< Romawa 1 >
1 Bulus, bawan Yesu Almasihu, kirayayye ya zama manzo, kuma kebabbe domin bisharar Allah.
Paul the seruaut of Iesus Christ called to be an Apostle put a parte to preache the Gospell of God
2 Wannan itace bisharar da ya alkawarta tuntuni ta wurin annabawansa ta wurin tsarkakakkun littattafan sa.
which he promysed afore by his Prophetes in the holy scriptures
3 Game da Dansa ne, haifaffe daga zuriyar Dauda ga zancen jiki.
that make mension of his sonne the which was begotte of the seed of David as pertayninge to the flesshe:
4 Ta wurin tashinsa daga mattatu aka aiyana shi ya zama Dan Allah ta wurin ikon Ruhu na tsarkakewa. Yesu Almasihu Ubangijimu.
and declared to be the sonne of God with power of the holy goost that sanctifieth sence ye tyme that Iesus Christ oure Lorde rose agayne from deeth
5 Ta wurinsa muka karbi alheri da manzanci sabo da biyayyar imani a cikin dukkan al'ummai, domin darajar sunansa.
by whom we have receaved grace and apostleshyppe to bringe all maner hethe people vnto obedience of the fayth that is in his name:
6 cikin wadannan al'ummai kwa, ku ma an kiraku ku zama na Yesu Almasihu.
of the which hethen are ye a part also which are Iesus christes by vocacio.
7 Wannan wasika ga dukkanku ne da kuke cikin Roma, kaunatattu na Allah, kirayayyun mutane tsarkakakku. Bari alheri ya kasance tare daku, da salama daga Allah Ubanmu, da kuma Ubangiji Yesu Almasihu.
To all you of Rome beloved of God and saynctes by callinge. Grace be with you and peace from God oure father and from the Lorde Iesus Christ.
8 Abu na farko dai ina yi wa Allah na godiya ta wurin Yesu Almasihu domin ku duka, domin kuwa ana labarta bangaskiyarku ko ina a cikin dukkan duniya.
Fyrst verely I thanke my God thorow Iesus Christ for you all because youre fayth is publisshed through out all the worlde.
9 Domin kuwa Allah shi ne shaida ta, wanda nake bautawa a cikin ruhuna a cikin bisharar Dansa, yadda a koyaushe na ke ambaton ku.
For God is my witnes whom I serve with my sprete in the Gospell of his sonne that with out ceasinge I make mencion of you alwayes in my prayers
10 A kullum ina roko cikin addu'o'ina domin ta kowanne hali in yi nasarar zuwa gare ku da izinin Allah.
besechinge that at one tyme or another a prosperous iorney (by ye will of god) myght fortune me to come vnto you.
11 Gama ina marmarin ganin ku, domin in baku wata baiwa ta ruhaniya, domin in karfafa ku.
For I longe to see you that I myght bestowe amoge you some spirituall gyfte to strength you with all:
12 Wato ina dokin in sami cikakkiyar karfafawa a cikin ku, ta wurin bangaskiyar junanmu, wato tawa da taku.
that is that I myght have consolacion together with you through the commen fayth which bothe ye and I have.
13 Yanzu fa bana so ku rasa sani, yan'uwa, sau da yawa nake yin niyyar zuwa wurinku, amma har yanzu hakan din bata samu ba. Na so yin hakan din ne don in sami 'ya'ya na ruhu a cikinku kamar dai yadda ya ke a sauran Al'ummai.
I wolde that ye shuld knowe brethre how that I have often tymes purposed to come vnto you (but have bene let hitherto) to have some frute amonge you as I have amonge other of ye Gentyls.
14 Ina dauke da nawayar Hellinawa da ta sauran jama'a, masu hikima da marasa hikima.
For I am detter both to the Grekes and to them which are no Grekes vnto the learned and also vnto the vnlearned.
15 Don a shirye na ke in sanar da bishara a gare ku, ku da kuke cikin Roma.
Lykewyse as moche as in me is I am redy to preache the Gospell to you of Rome also.
16 Don kuwa ni ba na jin kunyar yin bishara, don ita ce ikon Allah don samun ceto ga duk wanda ya gaskata, da farko dai Yahudawa kana kuma Hellinawa,
For I am not ashamed of the Gospell of Christ because it is ye power of God vnto salvacio to all yt beleve namely to the Iewe and also to ye getyle.
17 Domin a cikin ta adalcin Allah ya bayyana daga bangaskiy zuwa bangaskiya, kamar yadda yake a rubuce, “Mai adalci zai rayu ne tawurin bangaskiya.”
For by it ye rightewesnes which cometh of god is opened fro fayth to fayth. As it is written: The iust shall live by fayth.
