< Ru’uya ta Yohanna 6 >
1 Na duba lokacin da Dan Ragon ya bude daya daga cikin hatiman bakwai, sai na ji daya daga cikin rayayyun halittattun hudu ya fada da murya kamar tsawa, ''Zo!”
I saw that [Jesus, the one who is like a] lamb, opened the first of the seven seals [of the scroll]. Then I heard one of the four living [creatures] say in a voice [as loud] as [SIM] thunder, “Come!”
2 Sai Na duba sai ga wani farin doki, mahayinsa na rike da baka, kuma an bashi rawani. Ya fito a matsayin mai nasara domin ya yi nasara.
Then I saw a white horse [come out]. The one who sat on it had a bow [and arrows]. [God] gave him a crown [to show that he was the king]. Then the one who conquers [people] went out to continue to conquer [people].
3 Sa'anda Dan Ragon ya bude hatimi na biyu, sai na ji rayayyen halitta na biyu ya ce, ''Zo!''
When the [one who was like a] lamb opened the second seal, I heard the second living [creature] say, “Come!”
4 Sai wani doki ya fito waje - jawur. Ga mahayin aka bashi dama ya dauke salama daga duniya, domin mutanen ta su karkashe juna. Wannan mahayin an bashi babbar takobi.
Then a red horse came out. The one sitting on it was allowed {[God] allowed the one sitting on it} to cause [people] to no longer [live] peacefully, but instead to be killing each other. [For this purpose] he was given {[God’s agent] gave to him} a large sword.
5 Sa'anda Dan Ragon ya bude hatimi na uku, sai na ji rayayyen halita na uku ya ce, ''Zo!'' Na ga bakin doki, mai hawanta na rike da ma'auni a cikin hannunsa.
When [the one who is like a] lamb opened the third seal, I heard the third living [creature] say, “Come!” This time, I saw a black horse [come out]. The one who sat on it had a pair of scales in his hand.
6 Sai na ji kamar wata murya daga cikin rayayyun halittattun nan hudu ta ce, “Mudun alkama guda a kan albashin yini, kuma mudun sha'ir uku. Amma kar ka bata mai da kuma ruwan inabi.”
I heard a voice [that sounded] like [it was coming from] among the four living [creatures]. It was saying ([to the horseman/to the man who was sitting on the black horse]), “A quart of wheat [will cost so much that] a man must work a whole day to earn enough money to buy it, and three quarts of barley will sell for the same price. But do not cut off [the supply of] olive oil or the wine [MTY]!”
7 Da Dan Ragon ya bude hatimi na hudu, na ji muryar rayayyen halitta na hudu ya ce, ''Zo!''
When the [one who is like a] lamb opened the fourth seal, I heard the fourth living [creature] say, “Come!”
8 Sai na ga wani doki ruwan toka. Mai hawansa an bashi suna mutuwa, hades kuma tana biye da shi. An basu iko bisa kashi hudu na duniya su kashe da takobi, yunwa, cututtuka, da kuma namomin jeji na duniya. (Hadēs )
This time I saw a pale horse [come out]. The one who sat on it is named ‘[The one who causes] death [PRS]’, and [the one that is named ‘The place where dead people go’] accompanied him. [God] gave them authority over one quarter of the people on earth to incite them to kill each other with weapons [SYN], and also authority to kill them (by [causing them to] starve, by [their causing them to become] sick from epidemics, and by [their causing them to be attacked by] wild animals. (Hadēs )
9 Da Dan Ragon ya bude hatimi na biyar, a karkashin bagadi sai na ga rayukan wadanda aka kashe saboda maganar Allah, da kuma shaidar da suka rike.
When the [one who is like a] lamb opened the fifth seal, I saw under (OR, at the base of) the altar [in heaven] the souls of [God’s servants] who had been killed {whom [people had] killed} because of [their believing] God’s message, and because they told others [the message about Jesus].
10 Suka yi kuka da babban murya, ''Sai yaushe ya mai iko duka, Mai Tsarki da gaskiya, zaka shari'anta mazaunan duniya, ka kuma dauki fansar jininmu?
They spoke loudly [to God] saying, “Sovereign/Almighty Lord, you are holy and faithful. How long [will it be] before you judge [and punish] the people on earth who murdered [us(exc)]?”
11 Sai kowanne dayan su aka bashi farar tufa aka kuma fada masu su kara jira na lokaci kadan har sai adadin abokan bautar su da kuma 'yan'uwansu maza da mata wadanda aka kashe ya cika, kamar yadda aka kashe su.
[God] gave to each of them a long white robe, and [he] told them to rest a little longer until [people] killed all the believers who served [the Lord] with them. They were believers whom [God wanted to die in just the same way] that these others had been killed.
12 Da Dan Ragon ya bude hatimi na shidan, ina kallo sai ga babbar girgizar kasa. Rana ta zama baki kirin kamar bakar tufa, wata kuma ya zama kamar jini.
I saw that when [the one who is like a] lamb opened the sixth seal, the earth shook violently. The sun became as black as cloth made (of [black] wool/of pitch). The whole moon became [red] [SIM] like blood.
13 Taurarin sama suka fado kasa, kamar yadda itacen baure ke karkade 'ya'yansa da basu nuna ba, yayin da babbar iska ta kada.
The stars fell to the earth [in great numbers], just [SIM] like immature figs fall when a fig tree is shaken by a strong wind {when a strong wind shakes a fig tree}.
14 Sama kuma ta bace kamar takardar da aka nannade. Kowanne dutse da tsibiri aka kau da shi daga wurinsa.
The sky split open and [rolled up on either side] just [SIM] like an [old] scroll rolls up [when it is split in two]. Every mountain and island moved out of its place.
15 Sai sarakan duniya da muhimman mutane da sarakunan yaki, attajirai, da masu iko, tare da kowanne mutum, bawa da 'yantacce suka boye cikin duwatsu da tsaunuka.
[As a result, all the rebellious people] of the earth, [including] kings, high-ranking people, generals, the rich people, the powerful people, along with everyone [else], both slave and free, hid themselves in caves and between the mountain rocks.
16 Suka ce wa tsaunuka da duwatsu, “Ku fado bisan mu! Ku boye mu daga fuskar wanda yake zaune bisa kursiyin da kuma fushin Dan Ragon.
They shouted to the mountains and to the rocks, “Fall on us [(exc)] and hide us [(exc)] in order that the one who sits upon the throne will not be able to see us [(exc)] [MTY], and [in order that] the [one who is like a] lamb will not be able to punish [MTY] us [(exc)].
17 Domin babban ranar fushin sa ta zo. Wa zai iya tsayawa?''
This is the terrible day on which they will punish [MTY] us [(exc)], and [when that happens], no one will be able to survive! [RHQ]”