< Romawa 11 >
1 Sai na ce, Allah ya ki mutanensa ne? Ba zai taba yiwuwa ba. Domin ni ma ba-Isra'ile ne, na zuriyar Ibrahim, a kabilar Bilyaminu.
I say then, Has God cast away his people? God forbid. For I also am an Israelite, of the seed of Abraham, of the tribe of Benjamin.
2 Allah bai ki mutanen sa da ya ke da rigyasaninsu ba. Ko kun san abin da nassi ya ce game da Iliya, yadda ya kai karar Isra'ila a gaban Allah?
God has not cast away his people which he foreknew. Know you not what the scripture says of Elijah? how he makes intercession to God against Israel saying,
3 Ya ce, ''Ubangiji, sun kashe annabawanka, sun rushe alfarwanka kuma, Ni kadai ne na rage, ga shi suna neman su kashe ni.''
Lord, they have killed your prophets, and dig down your altars; and I am left alone, and they seek my life.
4 Amma wacce amsa ce Allah ya ba shi? Ya ce, ''Ina da mutane dubu bakwai da na kebe don kaina, da ba su taba rusuna wa Ba'al ba.''
But what says the answer of God to him? I have reserved to myself seven thousand men, who have not bowed the knee to the image of Baal.
5 Ban da haka ma, ban da haka ma a wannan lokacin akwai sauran zabe na alheri.
Even so then at this present time also there is a remnant according to the election of grace.
6 Amma tun da ta wurin alheri ne, ba ga ayyuka ba. In ba haka ba, alheri ba zai zama alheri ba kenan.
And if by grace, then is it no more of works: otherwise grace is no more grace. But if it be of works, then it is no more grace: otherwise work is no more work.
7 Sai kuma me? Abin da Isra'ila ke nema, ba su samu ba, amma zababbun sun same shi, saura kuma sun taurare.
What then? Israel has not obtained that which he seeks for; but the election has obtained it, and the rest were blinded.
8 Kamar yadda yake a rubuce, ''Allah ya ba su ruhun rashin fahimta, ga idanu amma ba za su gani ba, ga kunnuwa amma ba za su ji ba, har zuwa wannan rana.''
(According as it is written, God has given them the spirit of slumber, eyes that they should not see, and ears that they should not hear; ) to this day.
9 Dauda kuma ya ce, ''bari teburinsu ya zama taru, da tarko, ya zama dutsen tuntube da abin ramako a gare su.
And David says, Let their table be made a snare, and a trap, and a stumbling block, and a recompense to them:
10 Bari idanunsu ya duhunta domin kada su gani; bayansu kuma a duke kullum.''
Let their eyes be darkened, that they may not see, and bow down their back always.
11 Na ce, ''sun yi tuntube domin su fadi ne?'' Kada abu kamar haka ya faru. A maimakon haka, juyawa baya da suka yi ya sa, ceto ya zo ga Al'ummai, domin ya sa su kishi.
I say then, Have they stumbled that they should fall? God forbid: but rather through their fall salvation is come to the Gentiles, for to provoke them to jealousy.
12 Idan yanzu juyawa baya da sun yi ya zama arziki ga duniya, rashin su kuma arziki ga Al'ummai, yaya kwatancin girmansa zai kasance in sun zo ga kammala?
Now if the fall of them be the riches of the world, and the diminishing of them the riches of the Gentiles; how much more their fullness?
13 Yanzu ina magana da ku ku da ke Al'ummai. Tunda yake ni ne manzo ga Al'ummai, ina kuma fahariya cikin hidimata.
For I speak to you Gentiles, inasmuch as I am the apostle of the Gentiles, I magnify my office:
14 Yana yiwuwa in sa ''yan'uwa na kishi, domin mu ceci wadansu su.
If by any means I may provoke to emulation them which are my flesh, and might save some of them.
15 Idan kinsu ya kawo sulhuntawa ga duniya, Karbarsu kuma zata zama yaya? Zata zama rai ne daga mutuwa.
For if the casting away of them be the reconciling of the world, what shall the receiving of them be, but life from the dead?
16 'ya'yan farko sunan haka ma kakkabensu yake, Idan saiwar itace na nan, haka ma rassan za su zama.
For if the first fruit be holy, the lump is also holy: and if the root be holy, so are the branches.
17 Amma idan an karye wasu daga cikin rassan, idan ku rassan zaitun na ainihi ne, da aka samu daga cinkinsu, kuma idan kuna da gado tare da su, acikin saiwar itacen zaitun din.
And if some of the branches be broken off, and you, being a wild olive tree, were grafted in among them, and with them partake of the root and fatness of the olive tree;
18 Kada ku yi fahariya a kan rassan. Amma idan kuka yi fahariya to ba ku bane masu karfafa saiwar amma saiwar ce ke karfafa ku.