18 Domin fushin Allah ya bayyana ne daga sama gaba da rashin ibada da rashin adalci na yan'adam, wadanda suke danne gaskiya ta wurin rashin adalcin su.
For the wrath of God apereth from heven agaynst all vngodlynes and vnrightewesnes of me which withholde ye trueth in vnrightewesnes
19 Dalili kuwa abinda yakamata a sani game da Allah a bayyane ya ke a gare su. Domin kuwa Allah ya bayyana masu shi a zahiri.
seynge what maye be knowen of God that same is manifest amoge them. For God dyd shewe it vnto them.
20 Domin al'amuransa da ba'a iya gani a bayyane suke tun halittar duniya. A na iya gane su ta wurin halitatattun abubuwa. Wadannan al'amura kuwa sune madawwamin ikonsa da Allahntakarsa. Sakamakon haka, wadannan mutane ba su da hujja. (aïdios )
So that his invisible thinges: that is to saye his eternall power and godhed are vnderstonde and sene by the workes from the creacion of the worlde. So that they are without excuse (aïdios )
21 Dalili kuwa, koda suna jin sun san Allah, amma basu darajanta shi a matsayin Allah ba, ko kuma su nuna masa godiya. Maimakon haka, suka zama wawaye a cikin tunaninsu, zukatansu marasa tunani sun duhunta.
in as moche as when they knewe god they glorified him not as God nether were thakfull but wexed full of vanities in their imaginacions and their folisshe hertes were blynded.
22 Suna daukar kansu akan masu hikima ne su, amma sai ga su sun zama wawaye.
When they couted them selves wyse they became foles
23 Sun musanya daukakar Allah madawwami da ta kamannin abubuwan da basa dawwama, kamar mutum, da tsuntsaye, da dabbobi masu kafafu hurhudu, da masu jan ciki.
and turned the glory of the immortall god vnto the similitude of the ymage of mortall man and of byrdes and foure foted beastes and of serpentes.
24 Saboda haka Allah ya bashe su ga sha'awoyin kazantar zukatansu, su wulakantar da jukunansu a junansu.
Wherfore god lykewyse gave the vp vnto their hertes lustes vnto vnclennes to defyle their awne boddyes bitwene them selves:
25 Sune suka musanya gaskiyar Allah da karya, Kuma suke sujada da bauta ga halittaccen abu, maimakon Mahaliccin, Wanda yake abin yabo har abada. Amin. (aiōn )
which tourned his truthe vnto a lye and worshipped and served the creatures more then ye maker which is blessed for ever. Ame. (aiōn )
26 Saboda haka Allah ya bashe su, ga sha'awowin su na lalata da wulakanci, har matansu suka canza ka'idar jima'i da aka saba zuwa madigo mace da mace.
For this cause god gave them vp vnto shamfull lustes. For even their wemen did chaunge the naturall vse vnto the vnnaturall.
27 Mazajensu ma suka sauya ka'idar jima'i tsakanin mace da miji zuwa namiji da namiji suna yin aikin lalata. Maza su na kwana da maza suna aikata aikin ban kyama, suna kuwa girbe sakamakon aiknsu na ban kyama.
And lyke wyse also the men lefte the naturall vse of the woma and bret in their lustes one on another. And man with man wrought filthynes and receaved in them selves the rewarde of their erroure as it was accordinge.
28 Tunda shike ba su amince da Allah a cikkin al'amuransu ba, Allah ya bashe su ga bataccen hankalinsu, su aikata wadannan munanan abubuwa.
And as it semed not good vnto them to be aknowen of God even so God delivered them vp vnto a leawde mynd yt they shuld do tho thinges which were not comly
29 Suna cike da dukkan rashin adalci, mugunta, kyashi, keta, kuma cike da kishi, kisan kai, tarzoma, makirci, da kuma munanan manufafofi.
beinge full of all vnrighteous doinge of fornicacio wickednes coveteousnes maliciousnes full of envie morther debate disseyte evill codicioned whisperers
30 Masu gulma da kage, makiyan Allah. Masu tada zaune tsaye, masu taurin kai, da ruba, masu kaga kowadanne miyagun abubuwa, kuma masu kin yin biyayya ga iyayensu.
backbyters haters of God doers of wroge proude bosters bringers vp of evyll thinges disobedient to father and mother
31 Masu duhun zuciya; masu cin amana, marasa soyayya, da kuma rashin tausayi.
with out vnderstondinge covenaunte breakers vnlovinge trucebreakers and merciles.
32 Suna sane da tsarin Allah cewa masu yin irin wadannan al'amura sun cancanci hukuncin mutuwa. Ba kuwa yin wadannan abubuwan ka dai suke yi ba, harma goyon bayan masu yinsu suke yi.
Which me though they knew the rightewesnes of God how that they which soche thinges commyt are worthy of deeth yet not only do the same but also have pleasure in them that do them.