< Romawa 7 >

1 'Yan'uwa, ko baku sani ba (domin ina magana da wadanda suka san shari'a), cewar shari'a na mulkin mutum muddin ransa?
Ne savez-vous pas, mes frères (car je parle à ceux qui entendent ce que c'est que la Loi) que la Loi exerce son pouvoir sur l'homme durant tout le temps qu'il est en vie?
2 Domin ta wurin shari'a matar aure a daure take muddin mijinta nada rai, amma idan mijinta ya mutu, ta kubuta daga shari'ar aure.
Car la femme qui est sous la puissance d'un mari, est liée à son mari par la Loi, tandis qu'il est en vie; mais si son mari meurt, elle est délivrée de la loi du mari.
3 To don haka idan, mijinta na da rai, sai ta tafi ta zauna da wani mutumin, za'a kirata mazinaciya. Amma idan mijin ya mutu, ''yantarciya ce daga shari'a, domin kada ta kasance mazinaciya idan ta auri wani mutum.
Le mari donc étant vivant, si elle épouse un autre mari elle sera appelée adultère; mais son mari étant mort, elle est délivrée de la Loi; tellement qu'elle ne sera point adultère si elle épouse un autre mari.
4 Domin wannan, 'yan'uwana, ku ma an sa kun mutu ga shari'a ta wurin jikin Almasihu, saboda a hada ku aure da wani, wato, ga wanda aka tashe shi daga matattu, domin mu haifawa Allah 'ya'ya.
Ainsi mes frères, vous êtes aussi morts à la Loi par le corps de Christ, pour être à un autre, [savoir] à celui qui est ressuscité des morts, afin que nous fructifions à Dieu.
5 Domin sa'adda muke cikin jiki, ana motsa dabi'armu ta zunubi dake cikin jikunan mu ta wurin shari'a domin mu haifi 'ya'ya zuwa mutuwa.
Car quand nous étions en la chair, les affections des péchés [étant excitées] par la Loi, avaient vigueur en nos membres, pour fructifier à la mort.
6 Amma yanzu an kubutar damu daga shari'a, mun mutu daga abin da ya daure mu, domin mu yi bauta cikin sabuntuwar Ruhu, ba cikin tsohon rubutun shari'a ba.
Mais maintenant nous sommes délivrés de la Loi, [la Loi] par laquelle nous étions retenus étant morte; afin que nous servions [Dieu] en nouveauté d'esprit, et non point en vieillesse de Lettre.
7 To me zamu ce kenan? ita shari'ar kanta zunubi ce? ba zai taba faruwa ba. Duk da haka. Idan ba ta wurin shari'a ba, ba zan taba sanin zunubi ba, in ba ta wurin shari'a ba. Ba zan taba kyashin abin wani ba, har sai da shari'a tace, “Kada kayi kyashi.”
Que dirons-nous donc? La Loi est-elle péché? à Dieu ne plaise! au contraire je n'ai point connu le péché, sinon par la Loi: car je n'eusse pas connu la convoitise, si la Loi n'eût dit: tu ne convoiteras point.
8 Amma zunubi, sai ya dauki zarafi ta wurin dokar, ya jawo dukkan sha'awa dake cikina. Domin in da babu shari'a, zunubi matacce ne.
Mais le péché ayant pris occasion par le commandement, a produit en moi toute sorte de convoitise; parce que sans la Loi le péché est mort.
9 Ada na rayu sau daya ba tare da shari'a ba, amma da dokar ta zo, sai zunubi ya farfado, ni kuma na mutu.
Car autrefois que j'étais sans la Loi, je vivais; mais quand le commandement est venu, le péché a commencé à revivre.
10 Dokar wadda ta kamata ta kawo rai, sai na same ta matacciya.
Et moi je suis mort; et le commandement qui [m'était ordonné] pour [être ma] vie, a été trouvé [me tourner] à mort.
11 Domin zunubin, ya dauki zarafi ta wurin dokar, ya rude ni, kuma ta wurin dokar ya kashe ni.
Car le péché prenant occasion du commandement, m'a séduit, et par lui m'a mis à mort.
