< Ru’uya ta Yohanna 1 >
1 Wannan shine wahayin Yesu Almasihu da Allah ya bashi ya nuna wa bayinsa abinda zai faru ba da dadewa ba. Ya bayyana wannan ta wurin aiko da mala'ikansa ga bawansa Yahaya.
The Revelation of Jesus Christ, which God gave to him, to show to his servants what must shortly come to pass; and he sent and signified it by his angel to his servant John;
2 Yahaya yayi shaida akan abinda ya gani game da maganar Allah da kuma shaidar da aka bayar game da Yesu Almasihu.
who bore witness of the word of God, and of the testimony of Jesus Christ, —of whatever he saw.
3 Mai albarka ne wanda ke karanta littafin nan da murya mai karfi, da kuma wadanda ke sauraron kalmomin wannan annabci kuma suke biyayya da abinda aka rubuta a ciki, domin kuwa lokaci ya kusato.
Blessed is he that readeth, and they that hear the words of the prophecy, and keep the things written therein; for the time is at hand.
4 Ni Yahaya, zuwa ga ikilisiyoyi bakwai na kasar Asiya: alheri zuwa gare ku da salama daga wanda ke yanzu, wanda ya kuma kasance a da, shi ne kuma mai zuwa nan gaba, kuma daga ruhohin nan bakwai da ke gaban kursiyinsa,
John to the seven churches which are in Asia: Grace be to you, and peace, from him who is, and who was, and who is to come; and from the seven spirits which are before his throne;
5 kuma daga Yesu Almasihu, wanda ke amintaccen mashaidi, dan fari na tashi daga cikin matattu, kuma mai mulkin sarakunan duniya. Ga wanda ya ke kaunar mu ya kuma kwance mu daga daurin zunubanmu ta wurin jininsa,
and from Jesus Christ, the faithful witness, the first-born of the dead, and the ruler of the kings of the earth. To him that loveth us, and washed us from our sins in his own blood,
6 ya maishe mu masu mulki, firistoci na Allahnsa da Ubansa - daukaka da iko su tabbata gare shi har abada abadin, Amin. (aiōn )
and made us a kingdom, priests to God his Father, to him be the glory and the dominion for ever. Amen. (aiōn )
7 Duba yana zuwa tare da gizagizai, kowane ido zai gan shi, har ma da wadanda suka soke shi. Haka kuma dukkan kabilun duniya za su yi makoki saboda da shi. I, Amin.
Behold, he cometh with the clouds, and every eye shall see him, and they who pierced him; and all the tribes of the earth shall wail because of him. Even so, Amen.
8 “Nine na farko da na karshe”, in ji Ubangiji Allah, “Wanda yake shine a yanzu, shine wanda ya kasance a da, kuma shi ne mai zuwa nan gaba, Mai iko duka.”
I am the Alpha and the Omega, saith the Lord God, he who is, and who was, and who is to come, the Almighty.
9 Ni, Yahaya- dan'uwan ku da wanda ke tarayya daku cikin shan wahala, da mulki da tsawon jimrewa wadanda ke cikin Yesu - ina tsibirin da ake kira Batmusa saboda maganar Allah da kuma shaida game da Yesu.
I John, your brother, and companion in the affliction and kingdom and endurance in Jesus, was in the isle that is called Patmos, on account of the word of God, and the testimony of Jesus.
10 Ina cikin Ruhu a ranar Ubangiji. Sai naji wata murya mai karfi a baya na kamar ta kaho.
I was in the Spirit on the Lord's day; and I heard behind me a loud voice, as of a trumpet,
11 Ta ce, “Rubuta abinda ka gani a cikin littafi, ka kuma aika wa ikilisiyoyin nan bakwai - ga Afisus, ga Simirna, ga Birgamas, ga Tayatira, ga Sardisu, ga Filadalfiya, da kuma ga Laudikiya.”
saying: What thou seest, write in a book, and send it to the seven churches; to Ephesus, and to Smyrna, and to Pergamus, and to Thyatira, and to Sardes, and to Philadelphia, and to Laodicea.
12 Na juya don in ga wanda muryarsa ke magana da ni, da na juya sai na ga fitilu bakwai akan madorin su
And I turned to see the voice that was speaking with me; and having turned, I saw seven golden candlesticks,
13 A tsakiyar fitilun akwai wani mai kama da dan mutum, yana sanye da doguwar tufa har tafin sawunsa, da damara ta zinariya kewaye a kirjinsa.
and in the midst of the candlesticks one like to a son of man, clothed with a garment reaching down to the feet, and girded at the breasts with a golden girdle.
14 Kansa da gashinsa fari fat kamar auduga - kamar dusar kankara, kuma idanun sa kamar harshen wuta.
His head and his hairs were white as white wool, as snow; and his eyes were as a flame of fire;
15 Kafaffunsa kamar gogaggiyar tagulla, kamar tagullar da aka tace da wutar makera, muryar sa kuma kamar kugin ambaliyar ruwan teku ne.
and his feet were like fine brass, as if burning in a furnace; and his voice was as the sound of many waters.
16 A hannunsa na dama yana rike da taurari bakwai, daga bakinsa kuma kakkaifan takobi mai kaifi biyu ke fitowa. Fuskarsa tana haskakawa kamar sa'adda rana ke haskakawa kwarai.
And he had in his right hand seven stars; and out of his mouth went a sharp two-edged sword; and his countenance was as the sun shineth in his strength.
17 Lokacin da na gan shi, na fadi kamar mataccen mutum a kafaffunsa. Ya dora hannunsa na dama a kaina ya ce, “Kada ka ji tsoro. Nine na farko da na karshe,
And when I saw him, I fell at his feet as dead; and he laid his right hand on me, saying, Fear not; I am the first and the last,
18 da kuma wanda ke raye. Na mutu, amma duba ina raye har abada! Kuma ina da mabudin mutuwa da na hades. (aiōn , Hadēs )
and he that liveth; and I was dead, and behold, I am alive for evermore; and I have the keys of death and the underworld. (aiōn , Hadēs )
19 Domin haka ka rubuta abinda ka gani, abin da ke yanzu, da abin da zai faru bayan wanan.
Write therefore the things which thou sawest, and the things which are, and the things which shall be after these;
20 Akan boyayyar ma'ana game da taurari bakwai da ka gani a hannun dama na, da madorin fitilu bakwai na zinariya: Taurarin nan bakwai mala'iku ne na ikilisiyoyi bakwai, kuma madorin fitilun nan bakwai ikilisiyoyi ne bakwai.
the mystery of the seven stars which thou sawest in my right hand, and the seven golden candlesticks. The seven stars are the angels of the seven churches; and the seven candlesticks are the seven churches.