< Ru’uya ta Yohanna 1 >

1 Wannan shine wahayin Yesu Almasihu da Allah ya bashi ya nuna wa bayinsa abinda zai faru ba da dadewa ba. Ya bayyana wannan ta wurin aiko da mala'ikansa ga bawansa Yahaya.
[The] revelation of Jesus Christ which gave to him God to show to the bond-servants of Him what things it behooves to take place with speed And He signified [it] having sent through the angel of Him to the servant of Him John,
2 Yahaya yayi shaida akan abinda ya gani game da maganar Allah da kuma shaidar da aka bayar game da Yesu Almasihu.
who testified to the word of God and to the testimony of Jesus Christ as much as (then *k*) he saw.
3 Mai albarka ne wanda ke karanta littafin nan da murya mai karfi, da kuma wadanda ke sauraron kalmomin wannan annabci kuma suke biyayya da abinda aka rubuta a ciki, domin kuwa lokaci ya kusato.
blessed [is] the [one] reading and those hearing the words of the prophecy and keeping the [things] in it written; for the time [is] near.
4 Ni Yahaya, zuwa ga ikilisiyoyi bakwai na kasar Asiya: alheri zuwa gare ku da salama daga wanda ke yanzu, wanda ya kuma kasance a da, shi ne kuma mai zuwa nan gaba, kuma daga ruhohin nan bakwai da ke gaban kursiyinsa,
John To the seven churches in Asia: Grace to you and peace from (Him *K(O)*) who is and who was and who is coming and from the seven Spirits who (is *k*) before the throne of Him
5 kuma daga Yesu Almasihu, wanda ke amintaccen mashaidi, dan fari na tashi daga cikin matattu, kuma mai mulkin sarakunan duniya. Ga wanda ya ke kaunar mu ya kuma kwance mu daga daurin zunubanmu ta wurin jininsa,
and from Jesus Christ, the witness faithful, the firstborn (from *k*) the dead and the ruler of the kings of the earth. To the [One] (loving *N(k)O*) us and (having released *N(K)O*) us (from *N(k)O*) the sins of us through the blood of Him —
6 ya maishe mu masu mulki, firistoci na Allahnsa da Ubansa - daukaka da iko su tabbata gare shi har abada abadin, Amin. (aiōn g165)
and He has made us (a kingdom, *N(K)O*) (and *K*) priests to the God and Father of Him — to Him [be] the glory and the dominion to the ages of the ages, Amen. (aiōn g165)
7 Duba yana zuwa tare da gizagizai, kowane ido zai gan shi, har ma da wadanda suka soke shi. Haka kuma dukkan kabilun duniya za su yi makoki saboda da shi. I, Amin.
Behold He is coming with the clouds, and will behold Him every eye and those who Him pierced; and will wail because of Him all the tribes of the earth, Yes Amen!
8 “Nine na farko da na karshe”, in ji Ubangiji Allah, “Wanda yake shine a yanzu, shine wanda ya kasance a da, kuma shi ne mai zuwa nan gaba, Mai iko duka.”
I myself am the Alpha and the Omega (beginning and end *K*) says (the *k*) Lord (God, *NO*) who is being and who was and who is coming, the Almighty.
9 Ni, Yahaya- dan'uwan ku da wanda ke tarayya daku cikin shan wahala, da mulki da tsawon jimrewa wadanda ke cikin Yesu - ina tsibirin da ake kira Batmusa saboda maganar Allah da kuma shaida game da Yesu.
