< Romawa 15 >

1 Yanzu mu da muke da karfi ya kamata mu dau nauyi raunana, kuma bai dace mu nuna son kai ba.
Nous devons donc, nous qui sommes forts, supporter les infirmités des faibles, et ne pas nous complaire en nous-mêmes.
2 Bari kowannenmu ya faranta wa makwabcinsa rai, domin wannan yana da kyau, don a gina shi.
Que chacun de nous complaise plutôt à son prochain, dans le bien, pour l'édification;
3 Domin Almasihu bai faranta wa kansa rai ba. Kamar yadda aka rubuta, “zagin da wadansu suka yi masa ya sauka a kaina.”
Car aussi Christ ne s'est point complu en lui-même; mais selon qu'il est écrit: Les outrages de ceux qui t'outragent, sont tombés sur moi.
4 Don abin da aka rubuta a baya an rubuta ne domin a gargade mu, domin ta hakuri da karfafawar litattafai mu sami karfi.
Or, tout ce qui a été écrit autrefois, a été écrit pour notre instruction, afin que, par la patience et la consolation que donnent les Écritures, nous possédions l'espérance.
5 Yanzu Allah mai hakuri da karfafawa ya baku zuciya daya ta zaman tare da juna bisa ga halin Yesu Almasihu.
Et que le Dieu de patience et de consolation vous donne d'avoir les mêmes sentiments entre vous selon Jésus-Christ;
6 Domin ya yi haka ne da zuciya daya domin ku yi yabo da bakinku daya.
Afin que, d'un même cœur et d'une même bouche, vous glorifiiez le Dieu qui est le Père de notre Seigneur Jésus-Christ.
7 Domin ku karbi juna, kamar yadda Yesu ma ya karbe ku domin a daukaka Allah.
C'est pourquoi accueillez-vous les uns les autres, comme Christ nous a accueillis pour la gloire de Dieu.
8 Saboda na ce an mai da Almasihu bawan kaciya a madadin gaskiyar Allah. Ya yi wannan ne don a tabbatar da alkawarai da aka ba kakanin kakaninmu.
Je dis donc que Jésus-Christ a été ministre des circoncis, pour montrer la fidélité de Dieu, en accomplissant les promesses faites aux pères;
9 Domin Al'umai su daukaka Allah saboda jinkansa, kamar yadda ya ke a arubuce, “Domin ta haka zan yabe ka cikin Al'umai in yi wakar yabon sunanka.”
Et afin que les Gentils glorifient Dieu à cause de sa miséricorde, selon qu'il est écrit: C'est pour cela que je te louerai parmi les Gentils, et que je chanterai à ton nom.
10 Kuma an ce. “Ku yi faranciki, ku Al'ummai tare da mutanensa.”
Il est dit encore: Gentils, réjouissez-vous avec son peuple.
11 Kuma.” Ku yabi Ubangiji, ku dukan Al'ummai; bari dukan mutane su yabe shi.”
Et encore: Nations, louez toutes le Seigneur, et peuples, célébrez-le tous.
12 Kuma, Ishaya ya ce “Za a sami tsatson Yessi, wanda zai tashi ya yi mulki a kan Al'umai, Al'umai za su sami karfin hali a cikinsa.”
Ésaïe dit aussi: Jessé aura un rejeton qui se lèvera pour gouverner les Gentils; les Gentils espéreront en lui.
13 Yanzu Allah mai karfafawa ya cika ku da dukkan farin ciki salama, saboda da bangaskiyarku, domin ku sami cikkakiyar karafafawa, ta wurin ikon Ruhu Mai Tsarki.
Que le Dieu d'espérance vous remplisse donc de toute sorte de joie et de paix, dans la foi, afin que vous abondiez en espérance, par la puissance du Saint-Esprit.
14 Ni kaina na amince da ku, yan'uwa. Kuma na amince cewa ku da kanku kuna cike da alheri, cike da dukkan sani. Na amince cewa za ku sami zarafi ku gargadi juna.
Pour moi, frères, j'ai la persuasion que vous êtes pleins de bonté, remplis de toute connaissance, et capables de vous exhorter les uns les autres.
15 Amma ina rubuta maku da gabagadi kan wadansu abubuwa, domin in tunasheku, saboda baiwar da aka bani daga wurin Allah.
Cependant, frères, je vous ai écrit plus librement en quelque sorte, pour réveiller vos souvenirs, selon la grâce qui m'a été donnée de Dieu,
16 Cewa baiwar ta sa na zama bawan Almasihu Yesu da aka aika ga Al'ummai, limami na bisharar Allah. Zan yi wannan saboda baikon Al'ummai ya zama karbabbe, kuma kebbabe ga Allah ta wurin Ruhu Mai Tsarki.
D'être le ministre de Jésus-Christ auprès des Gentils et d'exercer les saintes fonctions de l'Évangile de Dieu, afin que l'oblation des Gentils lui soit agréable, étant sanctifiée par le Saint-Esprit.
