< Romawa 7 >
1 'Yan'uwa, ko baku sani ba (domin ina magana da wadanda suka san shari'a), cewar shari'a na mulkin mutum muddin ransa?
Czyż nie wiecie, bracia (bo mówię do znających prawo), że prawo panuje nad człowiekiem, dopóki on żyje?
2 Domin ta wurin shari'a matar aure a daure take muddin mijinta nada rai, amma idan mijinta ya mutu, ta kubuta daga shari'ar aure.
Zamężna kobieta bowiem, dopóki mąż żyje, jest z nim związana prawem, a jeśli mąż umrze, zostaje uwolniona od prawa męża.
3 To don haka idan, mijinta na da rai, sai ta tafi ta zauna da wani mutumin, za'a kirata mazinaciya. Amma idan mijin ya mutu, ''yantarciya ce daga shari'a, domin kada ta kasance mazinaciya idan ta auri wani mutum.
Tak więc, dopóki mąż żyje, będzie nazywana cudzołożnicą, jeśli zostanie żoną innego mężczyzny. Jeśli jednak jej mąż umrze, jest wolna od tego prawa, tak że nie będzie cudzołożnicą, choćby została żoną innego mężczyzny.
4 Domin wannan, 'yan'uwana, ku ma an sa kun mutu ga shari'a ta wurin jikin Almasihu, saboda a hada ku aure da wani, wato, ga wanda aka tashe shi daga matattu, domin mu haifawa Allah 'ya'ya.
Tak i wy, moi bracia, zostaliście uśmierceni dla prawa przez ciało Chrystusa, abyście należeli do innego, [to znaczy] tego, który został wskrzeszony z martwych, abyśmy przynosili Bogu owoc.
5 Domin sa'adda muke cikin jiki, ana motsa dabi'armu ta zunubi dake cikin jikunan mu ta wurin shari'a domin mu haifi 'ya'ya zuwa mutuwa.
Gdy bowiem byliśmy w ciele, namiętności grzechów, które [się wzniecały] przez prawo, okazywały swą moc w naszych członkach, aby przynosić śmierci owoc.
6 Amma yanzu an kubutar damu daga shari'a, mun mutu daga abin da ya daure mu, domin mu yi bauta cikin sabuntuwar Ruhu, ba cikin tsohon rubutun shari'a ba.
Lecz teraz zostaliśmy uwolnieni od prawa, gdy umarliśmy dla tego, w czym byliśmy trzymani, abyśmy służyli [Bogu] w nowości ducha, a nie w starości litery.
7 To me zamu ce kenan? ita shari'ar kanta zunubi ce? ba zai taba faruwa ba. Duk da haka. Idan ba ta wurin shari'a ba, ba zan taba sanin zunubi ba, in ba ta wurin shari'a ba. Ba zan taba kyashin abin wani ba, har sai da shari'a tace, “Kada kayi kyashi.”
Cóż więc powiemy? Że prawo [jest] grzechem? Nie daj Boże! Przeciwnie, nie poznałem grzechu [jak] tylko przez prawo, bo i o pożądliwości nie wiedziałbym, gdyby prawo nie mówiło: Nie będziesz pożądał.
8 Amma zunubi, sai ya dauki zarafi ta wurin dokar, ya jawo dukkan sha'awa dake cikina. Domin in da babu shari'a, zunubi matacce ne.
Lecz grzech, gdy zyskał okazję przez przykazanie, wzbudził we mnie wszelką pożądliwość. Bez prawa bowiem grzech jest martwy.
9 Ada na rayu sau daya ba tare da shari'a ba, amma da dokar ta zo, sai zunubi ya farfado, ni kuma na mutu.
I ja żyłem kiedyś bez prawa, lecz gdy przyszło przykazanie, grzech ożył, a ja umarłem.
10 Dokar wadda ta kamata ta kawo rai, sai na same ta matacciya.
I okazało się, że przykazanie, które [miało być] ku życiu, jest [mi] ku śmierci.
11 Domin zunubin, ya dauki zarafi ta wurin dokar, ya rude ni, kuma ta wurin dokar ya kashe ni.
Grzech bowiem, gdy zyskał okazję przez przykazanie, zwiódł mnie i przez nie [mnie] zabił.
