< Romawa 3 >

1 To ina fifikon da bayahude yake dashi? Kuma ina ribar kaciya?
WHAT advantage then hath the Jew? or what profit is there of circumcision?
2 Akwai muhimmancinsu ta kowacce hanya. Tun farko dai, yahudawa ne aka dankawa wahayi daga Allah.
Much every way: chiefly, because that unto them were committed the oracles of God.
3 Idan wasu yahudawa basu bada gaskiya ba fa? Rashin bangaskiyarsu zai hana amincin Allah aiki?
For what if some did not believe? shall their unbelief make the faith of God without effect?
4 Bazai taba zama haka ba. Maimakon haka, bari Allah ya zama mai gaskiya, ko da kowanne mutum makaryaci ne. Kamar yadda aka rubuta, “Domin a nuna kai mai adalci cikin maganganunka, kuma kayi nasara a lokacin da aka kawo ka gaban shari'a.”
God forbid: yea, let God be true, but every man a liar; as it is written, That thou mightest be justified in thy sayings, and mightest overcome when thou art judged.
5 Amma idan rashin adalcinmu ya nuna adalcin Allah, to me zamu ce? Allah ba marar adalci ba ne, wanda ke aiwatar da fushinsa, ko kuwa? Ina magana bisa ga tunanin mutuntaka.
But if our unrighteousness commend the righteousness of God, what shall we say? Is God unrighteous who taketh vengeance? (I speak as a man)
6 Bazai taba zama haka ba. Domin idan haka ne ta yaya Allah zai shar'anta duniya?
God forbid: for then how shall God judge the world?
7 Amma idan gaskiyar Allah ta wurin karyata ta habaka yabonsa, To me yasa ake shar'anta ni a matsayin mai zunubi?
For if the truth of God hath more abounded through my lie unto his glory; why yet am I also judged as a sinner?
8 To me zai hana ace kamar yadda ake fadin zancen karya a kanmu, wasu kuma sun dauka cewa mun fadi hakan, “Bari muyi mugunta, domin nagarta tazo?” Hukuncin su halal ne.
And not rather, (as we be slanderously reported, and as some affirm that we say, ) Let us do evil, that good may come? whose damnation is just.
9 To me kenan? Zamu ba kanmu hujja ne? ko kadan. Domin mun riga munyi zargin yahudawa da hellinawa, da cewar dukkansu, suna karkashin zunubi.
What then? are we better than they? No, in no wise: for we have before proved both Jews and Gentiles, that they are all under sin;
10 Kamar yadda aka rubuta, babu wani mai adalci, babu ko daya.
As it is written, There is none righteous, no, not one:
11 Babu wani mai fahimta. Babu wani mai neman Allah.
There is none that understandeth, there is none that seeketh after God.
12 Dukansu sun kauce hanya, dukansu gaba daya sun zama marasa amfani. Babu mai aikin nagarta, a'a, babu ko da guda daya.
They are all gone out of the way, they are together become unprofitable; there is none that doeth good, no, not one.
13 Makogwaronsu a bude yake kamar kabari. Harsunansu na dauke da cuta. Dafin macizai na karkashin lebunansu.
Their throat is an open sepulchre; with their tongues they have used deceit; the poison of asps is under their lips:
14 Bakunansu cike suke da la'ana da daci.
Whose mouth is full of cursing and bitterness:
15 Sawayensu na saurin zuwa zubar da jini.
Their feet are swift to shed blood:
16 Tafarkinsu wahala ce da lalacewa.
Destruction and misery are in their ways:
17 Wadannan mutane basu san hanyar salama ba.
And the way of peace have they not known:
18 Babu tsoron Allah a idanunsu.”
There is no fear of God before their eyes.
19 To mun san dai duk abin da shari'a tace, shari'a na magana ne da wadanda ke karkashinta, domin a rufe kowanne baki, domin dukan duniya ta bada amsa a gaban Allah.
Now we know that what things soever the law saith, it saith to them who are under the law: that every mouth may be stopped, and all the world may become guilty before God.
20 Domin a gabansa babu wanda zai barata ta wurin ayukan shari'a. Domin ta wurin shari'a ne sanin zunubi yazo.
Therefore by the deeds of the law there shall no flesh be justified in his sight: for by the law is the knowledge of sin.
21 Amma yanzu ba tare da shari'a ba an bayyana sanin adalcin Allah, wanda shari'a da annabawa suke shaidawa.
But now the righteousness of God without the law is manifested, being witnessed by the law and the prophets;
22 Wato, adalcin Allah ta wurin bangaskiya cikin Yesu Almasihu ga dukkan wadanda ke bada gaskiya. Domin babu bambanci:
Even the righteousness of God which is by faith of Jesus Christ unto all and upon all them that believe: for there is no difference:
23 Domin duk sun yi zunubi sun kuma kasa kaiwa ga darajar Allah,
For all have sinned, and come short of the glory of God;
24 Da alherinsa an baratar da mu ta wurin fansar dake cikin Yesu Almasihu.
Being justified freely by his grace through the redemption that is in Christ Jesus:
25 Amma Allah ya bayar da Yesu Almasihu wanda yake hadayar fansa ta wurin bangaskiya cikin jininsa. Ya mika Almasihu a matsayin tabbacin hukuncinsa, sabo da kuma ketarewar zunubanmu na baya
Whom God hath set forth to be a propitiation through faith in his blood, to declare his righteousness for the remission of sins that are past, through the forbearance of God;
26 cikin hakurinsa. Duk wannan ya faru ne domin a bayyana adalcinsa cikin wannan zamani, domin ya tabbatar da kansa mai hukunci, kuma ya nuna shine mai baratar da kowa saboda bangaskiya cikin Yesu.
To declare, I say, at this time his righteousness: that he might be just, and the justifier of him which believeth in Jesus.
27 To ina fahariya? An fitar da ita. A kan wane dalilin? Don ayyuka? A'a, amma ta dalilin bangaskiya.
Where is boasting then? It is excluded. By what law? of works? Nay: but by the law of faith.
28 Domin wannan muka kammala cewar ana baratar da mutum ta wurin bangaskiya ba tare da ayyukan shari'a ba.
Therefore we conclude that a man is justified by faith without the deeds of the law.
29 Ko kuwa Allah Allahn yahudawa ne kadai? Shi ba Allahn al'ummai bane? I, na al'ummai ne kuma.
Is he the God of the Jews only? is he not also of the Gentiles? Yes, of the Gentiles also:
30 Idan dai lallai Allah daya ne, zai baratar da mai kaciya ta wurin bangaskiya, da marar kaciya kuma ta wurin bangaskiya.
Seeing it is one God, which shall justify the circumcision by faith, and uncircumcision through faith.
31 Mun kawar da shari'a kenan ta wurin bangaskiya? ba zai taba kasancewa haka ba. Maimako ma, muna inganta shari'a kenan.
Do we then make void the law through faith? God forbid: yea, we establish the law.

< Romawa 3 >