Boast not against the branches. But if you boast, you bore not the root, but the root you.
19 Kana iya cewa, ''An karye rassan domin a same ni a ciki.''
You will say then, The branches were broken off, that I might be grafted in.
20 Wannan gaskiya ne! Saboda rashin bangaskiyarsu ne ya sa aka karye su daga rassan, amma ku tsaya da karfi acikin bangaskiyarku. Kada ku dauki kanku fiye da yadda ya kamata, amma ku ji tsoro.
Well; because of unbelief they were broken off, and you stand by faith. Be not high minded, but fear:
21 Domin idan Allah bai bar ainihin rassan ba, to ba zai bar ku ba.
For if God spared not the natural branches, take heed lest he also spare not you.
22 Ku duba yadda irin ayyuka masu tsananni na Allah. Ta daya hannun kuma, tsanannin kan zoa kan Yahudawa wadanda suka fadi. Har 'ila yau jinkai Allah ya zo maku, idan kun cigaba cikin alherinsa baza a sare ku ba. Amma in kun ki za a sare ku.
Behold therefore the goodness and severity of God: on them which fell, severity; but toward you, goodness, if you continue in his goodness: otherwise you also shall be cut off.
23 Hakanan, idan ba su ci gaba cikin rashin bangaskiyarsu ba, za a maida su cikin itacen. Domin Allah zai iya sake maida su.
And they also, if they abide not still in unbelief, shall be grafted in: for God is able to graft them in again.
24 Idan an yanke ka daga itacen zaitun da ke na jeji, har ya yiwu an hada ka cikin itacen zaitun na ainihi, yaya kuma wadannan Yahudawa wadanda sune ainihin rassan, da za'a maido cikin zaitun da ke na ainihi?
For if you were cut out of the olive tree which is wild by nature, and were grafted contrary to nature into a good olive tree: how much more shall these, which be the natural branches, be grafted into their own olive tree?
25 Yan'uwa, ba na so ku kasance cikin duhu a game da wannan asirin, domin kada ku zama da hikima cikin tunaninku. Wannan asirin shine cewa wannan taurarewa ta faru a Isra'ila, har sai da Al'ummai suka shigo ciki.
For I would not, brothers, that you should be ignorant of this mystery, lest you should be wise in your own conceits; that blindness in part is happened to Israel, until the fullness of the Gentiles be come in.
26 Ta haka dukan Isra'ila za su tsira, kamar yadda yake a rubuce: ''Daga cikin Sihiyona mai Kubutarwa zai fito; Zai kawar da kazanta daga cikin Yakubu.
And so all Israel shall be saved: as it is written, There shall come out of Sion the Deliverer, and shall turn away ungodliness from Jacob:
27 Wannan zai zama alkawarina da su, sa'adda na kawar da zunubansu.''
For this is my covenant to them, when I shall take away their sins.
28 A wani bangaren kuma game da bishara, su makiya ne amamadinku, ta wani fannin kuma bisa ga zabin Allah su kaunattatu ne saboda ubanni.
As concerning the gospel, they are enemies for your sakes: but as touching the election, they are beloved for the father’s sakes.
29 Domin baye-baye da kiran Allah basa canzawa.
For the gifts and calling of God are without repentance.
30 Domin ku ma da ba ku yin biyayya ga Allah, amma yanzu kun sami jinkai saboda rashin biyayyarsu.
For as you in times past have not believed God, yet have now obtained mercy through their unbelief:
31 Ta wannan hanyar dai, wadannan Yahudawan sun zama marasa biyayya. Sakamakon haka shine ta wurin jinkan da aka nuna maku, suma su samu jikai yanzu.
Even so have these also now not believed, that through your mercy they also may obtain mercy.
32 Domin Allah ya rufe kowa ga rashin biyayya, domin ya nuna jinkai ga kowa. (eleēsē )
For God has concluded them all in unbelief, that he might have mercy on all. (eleēsē )
33 Ina misalin zurfin wadata da kuma hikima da sani na Allah! Hukunce-hukuncensa sun fi gaban a bincika, hanyoyinsa kuma sun fi gaban ganewa!
O the depth of the riches both of the wisdom and knowledge of God! how unsearchable are his judgments, and his ways past finding out!
34 Don wanene ya san tunanin Ubangiji? Wanene kuma ya zama mai bashi shawara?
For who has known the mind of the Lord? or who has been his counselor?
35 Ko kuma, wanene ya fara ba Allah wani abu, domin a biya shi?''
Or who has first given to him, and it shall be recompensed to him again?
36 Daga wurinsa ne, ta wurinsa ne kuma, a gare shi ne kuma dukan abu suka fito. A gare shi daukaka ta tabbata har abada. Amin. (aiōn )
For of him, and through him, and to him, are all things: to whom be glory for ever. Amen. (aiōn )