12 Domin haka, shari'ar na da tsarki, dokar na da tsarki, adalci da kuma kyau.
A tak prawo [jest] święte i przykazanie [jest] święte, sprawiedliwe i dobre.
13 To abu mai kyau ya zamar mani mutuwa kenan? ba zai taba zama haka ba. Amma zunubi, domin ya nuna shi zunubi ne ta wurin abin da ke mai kyau, sai ya kawo mutuwa a cikina. Wannan ya kasance haka ne domin ta wurin dokar, zunubi ya zama cikakken zunubi.
Czy więc to, co dobre, stało się dla mnie śmiercią? Nie daj Boże! Przeciwnie, grzech, aby okazał się grzechem, sprowadził na mnie śmierć przez [to, co] dobre, żeby grzech stał się niezmiernie grzesznym przez przykazanie.
14 Domin mun san shari'a mai Ruhaniya ce, amma ni ina cikin jiki. An sai da ni karkashin bautar zunubi.
Gdyż wiemy, że prawo jest duchowe, ale ja jestem cielesny, zaprzedany grzechowi.
15 Domin ni ma ban fahimci abin da nake aikatawa ba. Domin abin da nake so in aikata, ba shi nake aikatawa ba, kuma abin da bana so, shi nake aikatawa.
[Tego] bowiem, co robię, nie pochwalam, bo nie robię tego, co chcę, ale czego nienawidzę, to robię.
16 Amma idan na aikata abin da bana so, na amince da shari'a kenan, cewar shari'a nada kyau.
A jeśli robię to, czego nie chcę, zgadzam się z tym, że prawo [jest] dobre.
17 Amma yanzu ba ni ke aikata abin ba, amma zunubi da ke zaune a cikina.
Teraz więc już nie ja to robię, ale grzech, który we mnie mieszka.
18 Domin na san a cikina, wato cikin jikina, babu wani abu mai kyau. Domin marmarin aikata abu mai kyau na tare da ni, amma ba ni iya aikatawa.
Gdyż wiem, że we mnie, to jest w moim ciele, nie mieszka dobro, bo chęć jest we mnie, ale wykonać tego, co [jest] dobre, nie potrafię.
19 Domin abu mai kyau da na ke so in aikata bana iyawa, amma muguntar da ba na so ita na ke aikatawa.
Nie czynię bowiem dobra, które chcę, ale zło, którego nie chcę, to czynię.
20 To idan na yi abin da ba ni so in aikata, wato kenan ba ni bane ke aikatawa, amma zunubin da ke zaune a cikina.
A jeśli robię to, czego nie chcę, [już] nie ja to robię, ale grzech, który we mnie mieszka.
21 Don haka, sai na iske, akwai ka'ida a cikina dake son aikata abu mai kyau, amma kuma ainihin mugunta na tare dani.
Odkrywam więc [w sobie] to prawo, że gdy chcę czynić dobro, trzyma się mnie zło.
22 Domin a cikina ina murna da shari'ar Allah.
Mam bowiem upodobanie w prawie Bożym według wewnętrznego człowieka.
23 Amma ina ganin wasu ka'idoji daban a gabobin jikina, su na yaki da wannan sabuwar ka'idar da ke cikin tunanina, suna kuma sanya ni bauta ta wurin ka'idar zunubi wadda ke cikin gabobin jikina.
Lecz widzę inne prawo w moich członkach, walczące z prawem mego umysłu, które bierze mnie w niewolę prawa grzechu, które jest w moich członkach.
24 Ni wahalallen mutum ne! wa zai kubutar dani daga wannan jiki na mutuwa?
Nędzny ja człowiek! Któż mnie wybawi z tego ciała śmierci?
25 Amma godiya ga Allah ta wurin Yesu Almasihu Ubangijinmu! Domin haka ni kaina a wannan hannu bisa ga tunani na ina bautawa shari'ar Allah. Duk da haka, ta wani gefen ina bautawa ka'idar zunubi da ke tare da jikina.
Dziękuję Bogu przez Jezusa Chrystusa, naszego Pana. Tak więc ja sam umysłem służę prawu Bożemu, lecz ciałem prawu grzechu.