< Romawa 1 >
1 Bulus, bawan Yesu Almasihu, kirayayye ya zama manzo, kuma kebabbe domin bisharar Allah.
Paul, a servant of Jesus Christ, called to be an apostle and set apart for the gospel of God,
2 Wannan itace bisharar da ya alkawarta tuntuni ta wurin annabawansa ta wurin tsarkakakkun littattafan sa.
which he promised beforehand by his prophets in the holy scriptures,
3 Game da Dansa ne, haifaffe daga zuriyar Dauda ga zancen jiki.
concerning his Son who was a descendant of David according to the flesh.
4 Ta wurin tashinsa daga mattatu aka aiyana shi ya zama Dan Allah ta wurin ikon Ruhu na tsarkakewa. Yesu Almasihu Ubangijimu.
Through the Spirit of holiness he was declared with power to be the Son of God by the resurrection from the dead, Jesus Christ our Lord.
5 Ta wurinsa muka karbi alheri da manzanci sabo da biyayyar imani a cikin dukkan al'ummai, domin darajar sunansa.
Through him we have received grace and apostleship for obedience of faith among all the nations, for the sake of his name.
6 cikin wadannan al'ummai kwa, ku ma an kiraku ku zama na Yesu Almasihu.
Among these nations, you also have been called to belong to Jesus Christ.
7 Wannan wasika ga dukkanku ne da kuke cikin Roma, kaunatattu na Allah, kirayayyun mutane tsarkakakku. Bari alheri ya kasance tare daku, da salama daga Allah Ubanmu, da kuma Ubangiji Yesu Almasihu.
This letter is to all who are in Rome, the beloved of God, who are called to be holy people. May grace be to you, and peace from God our Father and the Lord Jesus Christ.
8 Abu na farko dai ina yi wa Allah na godiya ta wurin Yesu Almasihu domin ku duka, domin kuwa ana labarta bangaskiyarku ko ina a cikin dukkan duniya.
First, I thank my God through Jesus Christ for all of you, because your faith is proclaimed throughout the whole world.
9 Domin kuwa Allah shi ne shaida ta, wanda nake bautawa a cikin ruhuna a cikin bisharar Dansa, yadda a koyaushe na ke ambaton ku.
For God is my witness, whom I serve in my spirit in the gospel of his Son, of how continually I make mention of you.
10 A kullum ina roko cikin addu'o'ina domin ta kowanne hali in yi nasarar zuwa gare ku da izinin Allah.
I always request in my prayers that by any means I may at last be successful now by the will of God in coming to you.
11 Gama ina marmarin ganin ku, domin in baku wata baiwa ta ruhaniya, domin in karfafa ku.
For I desire to see you, that I may give you some spiritual gift, in order to strengthen you.
12 Wato ina dokin in sami cikakkiyar karfafawa a cikin ku, ta wurin bangaskiyar junanmu, wato tawa da taku.
That is, I long to be mutually encouraged among you, through each other's faith, yours and mine.
13 Yanzu fa bana so ku rasa sani, yan'uwa, sau da yawa nake yin niyyar zuwa wurinku, amma har yanzu hakan din bata samu ba. Na so yin hakan din ne don in sami 'ya'ya na ruhu a cikinku kamar dai yadda ya ke a sauran Al'ummai.
Now I do not want you to be uninformed, brothers, that I often intended to come to you, (but I was hindered until now), in order to have a harvest among you, just as I have had among the rest of the Gentiles.
14 Ina dauke da nawayar Hellinawa da ta sauran jama'a, masu hikima da marasa hikima.
I am a debtor both to Greeks and to foreigners, both to the wise and to the foolish.
15 Don a shirye na ke in sanar da bishara a gare ku, ku da kuke cikin Roma.
So, as for me, I am ready to proclaim the gospel also to you who are in Rome.
16 Don kuwa ni ba na jin kunyar yin bishara, don ita ce ikon Allah don samun ceto ga duk wanda ya gaskata, da farko dai Yahudawa kana kuma Hellinawa,
For I am not ashamed of the gospel, for it is the power of God for salvation for everyone who believes, for the Jew first and for the Greek.
17 Domin a cikin ta adalcin Allah ya bayyana daga bangaskiy zuwa bangaskiya, kamar yadda yake a rubuce, “Mai adalci zai rayu ne tawurin bangaskiya.”
For in it God's righteousness is revealed from faith to faith, as it has been written, “The righteous will live by faith.”
18 Domin fushin Allah ya bayyana ne daga sama gaba da rashin ibada da rashin adalci na yan'adam, wadanda suke danne gaskiya ta wurin rashin adalcin su.
