< Romawa 10 >

1 'Yan'uwana, muradin zuciyata da dukkan addu'oi na ga Allah dominsu shine don su sami ceton.
Brødre! mit Hjertes Ønske og Bøn til Gud for dem er om deres Frelse.
2 Domin na shaida game da su cewa suna da kwazo game da Allah, amma ba a kan sani ba.
Thi jeg giver dem det Vidnesbyrd, at de have Nidkærhed for Gud, men ikke med Forstand;
3 Don, ba su da sani akan adalcin Allah, suna kokarin tabbatar da adalcin kansu. Ba su bada kan su ga adalcin Allah ba.
thi da de ikke kendte Guds. Retfærdighed og tragtede efter at opstille deres egen Retfærdighed, så bøjede de sig ikke under Guds Retfærdighed.
4 Gama Almasihu shi ne cikar doka zuwa ga adalci ga dukkan wadanda suka gaskata.
Thi Kristus er Lovens Ende til Retfærdighed for hver den, som tror.
5 Musa kam ya rubuta game da adalci da zai samu ta shari'a: ''mutumin da ya aikata adalcin shari'a, zai rayu ta wurin wannan adalcin.''
Moses skriver jo, at det Menneske, som gør den Retfærdighed, der er af Loven, skal leve ved den.
6 Amma adalcin da ya zo ta wurin bangaskiya yace, ''Kada ku ce a zuciyarku, wa zai hau zuwa sama?''(don ya sauko da Almasihu kasa).
Men Retfærdigheden af Tro siger således: Sig ikke i dit Hjerte: Hvem vil fare op til Himmelen? nemlig for at hente Kristus ned;
7 Kada ku ce, ''Wa zai gangara zuwa kasa?'' (Wato wa zai fito da Almasihu daga cikin matattu). (Abyssos g12)
eller: Hvem vil fare ned i Afgrunden? nemlig for at hente Kristus op fra de døde. (Abyssos g12)
8 Amma me yake cewa? “kalmar tana kusa da kai a cikin bakinka da kuma cikin zuciyarka.” Wato kalmar bangaskiya, wadda muke shaidawa.
Men hvad, siger den? Ordet er dig nær, i din Mund og i dit Hjerte, det er det Troens Ord, som vi prædike.
9 Don idan da bakinka, ka shaida Yesu Ubangiji ne, kuma ka gaskata a zuciyarka cewa Allah ya tashe shi daga matattu, za ka sami ceto.
Thi dersom du med din Mund bekender Jesus som Herre og tror i dit Hjerte, at Gud oprejste ham fra de døde, da skal du blive frelst.
10 Don da zuciya ne mutum yake gaskatawa zuwa ga adalci, da kuma baki ne yake shaida zuwa ga ceto.
Thi med Hjertet tror man til Retfærdighed, og med Munden bekender man til Frelse.
11 Don nassi na cewa, ''Duk wanda ya gaskata da shi ba zai ji kunya ba,''
Skriften siger jo: "Hver den, som tror på ham, skal ikke blive til Skamme."
12 Gama ba bambanci tsakanin Bayahude da Ba'al'ume. Gama dukkansu Ubangijinsu daya ne, Shi mayalwaci ne ga dukkan wanda ya kira shi.
Thi der er ikke Forskel på Jøde og Græker; thi den samme er alles Herre, rig nok for alle dem, som påkalde ham.
13 Duk wanda ya kira sunan Ubangiji zai sami ceto.
Thi hver den, som påkalder Herrens Navn, skal blive frelst.
14 To ta yaya zasu kira ga wanda basu gaskata ba? Kuma ta yaya zasu gaskata ga wanda ba su taba jin labarinsa ba?
Hvorledes skulde de nu påkalde den, på hvem de ikke have troet? og hvorledes skulde de tro den, som de ikke have hørt? og hvorledes skulde de høre, uden der er nogen, som prædiker?
15 Kuma ta yaya zasu ji in ba ayi masu wa'azi ba? Kuma ta yaya zasu yi wa'azin in ba an aike su ba? - Kamar yadda yake a rubuce, “Ina misalin kyau na kafafun wadanda ke shaida labarin farin ciki na abubuwa masu kyau!”
og hvorledes skulde de prædike, dersom de ikke bleve udsendte? Som der er skrevet: "Hvor dejlige. ere deres Fødder, som forkynde godt Budskab."
16 Amma ba dukkansu ne suka ji bishara ba. Gama Ishaya ya ce, ''Ubangiji, wa ya gaskata da sakon?
Dog ikke alle løde Evangeliet; thi Esajas siger: "Herre! hvem troede det, (han hørte af os?")
17 Saboda haka bangaskiya na zuwa ta wurin ji, jin kuwa daga maganar Almasihu.
Altså kommer Troen af det. som høres, men det, som høres, kommer igennem Kristi Ord.
18 Amma na ce, “ko basu ji ba ne? I, tabbas'' muryarsu ta kai dukkan duniya, kuma kalmominsu sun kai har karshen duniya.''
Men jeg siger: Have de ikke hørt? Jo vist, "over hele Jorden er deres Røst udgået og til Jorderiges Grænser deres Ord."
19 yau, na ce, ''Ko Isra'ila basu sani ba ne?'' Da farko Musa ya ce, “Zan sa kuyi fushi da kishi da abin da ba al'umma ba. Abin da nake nufi nan shine al'ummar da basu da fahinta, zan more su, in tayar maku da hankali.''
Men jeg siger: Har Israel ikke forstået det? Først siger Moses: "Jeg vil gøre eder nidkære på et Folk, som ikke er et Folk, imod et uforstandigt Folk vil jeg opirre eder."
20 Amma Ishaya da karfin hali ya ce, ''Ga wadanda basu neme ni ba suka same ni. Na bayyana ga wadanda basu nemi ni ba.
Men Esajas drister sig til at sige: "Jeg blev funden af dem, som ikke søgte mig; jeg blev åbenbar for dem. som ikke spurgte efter mig."
21 ''Amma ga Isra'ila kam ya ce, '' na mika hannu na ga masu rashin biyayya dukkan tsawon rana, domin su mutane ne masu taurin kai.''
Men om Israel siger han: "Den hele Dag udstrakte jeg mine Hænder imod et ulydigt og genstridigt Folk."

< Romawa 10 >