< Romawa 4 >
1 Me kenan zamu ce game da Ibrahim, kakanmu a jiki, me ya samu?
Twibetakujobha kiki kabhele kujha Abrahamu, dadi jhitu kwa namna jha mb'el'e, abhonekene?
2 Domin idan Ibrahim ya sami kubutarwa ta wurin ayuka, ai da ya sami dalilin fahariya, amma ba a gaban Allah ba.
Kwa ndabha ikajhelayi Abrahamu abhalangibhu haki kwa matendo, na aajhe ni sababu jha kwitufya, lakini sio palongolo pa K'yara.
3 Kuma fa me nassi ke fadi? “Ibrahim ya bada gaskiya ga Allah, sai aka lisafta ta adalci gare shi.”
Kwani majhandiku ghijobhuli? “Abrahamu an'kyeriri K'yara na abhalangibhu kwa muene kujha haki.”
4 Yanzu fa shi dake yin ayyuka, ladansa ba a lisafta shi alheri ba ne, amma abun da ke nasa.
Henu kwa munu jha ibhomba mbombo, mal'epu gha muene ghibhalangibhwa lepi kujha ni neema, bali kujha lideni.
5 Amma kuma shi da bai da ayyuka kuma maimakon haka ya gaskanta ga wanda ke kubutar da masu zunubai, bangaskiyarsa an lisafta ta a misalin adalci.
Lakini kwa munu jha ibhomba lepi mbombo jhojhioha bali akan'kiera muene ambajhe akambalangila haki jhaabeli kujha mtauwa, imani jha muene munu ojhu jhibalangibhu kujha haki.
6 Dauda ya yi furcin albarka bisa mutumin da Allah ya lisafta mai adalci da rashin ayyuka.
Daudi ni muene ijobha baraka panani pa munu ambajhe K'yara akambalangila haki bila matendo.
7 Sai ya ce, “Masu albarka ne wadanda aka yafe laifofinsu, kuma wadanda zunubansu a rufe suke.
Ajobhili, “Bhabarikibhu bhala ambabho maovu gha bhene ghasamehibhu ni ambapo dhambi sya bhene sigupikibhu.
8 Mai albarka ne mutumin da ko kadan Ubangiji ba zaya lisafta zunubin sa ba.”
Abarikibhu munu jhola ambajhe Bwana akambalangila lepi dhambi.”
9 To albarkar da aka fadi ko a bisansu wadanda aka yi wa kaciya ne kadai, ko kuwa a bisan su ma marasa kaciya? Domin mun yi furcin, “Bangaskiyar Ibrahim an lisafta ta adalci ce agare shi.”
Basi je baraka e'se ndo kwa bhala bhabhatahiribhu tu, au kabhele ni kwa bhala bhabhabelikutahiribhwa? Kwa ndabha twijobha, “kwa Abrahamu imani jha muene jhabhalangiki kujha jha haki.”
10 Yaya aka lisafta ta? Bayan Ibrahim ya yi kaciya, ko kuwa a rashin kaciya? Ba a cikin kaciya ba, amma a rashin kaciya.
Henu jhabhalangibhu bhuli? Wakati Abrahamu ajhele mu tohara, au bho akhona kutahiribhwa? Jhajhelepi mu kutahiribhwa, bali kubela kutahiribhwa.
11 Ibrahim ya amshi alamar kaciya. Wannan shi ne hatimin adalcin bangaskiyar da ya ke da ita tun cikin rashin kaciyarsa. Albarkacin wannan alama ce, ta sa shi ya zama uban dukkan wadanda suka badagaskiya, ko da shike ba su da kaciya. Wato ma'ana, adalci za a lisafta masu.
Abrahamu apokili alama jha kutahiribhwa. Obho bhwajhele bhola muhuribhwa jhela haki jha amani jhaajhe nayu tayari kabla jha kutahiribhwa. Matokeo jha ishara ejhe ndo kwamba abhombiki kujha dadi ghwa bhoha bhabhikiera, hata kama bhajhele mu kutokutahiribhwa. Ejhe jhijhe ni maana kujha haki jhibetakubhalangibhwa kwa bhene.
12 Wannan kuma yana da ma'anar cewa Ibrahim ya zama uban kaciya ga wadanda suka fito ba domin masu kaciya kadai ba, amma kuma domin wadanda ke biyo matakin ubanmu Ibrahim. Kuma wannan itace bangaskiyar da ya ke da ita a rashin kaciya.
Ejhe kabhele jha maamisi kujha Abrahamu abhombiki kujha dadi ghwa tohara sio tu kwa bhala bhabhitokana ni tohara, bali bhala bhabhakasikesya nyayu sya dadijhitu Abrahamu. Na ejhe ndo imani jhaajhe najhu kwa bhabeli kutahiribhwa.
13 Domin ba ta wurin shari'a aka bada alkawarin nan da aka yi wa Ibrahim da zuriyarsa ba, wannan alkawarin da ya ce zasu gaji duniya. Maimako, a ta wurin adalcin bangaskiya ne.