I myself John, (also *k*) brother of you and (fellow-partaker *NK(o)*) in the tribulation and (in *k*) kingdom and in endurance (in *no*) Jesus (Christ *K*) was in the island which is being called Patmos on account of the word of God and (through *k*) the testimony of Jesus (Christ. *K*)
10 Ina cikin Ruhu a ranar Ubangiji. Sai naji wata murya mai karfi a baya na kamar ta kaho.
I was in [the] Spirit on the Lord’s day and I heard behind me a voice loud like that of a trumpet
11 Ta ce, “Rubuta abinda ka gani a cikin littafi, ka kuma aika wa ikilisiyoyin nan bakwai - ga Afisus, ga Simirna, ga Birgamas, ga Tayatira, ga Sardisu, ga Filadalfiya, da kuma ga Laudikiya.”
saying (I myself *KO*) (am the Alpha and the Omega the first and the last; and *K*) What you see do write in a book and do send to the seven churches (in Asia: *K*) to Ephesus and to Smyrna and to Pergamum and to Thyatira and to Sardis and to Philadelphia and to Laodicea.
12 Na juya don in ga wanda muryarsa ke magana da ni, da na juya sai na ga fitilu bakwai akan madorin su
And (there *O*) I turned to see the voice that (was speaking *N(k)O*) with me. And having turned I saw seven lampstands golden
13 A tsakiyar fitilun akwai wani mai kama da dan mutum, yana sanye da doguwar tufa har tafin sawunsa, da damara ta zinariya kewaye a kirjinsa.
and in [the] midst of the (seven *KO*) lampstands [One] like ([the] Son *N(k)O*) of Man having clothed himself to the feet and having girded himself about at the breasts with a sash golden.
14 Kansa da gashinsa fari fat kamar auduga - kamar dusar kankara, kuma idanun sa kamar harshen wuta.
And the head of Him and the hairs [are] white (as if *N(k)O*) wool white as snow and the eyes of Him [are] like a flame of fire
15 Kafaffunsa kamar gogaggiyar tagulla, kamar tagullar da aka tace da wutar makera, muryar sa kuma kamar kugin ambaliyar ruwan teku ne.
and the feet of Him [are] like as fine bronze as in a furnace (refined *N(k)O*) and the voice of Him [is] like [the] voice of waters many
16 A hannunsa na dama yana rike da taurari bakwai, daga bakinsa kuma kakkaifan takobi mai kaifi biyu ke fitowa. Fuskarsa tana haskakawa kamar sa'adda rana ke haskakawa kwarai.
and He is holding in the right hand of Him stars seven and out of the mouth of Him a sword two-edged sharp is going forth and the face of Him [is] like the sun shining in the full strength of it.
17 Lokacin da na gan shi, na fadi kamar mataccen mutum a kafaffunsa. Ya dora hannunsa na dama a kaina ya ce, “Kada ka ji tsoro. Nine na farko da na karshe,
And when I saw Him, I fell at the feet of Him as though dead, And (He placed *N(k)O*) the right of Him (hand *K*) upon me myself saying (to me: *k*) Not do fear. I myself am the First and the Last
18 da kuma wanda ke raye. Na mutu, amma duba ina raye har abada! Kuma ina da mabudin mutuwa da na hades. (aiōn g165, Hadēs g86)
and the Living [One], and I was dead and behold living I am to the ages of the ages (Amen *K*) and I have the keys of Death and of Hades. (aiōn g165, Hadēs g86)
19 Domin haka ka rubuta abinda ka gani, abin da ke yanzu, da abin da zai faru bayan wanan.
do write (therefore *NO*) [the things] that you have seen and [the things] that are and [the things] that are about (to be *N(k)O*) after these,
20 Akan boyayyar ma'ana game da taurari bakwai da ka gani a hannun dama na, da madorin fitilu bakwai na zinariya: Taurarin nan bakwai mala'iku ne na ikilisiyoyi bakwai, kuma madorin fitilun nan bakwai ikilisiyoyi ne bakwai.
the mystery of the seven stars (which *N(k)O*) you saw on the right hand of Me and the seven lampstands golden: The seven stars [the] angels of the seven churches are and the lampstands (that *N(k)O*) (you saw *K*) seven [the] seven churches are.

< Ru’uya ta Yohanna 1 >