komai marar tsarki ne. Domin zuciyarsu da lamirinsu sun gurbata.
Všecko zajisté čisté jest čistým, poskvrněným pak a nevěřícím nic není čistého, ale poskvrněná jest i mysl jejich i svědomí.
16 Suna cewa sun san Allah, amma sun musanta shi ta wurin ayyukansu. Sun zama abin kyama da marasa biyayya. Ba za a iya tabbaatar dasu ba akan wani aiki maikyau.
Vypravují o tom, že Boha znají, ale skutky svými toho zapírají, ohavní jsouce, a nepoddaní, a ke všelikému skutku dobrému nehodní.