Kwa ndabha jha jhelepi kwa sheria kwamba ahadi jhahomesibhu kwa Abrahamu ni uzao bhwa muene, ahadi ejhe jha kujha bhibetakujha bharithi bha dunia. Isipokujha jhajhele kup'et'ela haki jha imani.
14 Domin idan su da ke na shari'a magada ne, bangaskiya bata da komai, kuma alkawarin an wofintar da shi kenan.
Kwa maana kama bhala, bha sheria ndo bharithi, imani ijhele jha bhwaka, ni ahadi jhibatiliki.
15 Domin shari'a ta kan jawo fushi, amma ta wurin rashin shari'a, babu karya umarni.
Kwa ndabha sheria jhileta ghadhabu, lakini pala ambapo ijhelepi sheria, kabhele kujhelepi kutii.
16 Saboda wannan dalili haka ta faru ta wurin bangaskiya, domin ya zama bisa ga alheri. Kamar haka, alkawarin ya tabbata ga dukkan zuriya. Kuma wannan zuriya ba zata kunshi wadanda suke da sanin shari'a ba kadai, har ma da wadanda ke daga bangaskiyar Ibrahim. Saboda shi ne uban dukkan kowa,
Kwa ndabha ejhe e'le lihomela kwa imani, ili ijhelayi kwa neema. Matokeo ghake, ahadi ndo dhahiri kwa uzao bhuha. Ni bhazawa abha sio tu bhala bhabhajhimanyi sheria, bali kabhele bhala ambabho ndo bha imani jha Abrahamu. Kwa maana muene ndo dadijhitu tete twebhoka,
17 kamar yadda aka rubuta, “Na maishe ka uba ga kasashe masu yawa.” Ibrahim na gaban aminin sa, wato, Allah, mai bada rai ga mattatu kuma ya kan kira abubuwan da basu da rai su kuma kasance.
kama kyajhilembibhu, “Nikubhombili bhebhe kujha dadi ghwa mataifa ghamehele.” Abrahamu ajhele mu uwepo bhwa jhola jhaamwamini, yaani, K'yara ambajhe akabhapela bhanu uzima ni kughakuta mambo ambagho ghajhelepi ili ghabhwesiajhi kujha.
18 Duk da halin da ke a bayyane, Ibrahim ya gaskata ga Allah kai tsaye game da abubuwan da ke nan gaba. Sai ya zama uba ga kasashe masu yawa, kamar yadda aka ambata, “... Haka zuriyarka zata kasance.”
Licha jha hali syoha syakwibhala, Abrahamu kwa ujasiri an'kieriri K'yara kwa magono ghaghahideghe. Naha ajhele dadi ghwa mataifa ghamehele, kul'engana ni khela kyakyajobhibhu, “... Ndo kwawibetakujha uzao bhwa bhebhe.”
19 Ba ya karaya a bangaskiya ba. Ibrahim ya yarda da cewa jikinsa ya rigaya ya tsufa (shekarun sa na misalin dari). Ya kuma yarda da cewa mahaifar Saratu bata iya bada 'ya'ya ba.
Muene ajhelepi dhaifu mu imani. Abrahamu ajobhili kujhamb'el'e ghwa muene bhwamalili kujha bhufwili - ajhele ni umuli kulibila miaka mia moja. Kabhele ajhedekili ni hali jha kufwa jha lileme lya Sara.
20 Amma domin alkawarin Allah, Ibrahim bai ji nauyin rashin bangaskiya ba. Maimakon haka, ya sami karfafawa a bangaskiyarsa sai ya daukaka Allah.
Lakini kwa ndabha jha ahadi jha K'yara, Abrahamu abelilepi kubela kukiera, bali apelibhu nghofu mu imani ni kun'tufya K'yara.
21 Ya na da cikakkiyar gamsuwa cewa idan Allah ya yi alkawari, shi mai iya kammalawa ne.
Ajhele amanyili bhukweli kujha khela ambakyo K'yara aahidi, ajhele kabhele ni bhuwezo bhwa kukikamilisya.
22 Haka nan ne kuma aka lisafta masa wannan a matsayin adalci.
Henu ejhe kabhele jhabhalangibhu kwa muene kujha ndo haki.
23 To ba'a rubuta kawai damin amfaninsa kadai ba, da aka lisafta dominsa.
Henu jhalembibhu lepi tu kwa faida jha muene, kujha jhabhalangibhu kwa muene.
24 A rubuce yake domin mu, domin wadanda za'a lisafta su, mu da muka bada gaskiya gare shi wanda ya tada Yesu Ubangijinmu daga matattu.
Jhalembibhu kwa ndabha jha tete kabhele, kwa bhabhekibhu kubhalangibhwa tete ambabho twikiera kwa muene jha amfufuili Bwana bhitu Yesu kuhoma kwa bhafu.
25 Wannan shi ne wanda aka bashe shi domin zunubanmu kuma an tada shi saboda fasar mu.
Ojho ndo jhola ambajhe apisibhu kwandabha jha makosa ghitu ni kufufulibhwa ili tukabhayi kubhalangibhwa haki.