For the wrath of God is revealed from heaven against all ungodliness and unrighteousness of people, who through unrighteousness hold back the truth.
19 Dalili kuwa abinda yakamata a sani game da Allah a bayyane ya ke a gare su. Domin kuwa Allah ya bayyana masu shi a zahiri.
This is because that which is known about God is visible to them. For God has enlightened them.
20 Domin al'amuransa da ba'a iya gani a bayyane suke tun halittar duniya. A na iya gane su ta wurin halitatattun abubuwa. Wadannan al'amura kuwa sune madawwamin ikonsa da Allahntakarsa. Sakamakon haka, wadannan mutane ba su da hujja. (aïdios )
For his invisible qualities, namely his eternal power and divine nature, have been clearly seen, ever since the creation of the world, in the things that have been made. So they are without excuse. (aïdios )
21 Dalili kuwa, koda suna jin sun san Allah, amma basu darajanta shi a matsayin Allah ba, ko kuma su nuna masa godiya. Maimakon haka, suka zama wawaye a cikin tunaninsu, zukatansu marasa tunani sun duhunta.
This is because, although they knew about God, they did not glorify him as God, nor did they give him thanks. Instead, they became foolish in their thoughts, and their senseless hearts were darkened.
22 Suna daukar kansu akan masu hikima ne su, amma sai ga su sun zama wawaye.
They claimed to be wise, but they became foolish.
23 Sun musanya daukakar Allah madawwami da ta kamannin abubuwan da basa dawwama, kamar mutum, da tsuntsaye, da dabbobi masu kafafu hurhudu, da masu jan ciki.
They exchanged the glory of the imperishable God for the likenesses of an image of perishable man, of birds, of four-footed beasts, and of creeping things.
24 Saboda haka Allah ya bashe su ga sha'awoyin kazantar zukatansu, su wulakantar da jukunansu a junansu.
Therefore God gave them over to the lusts of their hearts for uncleanness, for their bodies to be dishonored among themselves.
25 Sune suka musanya gaskiyar Allah da karya, Kuma suke sujada da bauta ga halittaccen abu, maimakon Mahaliccin, Wanda yake abin yabo har abada. Amin. (aiōn )
It is they who exchanged the truth of God for a lie, and who worshiped and served the creation instead of the Creator, who is praised forever. Amen. (aiōn )
26 Saboda haka Allah ya bashe su, ga sha'awowin su na lalata da wulakanci, har matansu suka canza ka'idar jima'i da aka saba zuwa madigo mace da mace.
Because of this, God gave them over to dishonorable passions, for their women exchanged natural relations for those that were unnatural.
27 Mazajensu ma suka sauya ka'idar jima'i tsakanin mace da miji zuwa namiji da namiji suna yin aikin lalata. Maza su na kwana da maza suna aikata aikin ban kyama, suna kuwa girbe sakamakon aiknsu na ban kyama.
Likewise, the men also left their natural relations with women and burned in their lust for one another. These were men who committed shameless acts with men and received in themselves the penalty they deserved for their error.
28 Tunda shike ba su amince da Allah a cikkin al'amuransu ba, Allah ya bashe su ga bataccen hankalinsu, su aikata wadannan munanan abubuwa.
Because they did not approve of having God in their awareness, he gave them up to a depraved mind, for them to do those things that are not proper.
29 Suna cike da dukkan rashin adalci, mugunta, kyashi, keta, kuma cike da kishi, kisan kai, tarzoma, makirci, da kuma munanan manufafofi.
They have been filled with all unrighteousness, wickedness, covetousness, and malice. They are full of envy, murder, strife, deceit, and evil intentions. They are gossips,
30 Masu gulma da kage, makiyan Allah. Masu tada zaune tsaye, masu taurin kai, da ruba, masu kaga kowadanne miyagun abubuwa, kuma masu kin yin biyayya ga iyayensu.
slanderers, haters of God, insolent, arrogant, boastful, inventing ways of doing evil; they are disobedient to parents.
31 Masu duhun zuciya; masu cin amana, marasa soyayya, da kuma rashin tausayi.
They are senseless, faithless, heartless, and unmerciful.
32 Suna sane da tsarin Allah cewa masu yin irin wadannan al'amura sun cancanci hukuncin mutuwa. Ba kuwa yin wadannan abubuwan ka dai suke yi ba, harma goyon bayan masu yinsu suke yi.
They understand the regulations of God, that those who practice such things are deserving of death. But not only do they do these things, they also approve of others who do them.