17 Don haka ina jin dadi cikin Yesu Almasihu da abubuwa na Allah.
J'ai donc un sujet de gloire en Jésus-Christ, dans les choses de Dieu.
18 Domin ba ni da abin da zan ce, sai abin da Yesu ya aikata ta wurina, domin Al'ummai su yi biyayya ta magana da aiki.
Car je n'oserais parler de quoi que ce soit que Christ n'ait opéré par moi, pour amener les Gentils à son obéissance, par la parole et par les ouvres;
19 Ta wurin alamu, da al'jibai, da ikon Ruhu Mai Tsarki. Daga Urushalima, da kewaye har zuwa Ilirikum, an kai bisharar Almasihu ko'ina dukka.
Par la vertu des miracles et des prodiges; par la puissance de l'Esprit de Dieu; de sorte que j'ai répandu l'Évangile de Christ depuis Jérusalem et les lieux voisins, jusqu'à l'Illyrie.
20 A cikin hanyar nan, burina in sanar da bishara, amma a inda ba a san Yesu ta wurin sunansa ba, don kada in sa gini akan harshashi wani.
Prenant ainsi à tâche d'annoncer l'Évangile où Christ n'avait point été nommé, afin de ne pas bâtir sur le fondement qu'un autre aurait posé;
21 Kamar yadda yake a rubuce.”Wadanda ba a taba fada wa labarinsa ba, su gane. Wadanda ba su taba jin labarinsa ba su fahimta.”
Selon qu'il est écrit: Ceux à qui il n'avait point été annoncé, le verront, et ceux qui n'en avaient point entendu parler, l'entendront.
22 Saboda an hana ni zuwa wurin ku a lokatai da dama.
C'est pour cela que j'ai été souvent empêché d'aller chez vous.
23 Amma yanzu bani da sauran wani wuri a lardin nan, kuma cikin shekaru masu yawa ina da marmarin in zo wurin ku.
Mais, comme à présent je n'ai plus affaire dans ce pays-ci, et que depuis plusieurs années j'ai un grand désir d'aller vers vous,
24 Duk lokacin da zan tafi Asbaniya ina begen ganin ku yayin wucewa, don ku raka ni bayan na ji dadin zama da ku na dan lokaci.
Quand je me rendrai en Espagne, j'irai chez vous; car j'espère que je vous verrai en passant, et que vous m'y ferez conduire, après que j'aurai satisfait en partie mon désir d'être avec vous.
25 Amma yanzu ina tafiya Urushalima don in yi wa tsarkaka hidima.
Mais maintenant je vais à Jérusalem, pour assister les Saints.
26 Domin abin farinciki ne ga mutanen Makidoniya da Akaya su yi bayarwa domin gajiyayyu masu bada gaskiya wadanda suke a Urushalima.
Car il a plu à ceux de Macédoine et d'Achaïe de s'imposer une contribution pour les pauvres d'entre les Saints de Jérusalem.
27 Suna jin dadi domin hakika kamar bashi ne a kansu. Domin Al'ummai sun yi tarayya da su cikin ayyukan ruhaniya, ya zama hakki a kansu su ma su taimake su da abubuwa.
Il leur a plu, en effet, et ils le leur devaient; car, si les Gentils ont eu part à leurs biens spirituels, ils doivent aussi les assister dans les choses temporelles.
28 Domin lokacin da na gama basu kudin, zan zo gareku a hanyata ta zuwa Asbaniya.
Après donc que j'aurai achevé cela, et que je leur aurai remis fidèlement ce produit, je partirai pour l'Espagne, en passant par chez vous.
29 Na san cewa lokacin da na zo gareku, zan zo da cikakkun albarku na Almasihu.
Or, je sais qu'en me rendant auprès de vous, je viendrai avec la plénitude des bénédictions de l'Évangile de Christ.
30 Yanzu ina rokonku, yan'uwa, ta wurin Ubangiji Yesu Almasihu, da kaunar Ruhu Mai Tsarki, ku yi ta fama tare da ni a cikin yin addu'o, inku ga Allah saboda ni.
Je vous conjure donc, frères, par notre Seigneur Jésus-Christ, et par l'amour de l'Esprit, de combattre avec moi dans les prières que vous ferez à Dieu pour moi;
31 Kuyi haka saboda in tsira daga wadanda suke masu biyayya ga Yahudiya, domin kuma hidimata saboda Urushalima ta zama karbabbiya.
Afin que je sois délivré des incrédules de Judée, et que mon ministère à Jérusalem soit agréable aux Saints;
32 Ku yi addu'a cewa in zo wurinku da farinciki ta wurin nufin Allah, cewa tare da ni da ku, mu sami hutu.
En sorte que, par la volonté de Dieu, j'arrive chez vous avec joie, et que je me repose avec vous.
33 Allah na salama ya kasance tare da ku duka. Amin.
Que le Dieu de paix soit avec vous tous! Amen.

< Romawa 15 >