< Ru’uya ta Yohanna 1 >

1 Wannan shine wahayin Yesu Almasihu da Allah ya bashi ya nuna wa bayinsa abinda zai faru ba da dadewa ba. Ya bayyana wannan ta wurin aiko da mala'ikansa ga bawansa Yahaya.
A revelation of Jesus Christ that God gave to Him to show to His servants what things must quickly come to pass; and He signified [it], having sent through His messenger to His servant John,
2 Yahaya yayi shaida akan abinda ya gani game da maganar Allah da kuma shaidar da aka bayar game da Yesu Almasihu.
who testified [to] the word of God, and the testimony of Jesus Christ, as many things as he also saw.
3 Mai albarka ne wanda ke karanta littafin nan da murya mai karfi, da kuma wadanda ke sauraron kalmomin wannan annabci kuma suke biyayya da abinda aka rubuta a ciki, domin kuwa lokaci ya kusato.
Blessed is he who is reading, and those hearing the words of the prophecy, and keeping the things written in it, for the time is near!
4 Ni Yahaya, zuwa ga ikilisiyoyi bakwai na kasar Asiya: alheri zuwa gare ku da salama daga wanda ke yanzu, wanda ya kuma kasance a da, shi ne kuma mai zuwa nan gaba, kuma daga ruhohin nan bakwai da ke gaban kursiyinsa,
John, to the seven assemblies that [are] in Asia: Grace to you, and peace, from Him who is, and who was, and who is coming, and from the Seven Spirits that are before His throne,
5 kuma daga Yesu Almasihu, wanda ke amintaccen mashaidi, dan fari na tashi daga cikin matattu, kuma mai mulkin sarakunan duniya. Ga wanda ya ke kaunar mu ya kuma kwance mu daga daurin zunubanmu ta wurin jininsa,
and from Jesus Christ, the faithful witness, the firstborn out of the dead, and the ruler of the kings of the earth; to Him loving us and having released us from our sins in His blood,
6 ya maishe mu masu mulki, firistoci na Allahnsa da Ubansa - daukaka da iko su tabbata gare shi har abada abadin, Amin. (aiōn g165)
[He] has also made us kings and priests to His God and Father, to Him—the glory and the power through the ages of the ages! Amen. (aiōn g165)
7 Duba yana zuwa tare da gizagizai, kowane ido zai gan shi, har ma da wadanda suka soke shi. Haka kuma dukkan kabilun duniya za su yi makoki saboda da shi. I, Amin.
Behold, He comes with the clouds, and every eye will see Him, even those who pierced Him, and all the tribes of the land will wail because of Him. Yes! Amen!
8 “Nine na farko da na karshe”, in ji Ubangiji Allah, “Wanda yake shine a yanzu, shine wanda ya kasance a da, kuma shi ne mai zuwa nan gaba, Mai iko duka.”
“I am the Alpha and the Omega, beginning and end, says the LORD, who is, and who was, and who is coming—the Almighty.”
9 Ni, Yahaya- dan'uwan ku da wanda ke tarayya daku cikin shan wahala, da mulki da tsawon jimrewa wadanda ke cikin Yesu - ina tsibirin da ake kira Batmusa saboda maganar Allah da kuma shaida game da Yesu.
I, John, who [am] also your brother, and fellow-partner in the tribulation, and in the kingdom and endurance of Jesus Christ, was in the island that is called Patmos, because of the word of God, and because of the testimony of Jesus Christ;
10 Ina cikin Ruhu a ranar Ubangiji. Sai naji wata murya mai karfi a baya na kamar ta kaho.
I was in the Spirit on the LORD’s Day, and I heard a great voice behind me, as of a trumpet, saying,
11 Ta ce, “Rubuta abinda ka gani a cikin littafi, ka kuma aika wa ikilisiyoyin nan bakwai - ga Afisus, ga Simirna, ga Birgamas, ga Tayatira, ga Sardisu, ga Filadalfiya, da kuma ga Laudikiya.”
“I am the Alpha and the Omega, the First and the Last,” and, “Write what you see in a scroll, and send [it] to the seven assemblies that [are] in Asia: to Ephesus, and to Smyrna, and to Pergamos, and to Thyatira, and to Sardis, and to Philadelphia, and to Laodicea.”
12 Na juya don in ga wanda muryarsa ke magana da ni, da na juya sai na ga fitilu bakwai akan madorin su
And I turned to see the voice that spoke with me, and having turned, I saw seven golden lampstands,
13 A tsakiyar fitilun akwai wani mai kama da dan mutum, yana sanye da doguwar tufa har tafin sawunsa, da damara ta zinariya kewaye a kirjinsa.
and in the midst of the seven lampstands, [One] like a Son of Man, clothed to the foot, and having been girded around at the breasts with a golden girdle,
14 Kansa da gashinsa fari fat kamar auduga - kamar dusar kankara, kuma idanun sa kamar harshen wuta.
and His head and hairs [were] white, as if white wool—as snow, and His eyes as a flame of fire;
15 Kafaffunsa kamar gogaggiyar tagulla, kamar tagullar da aka tace da wutar makera, muryar sa kuma kamar kugin ambaliyar ruwan teku ne.
and His feet like to frankincense-colored brass, as having been fired in a furnace, and His voice as a sound of many waters;
16 A hannunsa na dama yana rike da taurari bakwai, daga bakinsa kuma kakkaifan takobi mai kaifi biyu ke fitowa. Fuskarsa tana haskakawa kamar sa'adda rana ke haskakawa kwarai.
and having seven stars in His right hand, and out of His mouth a sharp two-edged sword is proceeding, and His countenance—as the sun shining in its might.
17 Lokacin da na gan shi, na fadi kamar mataccen mutum a kafaffunsa. Ya dora hannunsa na dama a kaina ya ce, “Kada ka ji tsoro. Nine na farko da na karshe,
And when I saw Him, I fell at His feet as dead, and He placed His right hand on me, saying to me, “Do not be afraid; I am the First and the Last,
18 da kuma wanda ke raye. Na mutu, amma duba ina raye har abada! Kuma ina da mabudin mutuwa da na hades. (aiōn g165, Hadēs g86)
and He who is living, and I became dead, and behold, I am living through the ages of the ages. Amen! And I have the keys of Hades and of death. (aiōn g165, Hadēs g86)
19 Domin haka ka rubuta abinda ka gani, abin da ke yanzu, da abin da zai faru bayan wanan.
Write the things that you have seen, and the things that are, and the things that are about to come after these things;
20 Akan boyayyar ma'ana game da taurari bakwai da ka gani a hannun dama na, da madorin fitilu bakwai na zinariya: Taurarin nan bakwai mala'iku ne na ikilisiyoyi bakwai, kuma madorin fitilun nan bakwai ikilisiyoyi ne bakwai.
the secret of the seven stars that you have seen on My right hand, and the seven golden lampstands: the seven stars are messengers of the seven assemblies, and the seven lampstands that you have seen are seven assemblies.”

< Ru’uya ta Yohanna 1 >