12 Domin haka, shari'ar na da tsarki, dokar na da tsarki, adalci da kuma kyau.
La Loi donc est sainte, et le commandement est saint, juste, et bon.
13 To abu mai kyau ya zamar mani mutuwa kenan? ba zai taba zama haka ba. Amma zunubi, domin ya nuna shi zunubi ne ta wurin abin da ke mai kyau, sai ya kawo mutuwa a cikina. Wannan ya kasance haka ne domin ta wurin dokar, zunubi ya zama cikakken zunubi.
Ce qui est bon, m'est-il devenu mortel? nullement! mais le péché, afin qu'il parût péché, m'a causé la mort par le bien; afin que le péché fût rendu par le commandement excessivement péchant.
14 Domin mun san shari'a mai Ruhaniya ce, amma ni ina cikin jiki. An sai da ni karkashin bautar zunubi.
Car nous savons que la Loi est spirituelle; mais je suis charnel, vendu au péché.
15 Domin ni ma ban fahimci abin da nake aikatawa ba. Domin abin da nake so in aikata, ba shi nake aikatawa ba, kuma abin da bana so, shi nake aikatawa.
Car je n'approuve point ce que je fais, puisque je ne fais point ce que je veux, mais je fais ce que je hais.
16 Amma idan na aikata abin da bana so, na amince da shari'a kenan, cewar shari'a nada kyau.
Or si ce que je fais je ne le veux point, je reconnais [par cela même] que la Loi est bonne.
17 Amma yanzu ba ni ke aikata abin ba, amma zunubi da ke zaune a cikina.
Maintenant donc ce n'est plus moi qui fais cela; mais c'est le péché qui habite en moi.
18 Domin na san a cikina, wato cikin jikina, babu wani abu mai kyau. Domin marmarin aikata abu mai kyau na tare da ni, amma ba ni iya aikatawa.
Car je sais qu'en moi, c'est-à-dire, en ma chair, il n'habite point de bien; vu que le vouloir est bien attaché à moi, mais je ne trouve pas le moyen d'accomplir le bien.
19 Domin abu mai kyau da na ke so in aikata bana iyawa, amma muguntar da ba na so ita na ke aikatawa.
Car je ne fais pas le bien que je veux, mais je fais le mal que je ne veux point.
20 To idan na yi abin da ba ni so in aikata, wato kenan ba ni bane ke aikatawa, amma zunubin da ke zaune a cikina.
Or si je fais ce que je ne veux point, ce n'est plus moi qui le fais, mais [c'est] le péché qui habite en moi.
21 Don haka, sai na iske, akwai ka'ida a cikina dake son aikata abu mai kyau, amma kuma ainihin mugunta na tare dani.
Je trouve donc cette Loi au-dedans de moi, que quand je veux faire le bien, le mal est attaché à moi.
22 Domin a cikina ina murna da shari'ar Allah.
Car je prends bien plaisir à la loi de Dieu quant à l'homme intérieur;
23 Amma ina ganin wasu ka'idoji daban a gabobin jikina, su na yaki da wannan sabuwar ka'idar da ke cikin tunanina, suna kuma sanya ni bauta ta wurin ka'idar zunubi wadda ke cikin gabobin jikina.
Mais je vois dans mes membres une autre loi, qui combat contre la loi de mon entendement, et qui me rend prisonnier à la loi du péché, qui est dans mes membres.
24 Ni wahalallen mutum ne! wa zai kubutar dani daga wannan jiki na mutuwa?
[Ha!] misérable que je suis! qui me délivrera du corps de cette mort?
25 Amma godiya ga Allah ta wurin Yesu Almasihu Ubangijinmu! Domin haka ni kaina a wannan hannu bisa ga tunani na ina bautawa shari'ar Allah. Duk da haka, ta wani gefen ina bautawa ka'idar zunubi da ke tare da jikina.
Je rends grâces à Dieu par Jésus-Christ notre Seigneur. Je sers donc moi-même de l'entendement à la Loi de Dieu, mais de la chair, à la loi du péché.

< Romawa 7 >