< Ru’uya ta Yohanna 1 >

1 Wannan shine wahayin Yesu Almasihu da Allah ya bashi ya nuna wa bayinsa abinda zai faru ba da dadewa ba. Ya bayyana wannan ta wurin aiko da mala'ikansa ga bawansa Yahaya.
Jesu Kristi Aabenbaring, som Gud gav ham for at vise sine Tjenere, li vad der skal ske snart, og han sendte Bud ved sin Engel og fremstillede det i Billeder for sin Tjener Johannes,
2 Yahaya yayi shaida akan abinda ya gani game da maganar Allah da kuma shaidar da aka bayar game da Yesu Almasihu.
som har vidnet om Guds Ord og Jesu Kristi Vidnesbyrd: Alt, hvad han har set.
3 Mai albarka ne wanda ke karanta littafin nan da murya mai karfi, da kuma wadanda ke sauraron kalmomin wannan annabci kuma suke biyayya da abinda aka rubuta a ciki, domin kuwa lokaci ya kusato.
Salig er den, som oplæser, og de, som høre Profetiens Ord og bevare det, som er skrevet i den; thi Tiden er nær.
4 Ni Yahaya, zuwa ga ikilisiyoyi bakwai na kasar Asiya: alheri zuwa gare ku da salama daga wanda ke yanzu, wanda ya kuma kasance a da, shi ne kuma mai zuwa nan gaba, kuma daga ruhohin nan bakwai da ke gaban kursiyinsa,
Johannes til de syv Menigheder i Asien: Naade være med eder og Fred fra ham, som er, og som var, og som kommer, og fra de syv Aander, som ere foran hans Trone,
5 kuma daga Yesu Almasihu, wanda ke amintaccen mashaidi, dan fari na tashi daga cikin matattu, kuma mai mulkin sarakunan duniya. Ga wanda ya ke kaunar mu ya kuma kwance mu daga daurin zunubanmu ta wurin jininsa,
og fra Jesus Kristus, det troværdige Vidne, den førstefødte af de døde og Jordens Kongers Fyrste. Ham, som elsker os og har udløst os af vore Synder med sit Blod
6 ya maishe mu masu mulki, firistoci na Allahnsa da Ubansa - daukaka da iko su tabbata gare shi har abada abadin, Amin. (aiōn g165)
og har gjort os til et Kongerige, til Præster for sin Gud og Fader: Ham være Æren og Magten i Evighedernes Evigheder! Amen. (aiōn g165)
7 Duba yana zuwa tare da gizagizai, kowane ido zai gan shi, har ma da wadanda suka soke shi. Haka kuma dukkan kabilun duniya za su yi makoki saboda da shi. I, Amin.
Se, han kommer med Skyerne, og hvert Øje skal se ham, ogsaa de, som have gennemstunget ham, og alle Jordens Stammer skulle jamre ved hans Komme. Ja, Amen!
8 “Nine na farko da na karshe”, in ji Ubangiji Allah, “Wanda yake shine a yanzu, shine wanda ya kasance a da, kuma shi ne mai zuwa nan gaba, Mai iko duka.”
Jeg er Alfa og Omega, siger Gud Herren, han, som er, og som var, og som kommer, den Almægtige.
9 Ni, Yahaya- dan'uwan ku da wanda ke tarayya daku cikin shan wahala, da mulki da tsawon jimrewa wadanda ke cikin Yesu - ina tsibirin da ake kira Batmusa saboda maganar Allah da kuma shaida game da Yesu.
Jeg Johannes, eders Broder og meddelagtig i Trængselen og Riget og Udholdenheden i Jesus, var paa den Ø, som kaldes Patmos, for Guds Ords og for Jesu Vidnesbyrds Skyld.
10 Ina cikin Ruhu a ranar Ubangiji. Sai naji wata murya mai karfi a baya na kamar ta kaho.
Jeg henryktes i Aanden paa Herrens Dag, og jeg hørte bag mig en høj Røst som af en Basun, der sagde:
11 Ta ce, “Rubuta abinda ka gani a cikin littafi, ka kuma aika wa ikilisiyoyin nan bakwai - ga Afisus, ga Simirna, ga Birgamas, ga Tayatira, ga Sardisu, ga Filadalfiya, da kuma ga Laudikiya.”
Hvad du ser, skriv det i en Bog, og send det til de syv Menigheder, til Efesus og til Smyrna og til Pergamus og til Thyatira og til Sardes og til Filadelfia og til Laodikea.
12 Na juya don in ga wanda muryarsa ke magana da ni, da na juya sai na ga fitilu bakwai akan madorin su
Og jeg vendte mig for at se Røsten, som talte med mig; og da jeg vendte mig, saa jeg syv Guldlysestager
13 A tsakiyar fitilun akwai wani mai kama da dan mutum, yana sanye da doguwar tufa har tafin sawunsa, da damara ta zinariya kewaye a kirjinsa.
og midt imellem de syv Lysestager en, lig en Menneskesøn, iført en fodsid Kjortel og omgjordet om Brystet med et Guldbælte.
14 Kansa da gashinsa fari fat kamar auduga - kamar dusar kankara, kuma idanun sa kamar harshen wuta.
Men hans Hoved og Haar var hvidt som hvid Uld, som Sne; og hans Øjne som Ildslue;
15 Kafaffunsa kamar gogaggiyar tagulla, kamar tagullar da aka tace da wutar makera, muryar sa kuma kamar kugin ambaliyar ruwan teku ne.
og hans Fødder lignede skinnende Malm, naar det gløder i Ovnen; og hans Røst var som mange Vandes Lyd;
16 A hannunsa na dama yana rike da taurari bakwai, daga bakinsa kuma kakkaifan takobi mai kaifi biyu ke fitowa. Fuskarsa tana haskakawa kamar sa'adda rana ke haskakawa kwarai.
og i sin højre Haand havde han syv Stjerner; og af hans Mund udgik der et tveægget, skarpt Sværd, og hans Udseende var som Solen, naar den skinner i sin Kraft.
17 Lokacin da na gan shi, na fadi kamar mataccen mutum a kafaffunsa. Ya dora hannunsa na dama a kaina ya ce, “Kada ka ji tsoro. Nine na farko da na karshe,
Og da jeg saa ham, faldt jeg ned for hans Fødder som død; og han lagde sin højre Haand paa mig og sagde:
18 da kuma wanda ke raye. Na mutu, amma duba ina raye har abada! Kuma ina da mabudin mutuwa da na hades. (aiōn g165, Hadēs g86)
Frygt ikke! Jeg er den første og den sidste og den levende; og jeg var død, og se, jeg er levende i Evighedernes Evigheder, og jeg har Dødens og Dødsrigets Nøgler. (aiōn g165, Hadēs g86)
19 Domin haka ka rubuta abinda ka gani, abin da ke yanzu, da abin da zai faru bayan wanan.
Skriv derfor, hvad du saa, baade det, som er, og det, som skal ske herefter.
20 Akan boyayyar ma'ana game da taurari bakwai da ka gani a hannun dama na, da madorin fitilu bakwai na zinariya: Taurarin nan bakwai mala'iku ne na ikilisiyoyi bakwai, kuma madorin fitilun nan bakwai ikilisiyoyi ne bakwai.
Dette er de syv Stjerners Hemmelighed, hvilke du har set i min højre Haand, og de syv Guldlysestager: De syv Stjerner ere de syv Menigheders Engle, og de syv Lysestager ere syv Menigheder.

< Ru’uya ta Yohanna 1 >